Advertisement
_
*INA MASU NEMAN MAGANIN INFECTION SADIDAN? MAGANIN NI’IMAH, MAGANIN GYARAN HIPS AND BOOBS? MAGANIN BASIR….NA HAUSA BANA BATURE ME KWANTAR DA CIWO BA? TO KU MARMATSO KUSA, DOMIN YAU MUNA TAFE DA ALBISHIR WANDA ZAI FADADA MURMISHIN FUSKOKIN KU.. YA KUMA KAWATA ZUKATAN KU. MUN GWADA MUN GANI, MAGUNGUNANTA SUNADA KYAU KUMA SUNA DA AIKI.. BABU SIDE EFFECT, ANYI SU NE DAGA TSAFTATTUN KAYAN ITATUWA, DA SIRRIN CHADIAN HERBALS.. KARNA CIKAKU DA SURUTU;_
_*AISHA S BAYERO TRADITIONAL MEDICINE AND HERBAL RESEARCH CENTER…_*
_KUNJI SUNAN KO? CENTER CE TA MAGUNGUNAN GARGAJIA, WANDA DUK WANI DAMUWA DAKE DAMUNKA IDAN HAR KAZO WAJEN S BAYERO TA KARE DA YARDAR ALLAH.._
_KADAN DAGA MAGUNGUNANTA SUN KUNSHI:_
_MAGANIN SANYI _
Advertisements
_MAGANIN NIIMA SET_
_MAGANIN NANKARWA _
_MAGANIN KIBA BABBA DA _KARAMI _
_MAGANIN HIPS _
_MAGANIN GYARAN NONO _
_MAGANIN RAGE KIBA _
_MAGANIN SAKA FEELING _
_MAGANIN CIDA KWAI _
_ZUMA YAR ASALI_
_MAGANIN BASIR KOWANNE IRI _
_HODAR NI’IMA _
_MAGANIN MALLAKA _
Advertisements
_GUMBAR NONON RAK’UMI _
_GUMBAR MADARA _
_TURAREN FARIN JINI _
_KAZA MARA KWAI _
_TURAREN MALLAKA 3 STEP _
_HAD’IN MATAR MINISTER 1_
_KAZA ME KWAI_
_STEP 2:_
_TURAREN MALLAKA ME KWALBA _
_ME KUNAMA DAN MATSI _
_TURAREN GOSHI _
_TURAREN QIRJI _
_TAUWADAR MATA _
_MEMORY _
_KAHON MALLAKA_
_YAJIN MAZA_
_TEA DIN MAZA _
_DAMBUN MATSI_
_MAN AYU_
_MAN DAMO PURE _
_KWALLIN IDONKA IDONA _
_GARIN SHA DAKA ME KYAU _
_KUBEWAR MATA_
_DUKA WADANNAN INGATTUN MAGUNGUNA NA GARGAJIYA HAJ AISHA NA DASU GANGARIYA.. HERBAL MAGUNGUNA NE MASU KYAU DA INGANCI.. TAFIYAYYU NA KASAR CHAD. CHADIAN HERBAL MEDICINE AND RESEARCH CENTER.. KYAU, INGANCI.. RAHUSA… SAI MAGUNGUNAN *AISHA S BAYERO TRADITIONAL MED AND HERBAL RESEARCH CENTER…._
_NUMBER WAYAR WHATSAPP: 08121491609 KO KIRA TA NUMBER 08145873617._
_ADIRESHI: KUNTAU KARSHEN KWALTA KAN A KARASA YAN TIFA, DAIDAI GADON KAYA CEMENT.._
*13*
*wattpad:missxoxo00*
*IG Business: yerwaincense_and_more*
*KHADIJAA*
Ina kammala shiryawa nasa kayan bacci wasu riga da wando, kiran waya ne ya sani dakatawa do nike wajan daure gashin kai na. Naje nai picking baki na dauke da sallama, muryarshi ta daki cikin kunne na inda yake cewa.
“Idan da hali kuma zaki samu dama, ina son ganinki yanzu.”
Kamar bazan amsa ba, Sai kuma naga rashin dacewar hakan, cikin dakile murya nace.
“Toh ina zuwa.”
Ina jin sanda ya furta ‘okay’ a hankali sannan kuma katse ni kuma na bi wayar da kallo ina tabe baki. Wardrobe na nufa ina tunanin saka kaya, Sai kuma na kalli jikina naga babu inda za’a iya gani, na janyo dogon hijab har kasa nasa tare da bin ko’ina da turaruka masu dadin kamshi.
Babu abin da na dauka dan ko magungunin su duk sun kare, na kuma sanar da Gwaggo ta fada, tace malam zai kawo wasu idan ya gama hadawa. Ta baya nabi ko ina haske tamkar ba dare ba, na karasa ciki kai na a kasa kamar wata marar gaskiya. Tamkar a tare muka zo da Shaheedah, dan ko sallama ban gama furtawa ba naji shigowarta cikin isa da takama, na kai duba na wajan da Salman yake a zaune shima yana kallon mu, duk a zato na yana sane ya kiramu mu duka.
Sanye yake cikin wasu fitinannun kayan bacci masu mugun santsi milk color, ba karamin kyau suka yi mai ba abin ka da farar fata wacce ta hadu da jin dadi. Zaune yake akan sofa ya dora kafa daya kan daya yana girgizawa, hannunsa dauke da glass cup mai dauke da fura da nono da yaji ayaba da kwakwa yana sha. Daga ni har Shaheedah tsayawa mukai muna kallonsa dan kamar be san da tsayuwar mu ba a gurin, ina ta tunanin abin yi kawai naga ta nufe shi tare da hayewa kan cinyarsa tana lankwasa kai.
“Honey ban gane wannan lamarin ba, yaushe rabon da na kasance tare da kai, kullum kuna tare da waccen yarinyar mai kashin tsiya. Na gaji to gaskiya dan haka yau sai dai ta hakura da duk wata jarabarta dan ba zata samu ba.”
Shi kanshi Salman dagowa yai yana kallona, Shi kansa yaji abin da be taba kawowa ba. Ni kuma na sakar masa wani shu’umin kallo da ya sanya shi hadiye furar da ya kurba cikin bakin sa. Na karasa wajan center table tare da cire hijabi na ina faman jujjuya kugu na. Ban yi gigin zuwa gurin su ba tunda ta rigani hayewa kan cinyar da nake samu na zaune dan kawai na guma mata.
Ina tsaye kam sai faman gyara gashin kai na nake yi, ina kuma karya wuya cikin salon shagwaba nace.
“Whole world kasan yadda naji dadi dazu da ka matsa min mara ta? Ina komawa part dina period din yazo cikin sauki. But naji yanzu ma tana dan tsira min, shine nazo ka kuma yi min irin yadda kai min please.”
“Ba Zai yi ba din, ko baki ji ba? Na ce ba zai yi ba ko kin dauka bawanki ne Shi. Kuma yanzu ba ke kike da Shi ba, ni ce nan, kwana biyu ina sane da yadda kike yi masa zarya ko kin dauka Shi irin jarababnun mazan nan ne?”
“Dan Allah Yaya ki yi hakuri ya dan matsa min, ai ba wani abin zamu yi ba tunda dazu mun hadu, mun dade kuma tare. Ki barshi a matsayinsa na miji na ya yi min ba sai naje asibiti wani ya yi min ba.”
Nai maganar cike da nuna mata Cewa a kage nake, na kuma tabbatar mata da cewa mun yi wani abu da Salman din Wanda take ta kurin yau da ita Za a yi. Tartsatsatsatsasss muka ji jikin kunnuwan mu, da sauri nai tsalle biyu na rungume bayan Salman din ina kudindine fuska, Jiki na kuma yana bari alamar ina cikin tsoro, Sai faman wayyo Allah nake kai kace wani abu ya biyo ni tsabar iya acting. Shaheedah kuwa baki ta saki tana kallon yadda na cukwikuiye Salman kamar bana san ya gudu ya bar ni.
“Ke! Menene haka kamar wata yar karamar yarinya? Baki ga glass cup din hannunsa ne ya fadi ya fashe ba zaki mana Wannan dramar. Ke ko dai kin tab’a d’ana wasan hausa ne, dan naga kin iya acting din sosai?”
Nai kamar zan yi kuka ina cewa,
“Yaya ni banga lokacin da cup din ya fadi ba, kawai kara naji na dauka ma bomb ne. Kuma ni fa ko hausa drama bana kallo bare nasan me suke koyarwa.”
Shaheedah taja tsaki tare da kallon Salman tana shafar habar sa mai dauke da kwantaccen gashi, nima kuma naki sakin shi sai dad’a ma kwanciya da nai a bayan nasa ina faman sauke numfashi. Ta kuma jan tsaki, abin da yake batawa Salman rai kenan wato mutum ya yi ta tsaki a gabansa, ko ba dashi kake ba baya so sam.
“Yaya Shaheedah dan Allah ki bamu koda one minute ne ya gama yi min please.”
Shi kanshi Salman yana mamakin ganin yadda Shaheedah tak’i daga masa cinya tunda ba saba yin haka tai ba, ya gane cewa ta yi haka ne tunda Dije ma yi take a gabanta, sai dai sam ba ta burgeshi ba tunda abin na ta kwaikwayo ne.
“Idan zaki zo ki wuce kizo ga hanya nan, idan har sai ya danna miki zaki ji sauki toh wallahi sai dai marar taki ta zazzago makira kawai.”
Na zare hannuwa da jikina daga na Salman na mike tsaya cikin nuna bacin rai a fuskata, zuciya ta kuwa shar dan nasan yanzu ma na guma mata bacin rai a zuciyar ta. Nazo zan wuce shi yasa tattausan hannunsa ya riko ni, muka had’a ido dashi, sai ya lashi saman lips din shi tare da furta.
“Why…?!”
Duk da ban gane dalilin ce min haka ba, sai nai amfani da wannan damar wajan sunkuyar da kai na ce.
“Ka barshi kawai na hakura tunda ba ta yarda ba, ni bana son rigima kuma itace babba.”
Ji nai ya sakar min hannun haushi ya kamani duk a zato na zai ki saki na ko kuma ma ya janyo ni jikinsa dan mu kunsawa Shaheedah bacin rai. da sauri na dauki hijab dina na saka, ko ta kansu ban kuma bi ba haka na fice ina kunku ni. wallahi duk da bana jin ina son Salman, amman tabbas naji na tsani Shaheedah, haushin ta nake ji fiye da tunanin mai hasashe. Ina shiga daki nayi cilli da hijabin tare da fadawa kan gado, tunanin Mas’oud yana son fado min nai saurin mikewa zaune dan bana son akwai auran wani a kai na kuma a ce ina tunanin wani daban.
A can wajan su kuwa, Dije fitowa Shaheedah ta fara kissing din shi tana kokarin cire masa riga, Salman yai saurin rikewa tare da daga ta daga cinyarsa ya mike tsaya. kallan ta ya yi cikin dafe kai yana rintsa ido shi a dole ga wanda kanshi ya fara ciwo. Ya riko hannunta suka nufi kan gado yana ta dafe goshi yace.
“Kai na ke ciwo, ga sanyi ina ji lullube ni please.”
Shaheedah ta saki baki da hanci tana kallon sa, ganin yadda yake rawar jiki ne yasa itama ta hakura ta rufa masa tattausan bargo tana mai hadiye maitarta a fili. Gashi maganin da ta sha so ake suyi mu’amula a daren, kuma ta kasa samu tunda gashi kwance yana rawar sanyi. Da kyar ta iya fitowa daga dakin ta koma sashen ta tana jan tsaki. Salman kuwa tana fita ya yaye bargon tare da bin kofar da kallo, sam ba wani ciwon kai da yake ji, kawai tunda ya ga wata yar k’aramar laya a wuyanta, ta sanya zaran sarka a jiki ta yadda idan ba kula kayi sosai ba bai zama lallai ka gane cewa laya bace.
Shi kuma tun da ya gani yaji sam hankalinsa be kwanta da sarkar ba, hakan yasan ya shi yin pretending na ciwon kai da jin alamar zazzabi. can kuma salon khadija ya fado masa, wato yarinyar ta san ta kan makirci, idan ban da haka me yasa idan su biyu ne bata tab’a ko rike masa hannu idan ba da dalili ba. Amman a gaban Shaheedah sai tai ta nuna ai har sun riga sun zama abu daya? yana son sanin me yasa take masa wannan salon, yau tsabar kwarewa ma cewa tai ya matsa mata mara bayan beji ba kuma be gani ba.
Tunani ya fara tabbas akwai wani abu da khadija ba ta son Shaheedah ta sani game da rayuwar su. kamar yadda yanzu ya fara tunanin akwai babbar matsala tattare da wadanda suke zagaye dashi. Lallai ya zame masa tilas akan ya kara wani salon kusanci tsakanin shi da khadija, yana ji a jikinsa cewar ba zata cuce shi ba duk da cewar yasan ba son shi a ranta, amman yasan ba tasan komai ba a cikin makircin sarautar Bassannabas bare tace zata yi masa. Dole ya kusantota gurin shi tun kafin wani ko wata a cikin masarautar su fara kulla mata mummunar dabi’a.
Da wannan tunanin ya shiga toilet yai alwala ya fito, gurin da furar sa ta kife yana nan ba a gyara ba, kuma a ka’ida Shaheedah ce ya kamata ta tsaya ta gyara masa, amman saboda bata saba ba kuma ta fita da b’acin rai shi yasa ko a jikin ta. Da kanshi ya tsabtace gurin dan ba zai iya barinsa har gari ya waye ba.
Sallah yai sannan ya yi ta addu’a tsawon lokaci kafin ya tashi ya hau kan gado, kwanciya yai tare da lumshe idanunsa. Khadija yake tunawa da yanayin yadda ya ganta cikin kayan bacci, be san dalilin da yasa yake yawan tunaninta ba. Amman ya fara jin cewa ya yarda da ita a cikin rayuwar sa, yana jin ta cikin zuciyar shi musamman yadda yaga tana nuna masa muhimman abubuwan da yai wasarere da su. Da kyar ya samu bacci ya dauke shi bayan ya duba sakkon da aka turo masa ta waya.
*WASHE GARI*
(SASHEN GIMBIYA KHADIJA)
Da kyar na iya tashi daga bacci sakamakon wani mummunan mafarki da nai akan Salman, bathroom na shiga ba jimawa na fito daure da alwala, sallaya na shimfid’a nai nafila ina idarwa nayi sallar asuba daga nan azkhar nayi ban tashi daga kan sallaya ba sai wajan karfe bakwai na safe. Wanka nai nazo na shirya kai na cikin wata atamfa d’inkin riga da zani, na dakko alkyabba na d’ora daga nan na fito zuwa parlour na inda na tarar da hadimai na suna ta aikin tsabtace gidan. Bayan sun gaishe dani ne na ce mutum daya tazo ta yi min rakiya sashen da bayi mata suke a cikin masarutar.
Tana gaba ina bin bayanta har muka karasa, tun a hanya dama nake ta samun yan gaisuwa haka da na shigo baiwayar tawa da ta rako ni tai musu bayanin ko ni wacece, nan da nan kuwa suka dinga sunkuyawa suna gaishe dani. Jakar hannu na da nake rike da ita, na bude tare da ciro kud’i na dinga rarraba musu sadaka da niyar Allah yasa mafarkin da nayi akan Salman ya zame masa alkairi. Sai da na tabbar na bawa kowa dama d’ari biyar-biyar na basu, suka dinga godiya kuwa kamar na basu duniya.
Ina kammalawa sashen Ammi na wuce inda na tarar kafarta ta dameta da ciwo, sai da na tabbatar tayi breakfast sannan na zauna na dinga matsa mata, tun tana hanani har tai shiru daga karshe ma muka fara hira ina ta sako mata labarin Salman yadda ya fara kiran sunan ta da yadda naga jikin nasa yana samun sauki. Allah sarki uwa tunda taji haka ta fara murmushi nasan ko ba a fada ba wata kyakkyawar addu’ar take sake yi masa a cikin zuciyar ta.
Na dade sosai a gurin Ammi sannan na koma sashe na, duk a takure nake babu wani aikin yi da zanyi bare ya debe min kewa. Wayata na dakko wacce take a kashe na lalibo lambar kawu Daddy, bugu uku ya d’aga cikin fara’arsa yake min magana.
“Yata ta kai na, ince dai lafiya lau kike ko?”
“Lafiya ta kalau kawu daddy, kwana biyu shine nace bari na kiraka mu gaisa.”
“Alhamdulillahi yarinya ta ai ta hakuri da zaman aure, na san kina da hakuri khadija, amman ki kara akan wanda kike da shi kinji? Allah ya yi miki albarka.”
“Amin kawu Daddy na gode sosai da addu’a. kawu da na ce wai babu yadda za ai na koma gurin aiki na, wallahi kawu na gaji da zaman kadaici ba aikin yi sai kwanciya.”
Dariya naji ya dinga yi, nai shiru ina tunanin abinda ya sashi dariya a magana ta, har na fara tunanin kodai ba ni yake yiwa ba sai naji yana cewa.
“Khadija ai ni yanzu bani da iko dake sai dai mijin ki, kuma gaskiya zai yi wuya a ce mai irin matsayinki tana irin wannan aikin. sai dai business wanda zaki kina daga zaune amman ba dai na fita office ba.”
Nai shiru a rai na ina tunanin ai ba zama nazo yi gidan sarautar ba bare nayi tunanin tarewa ta har abada, harga Allah ina son aiki na dan yana cikin buri na tun ina karama, ta ya za ai na samu kuma yanzu a ce sai dai na ajiye shi kacokam saboda kawai sarki ya aure ni. muryar kawu daddy ta katse min tunani na, inda yake cewa.
“Bana son ki matsa masa akan wannan aikin khadija, auranki yafi wannan aikin da kike son fitowa kiyi. ina miki fatan alkairi a duk inda kike.”
Ba haka na so ji ba, amman babu yadda zan yi na musa masa sai kawai nai dauriya wajan cewa.
“Shikenan kawu Daddy na gode Allah ya kara girma da lafiya mai dorewa.”
“Amin yar albarka na gode miki nima. ki gaida min da mai gidan.”
Na yi shiru ban amsa ba har ya katse, kamar jira na gama wannan wayar naji telephone din dakin ta fara ringing, na tashi da kyar naje na dauka ina turo baki tamkar ina gabansa. cikin kasalalliyar muryarshi yake min magana a tausashe.
“Ki kawo min wayar ki yanzu.” Cikin rashin kulawa da maganar tashi nace.
“Okay bari na aiko ma da ita.”
“No… kuzo tare da ke da wayar.”
“But amman ni….”
“Ina jiranki.” Ya katse.
Wannan mutumin akwai iko, gabaki daya bani da amfani a gurinsa sai yana da bukatar nai masa wani abin. Tashi nai na shirya cikin wasu riga da skirt english, wai ko zan iya haduwa da Shaheedah. nasa hijabi na har kasa sannan na dauki wayar na tafi. Ina shiga na tarar babu kowa, ban kula ba naji an janyo ni nai baya, gashi an toshe min baki saboda kar na yi ihu. Sai da aka kai ni wani guri mai duhu kafin a sakar min baki na, nai saurin fincikewa daga rikon da ya yi min dan na gane shi ta hanyar jin daddad’an kamshin sa.
Wani irin kallo na bishi dashi be kalle ni ba sai dakin da yake bi da kallo bayan ya kunne haske, haushi ya kuma kamani ji nake kamar na rufe shi da duka saboda takaicin da yake bani. Ya kamo hannu na tare da zama akan kujera. gurin mai kyau cike da littattafai da alamar library ne, ya tsaru an ajiye kowane littafi a inda ya dace. Ya rike ni da hannu bibiyu tare ba tare da ya yi magana ba, na maido da tunani na kanshi ina kare masa kallo cike da mamakin yadda yake rike dani nace.
“Lafiya dai ko?”
Tamkar na yi da dutse, har na hakura da bani amsar da nake so ya yi sai naji yace.
“Ina son na yarda dake, yarda irin wacce ake kira da amana.”
“Toh amma shakku kake yi ko kuwa ka yarda dani din har cikin ranka?”
Dagowa ya yi ya kalle ni muka hada ido dashi ta cikin glasses din fuskarsa. Ya lashi kasan jan lips din sa…..
_Duk wani shaukin typing da kara yawan sa, Yana tattare ne da yanayin yadda makaranta ke sharhin sa, Comments na karawa marubuciya kwarin gwiwar rubutu, Haka dena shi yana kashe mata gwiwa wajen fargabar yin sa… Makaranta books din zafafa.. A dinga comment ko writers saji kwarin gwiwar kara yawan typing_
_Sannan Afuwan Pls.. A dinga yiwa marubuciyar kibiyar ajali uzuri 👏🏻idanu hud’u take amfani da.. So yanayin typing dina dana sauran writers dole bazai zo d’aya ba. Ahakanma ana kokartawa. Akwai lokacin da dole zaka ajiye typing don karka rubuta abu ba daidai ba, Ko ka gajarta shafin.. _
_Hakki ne muka dauka dole mu sauke shi.. Dan Allah a dinga uzuri. Me cewa kibiyar ajali na jan k’afa, Ayi uzuri Pls 😊k’arshen gaskiya ta kenan..!_
_Kaunar kauna fisabilillahi masoyan zafafa❤️❤️_
ZAFAFA BIYAR
NA KUDI NE:::
Duka BIYAR 5 zaku samesu akan garabasar naira 700 kacal,
Guda hudu 4 Kuma 500,
Guda uku 3 Kuma 450,
Guda biyu 2 Kuma 400,
Guda daya akan 300.
Ma’ana
Each one is 300
2 is 400
3 is 450
4 is 500
5 is 700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO- *0812652655*
ACCOUNT NAME- *HAFSAT LAWAN GAMBO*
BANK NAME: *ACCESS BANK*
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*+234 903 234 5899*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
*09033181070*
Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO
TEAM#ZAFAFABIYAR🔥
GIPHY App Key not set. Please check settings