Advertisement
*JUHUD*
*(OUM HAIRAN)*
Advertisements
*(Pure love sex nd romantic story)*
*LAST FREE PAGE TEN 10*
*Qarshen Free page na labarin nan kenan idan baki biya ba kiyi sauri ki hanzarta biya ta wannan hanyoyin dake qasa*
*Regular group 300 VIP 600 via bank Account 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank or card for This number 09013718241 only WhatsApp or vtu only for dis 09031307566*
Advertisements
*DON ALLAH IDAN KIN/KA TURA KUDINKA BANA BUQATAR DOGUWAR GAISUWA KAWAI EVIDENCE OF PAYMENT DA SUNAN LITTAFIN DA KIKESO NAKE BUQATAR GANI KO BANA ONLINE KIBARMIN IN NA HAU ZAN GANI KUMA ZANYI ADD NAKI A GROUP DINA COURSE MUTANEN DA YAWA.*
*CIGABA*
Bai jira abinda zasuce ba ya fice daga dakin yabarsu zaune da sakakken baki suna kallon kallo ta kalli Ya’isha tace “meye yake nufi da inada kadarar da tafi kudi Ya’isha don Allah Amrah idan kun gane ku ganar dani nikam daqiqiya ce ban gane komai ba” wata iska Ya’isha ta furzar tace “akwai matsala ne Juhud muje rabuda wannan dan iskan ni dama nasan abinda yaketa yiwa raragefe kenan” fita sukayi har zuwa lkcn kanta a kulle yake kalaman nasa sunayi mata yawo a qwanya saidai ta kasa gane inda zatayi musu matsugunni Baffa’am dinta bariki yana taba bariki? Meye ma ma’anar barikin?”
Da wannan tunanin suka shiga gda tun daga nesa suka hango Kareem tsaye jikin mota ya zuba musu ido kamar me nazarinsu har suka qaraso suka giftashi kowa da abinda yake saqawa a zuciyarsa “Aminah” taji an kirata da asalin sunanta turus sukaja suka tsaya dukkansu ya tako cikin takunsa na isa ya iso gabanta ya kalli qannen nasa dukka suka watse ya rage daga ita saishi, hannu yasa ya dago kanta ta lumshe idonta tana shaqar qamshin turarensa me tsayawa a rai yaja numfashi tare da furzar da wata iska me zafi yace “duk da kasancewata abin gudu a gurinki saboda Ina doraki akan tafarkin daidai Aminatuh bazan fasa fada miki ba Babu biyayya gurin abokin halitta wajen sabawa ubangiji zanso Kuma zanyi alfahari idan ya kasance nasihar da nakeyi miki daga ranar da kika tsinci kanki cikin wannan ahli me rangwamen tarbiyyar islama ta zame miki abar tunawa a duk lkcn da wani abokin halitta ya gayyaceki domin aikata sabon Allah.
Nasani cikin watannan da kika samu goyan baya daga Momy kin fara biyewa su Ya’isha kina binsu kuna fita chilling kune har Dikko Club wai abin takaicin hardake a cikin yan shiga rawa bama ki tsaya iyakar kallo ba”
Kallonsa tayi da sauri idanunta ya ciko da qwallar da tun dazu take maqale jikinta ya dauki rawa, murmushi yayi yace meye naki na firgita bayan Baffa’am dinki baisan rayuwar da kika zabawa kanki ba?” Sake firgita tayi bakinta na rawa tanason mgn ya katseta da hannunsa yace “karkicemin komai Aminah kinji dadin zuwa club har kina bada tabbacin gobe ma zaki koma ko?”
Girgiza masa kai tayi haqoranta na rawa tunaninta Ina yasan wannan sirrin da sukayishi iyakar su uku sukayi alqawarin bazasu fadawa kowa ba?” Murmushi yayi ya kama hannunta yace “inasonki da gasken gaske Juhud meye ribarki idan aka tashi mahaifanki aka nuna musu ke matsayin yar rawar Club?”
Girgiza masa kai tayi jikinta duk yayi sanyi tace “Allah Amrah ce tajani tace dole saina shiga Kuma Dana shigama tsayawa nayi ban iya irin rawar da sukeyi ba”
Zubanta ido yayi Yana kallon yanda duk ta tsorata yaji dadin hakan ya shafa kansa yace “da nayi niyyar fadawa Baffa’am dinki Amma idan kikayi alqawarin bazaki qara zuwa ba to zan rufa miki asiri ke qilama ya sani fah don duk motsin da zakiyi abune me sauqi su sani din” batasan sanda tace “insha Allahu baima sani ba bakuma zai sani ba bazan qara zuwa ba”
Yaji dadin hakan yace “ok meye kukaje yi a dakin Muntaz?” Nan taji wani dukan saukar aradu ta dago suka hada ido mugum kwarjini ne dashi shima kamar Baffa’am dinta duk iyakar zille zillensu idan aka hadasu dashi basa iyayi masa qarya, cikin in…Ina tace “ha….hqr mukaje mubashi yaci gaba dayi Mana lesson shine yace wai saidai na rinqa biyansa Wai banida kudin biyansa Amma inada kadarar da tafi kudi ni na kasa gane me yake nufi Ya Kareem ko kai ka gane?……”
“Wht?” Ya furta da qaraji ta dago da sauri ga mamakinta sai taga gabadaya ya hargitse jikinsa har wata rawa yakeyi idanunsa sun kada sunyi jawur ya dafe kansa yace “innanillahi wa innah ilaihir raji’un”
Daidai lkcn Muntaz ya fito cikin shirinsa na tafiya qwallo hangosu tsaye yasashi daure fuska ya nufi motarsa ya bude zai shiga Kareem ya daga murya ya kirasa ya tsaya batare daya juyo ba, matsawa yayi bayansa yace “bantaba tunanin akuyancinka yakai ka rinqa farautar lalata rayuwar Aminatuh ba sai yau so inason kasani wlh tallahi idan naji ko naga wani abu akasin daidai ya faru da Juhud billahil lazi saina tona maka asiri dan iskan banza dan iskan wofi duk kuyangin gdannan da bayi Basu isheka ba saika tsallaka kan yar Amana…….” Dakatar dashi yayi yace “dakata Mal kaima fah abinda nakewa shine kakeyiwa duka dodo daya mukewa tsafi aikin banza kaine kake tunanin ci da addini ni tun tuni na dade da fahimtar ka dade da lalube…….” Wani gigitaccen mari ya sauke masa ya shaqesa suka kama kokawa ya rinqa gwara masa kai a jikin bishiya Mai Martaba dake tahowa ya hangosu ya iso da sauri shida dogaransa daqyar ya bambare hannun Kareem daga wuyan Muntaz, duk da haka Muntaz bai rusuna ba cewa yake wlh ko kanaso ko bakaso tunda nayi niyya saina aikata qarshen kishi kasa a daura maka aure da ita yau dinnan ko a gdanka take saina mayar da yawuna saidai idan mutuwa nayi”…………
*THIS BOOK IS NOT FREE… REGULAR GROUP 300 VIP 600 VIA BANK ACCOUNT 0255526235 FAUZIYYA TASIU UMAR GTBANK OR CARD FOR THIS NUMBER 09013718241 ONLY WHATSAPP OR VTU ONLY FOR DIS 09031307566*
*DON ALLAH IDAN KIN/KA TURA KUDINKA BANA BUQATAR DOGUWAR GAISUWA KAWAI EVIDENCE OF PAYMENT DA SUNAN LITTAFIN DA KIKESO NAKE BUQATAR GANI KO BANA ONLINE KIBARMIN IN NA HAU ZAN GANI KUMA ZANYI ADD NAKI A GROUP DINA COURSE MUTANEN DA YAWA.*
*Oum Hairan*
GIPHY App Key not set. Please check settings