JUHUD 6

Advertisement

 *JUHUD*

*(OUM HAIRAN)*

Advertisements

*( Pure love sex nd romantic)*

*FREE PAGE SIX 6*

*SANARWA*

Wannan littafin na kudine idan kina buƙatar ci gaba da samunsa bayan gama free page kiyi ƙasa a ƙarshe an faɗi hanyoyin da zakubi don biya da karatu cikin Aminci.

Advertisements

*SUBSCRIBE*

_DUNIYAR LITTAFAN HAUSA TV_

https://www.youtube.com/channel/UCcAjVQ74qod9_dL0e_AqkiQ

     

*TUNATARWA*

Kasance me yawan tuba tabbas mutane masu yawaita Istigfari suna samun kusanci da ubangiji sana qofofin arziqinsu na budewa a koda yaushe, domin samun gafarar ubangiji da kusanci dashi sune mafi qololuwar arziqin duniya dana lahira.👌🏻

*CIGABA*

Yana kallonta Yana kallon likitan har ya gama rubuce²nsa ya juya zai fita ya riqosa yace “meye kake tunani game da ita wanne taimako zaka iya bata bayan wanda kake bata yanzu?” Dubansa yayi da alamu na rashin fahimta yace “ban fahimta ba Sir” iska ya furzar ya juya ya fice daga dakin yana cewa idan bata daina haukanna ba kada ka qara kirana tunda bakada abinyi nonsense kawai” 

Qwafa Dr Razaq yayi shikam yaga mutane da dama cikin aikinsa Amma baitaba ganin mutum mara sanin haqqin mutum kamar Conel Rasheed ba, tabe baki yayi ya fice ya turo wata nurse tazo ta zauna da Juhud, abun kamar wasa ba ita ta farka ba saida aka kwana uku kullum cikin yimata Allurai ake jini kawai Saida akasa mata leda uku biyu a jikin Rasheed aka diba daya aka siya aka jorner mata, koda ta tashi farkawa ta farka cikin hayyaci tsakiyar dare ta farka babu kowa a dakin sai Nurse Karima ta zubanta ido tanason tuno a Ina take sannan wace wannan din?

Matsowa Karima tayi gabanta ta zauna tana qare mata kallo tunda take ganin kyawawan mutane bata taba ganin halitta me sihirtaccen kyau kamar wannan yarinya ba numfashi ta sauke tace “sannu ya jikin naki Ina fatan dai kinajin sauqi?” Maimakon ta bata Amsa sai taga tayi qasa da kanta taja ajiyar zuciya tare da dafe kanta abubuwan da takasa tunowa suna dawo mata ta wani zabura zata miqe daidai lkcn da Dr Razaq yake shigowa ya qaraso da gudu suka riqeta ta dago tana kallonsu daidai hawaye ya ballewa idanunta cikin fullanci tace “da gaske sun qone bukkar Innatu tana ciki sun kasheta?” Kallon juna sukayi Nurse Karima tayi saurin qaqaro murmushi tace “aa basu kasheta ba itace ma take jinyarki kiyi hqr kada ki tashi ciwo ne a qirjinki” 

Sai yanzu takai dubanta ga qirjinta dake nade da bandeji tana girgiza kai hawayenta Yana qara yawaita ta zame daga hannunsu ta koma ta kwanta dafe da kanta ta saki wani marayan kuka me kashe jiki da tsuma zuciya ta tuna lkcn da Hamma Manga ya daga adda ya sauke mata a qirjinta ta tuna lkcn da taji gabanta ya Fadi ta nufo rugarsu da gudu ta hangi hayaqi Yana tashi ta tuna lkcn da Baffa Buba ya jata ya nufi daji da ita Kuma ta tuna kalamansa, shikenan yanzun sauran gatanta ya tafi ya barta batada sauran me duba rayuwarta, shikenan ta tabbata marainiya maraici mara galihu inama ace ta mutu ta huta meye yasa bata mutum ba meye amfanin sauran rayuwarta, ribar me su Baffa Ribado suka samu ko zasu samu da jefa rayuwarta cikin tsaka me wuyar da sukayi?……

Tambayoyin da taketa yiwa kanta kenan ta kasa samun Amsarsu gashi batada me bata amsar sosai take shassheqa tanajan zuciya, babu wanda yayi yunqurin hanata kukanta saboda sun fahimci damuwarta bata buqatar rarrashi lkc ne kawai yake da ikon rarrashinta, itadai a wannan dare idan barawo ya rintsa Juhud ta sake Rintsawa saqawa take kawai da warwarewa ta taba lalitar jikinta yakai sau uku taji wadannan abubuwan da Innatu ta bata sunanan.

Da asuba Nurse Karima ce ta taimaka mata ta kaita bayi tayi alwala babu damar wanka saboda baa buqatar ruwa ya taba ciwon dake qirjinta a zaune tayi sallar duk da cewa ba wani ilimin addini ne da itaba cikin surorin qur’ani uku ta iya Fatihatul kitabi Iklas da Khausar su dai take karantawa a duk wata sallarta bayan ta idar ta daga hannunta tanason yima iyayenta addu’a Amma bakinta yayi nauyi ta kasa furta komai sai yararin hawaye da batasan ta inda yake fitowa ba da yakebin kuncinta ganin cewa addu’ar batta samuwa yasata sauke hannunta ta juya ga Nurse Karima dake hada kayanta tace “inane nan?” Juyowa tayi tace “barikin sojoji ne” wani dam gabanta yayi tace “bariki Kuma oye ayye na shiga Sha biyu waye ya kawoni nan…..” 

Mgnr ce ta maqale lkcn da taji an turo qofar an shigo wani qamshi ya gauraye dakin nurse Karima ta Sara masa tace “Sir Alhmdllh anyi nasara petiant dinka ta samu lfy Amma…..” daganta hannu yayi yace “nasan me zakice jeki kawai banson surutu” sumsum ta fice yaja tsaki ya juya ya zuba idanunsa ga Juhud daketa barin jiki yau taga mala’ika ido biyu a rayuwar Juhud babu abinda take tsoro kamar Soldier batason ko a hanya su hadu yau gata a cikin barikinsu wannan wacce irin masifar qaddara ce daga wannan sai wannan?

Inuwarsa da taga ta lullubeta yasata dago kanta kafin ta gama sauke idanunta akansa fitsari ya fara qwace mata hakan yayi daidai da lkcn daya daka mata wata uwar tsawa yace “meye hakadin banason shashanci sanyi kikeji da zaki rinqq wata tsumar jiki?” Kafin ya rufe bakinsa ta saki kuka me gunji cikin kukan take cewa “ni dama nasani mutuwar Innatu bazata taba zamemin Alkhairi ba wlh gara na mutu na hutt…..” Ko kadan bai daukan shirme da raini hakan yasashi shaqota ya miqar da ita ta rintse idonta lkcn da shikuma yayi saurin sakinta saboda qarnin manshanun daya shaqa a hancinsa daya sanyashi jin amai ya yunquro masa da sauri ya nufi bathroom din ya fara kelaya aman ta miqe zaune tana jan zuciya har yanzu jikinta rawa yakeyi. Fitowa yayi daga bathroom din yana qwafa baiko tsaya a dakin ba ya fice ya jima da fita kafin ya dawo dauke da wata jaka a hannunsa ya cilla mata yace “kije kiyi wanka ki cire abinda yake qarni a jikinki bana zama inuwa daya da qazami”

Dagansa kai tayi cikin yanayin tsoro ya sake ajiye gongonayen Madara da Milo da nescafe ya fita can saiga wata Christy ta shigo dauke da flast na ruwan zafi da wata kula a hanunta ta aje ta juyo ta watsawa Juhud wani dan iskan kallo ta tabe baki tace “gashinan yace ki tashi kiyi break kafin ya dawo” ko kallon tsiya bata samu gurin Juhud ba balle na arziqi bama tasan tanayi ba ta lula duniyar tunanin rayuwarta ta baya hakan yabata damar qare mata kallo taja tsaki a ranta tace “dubeta kamar aljana” a fili Kuma waya ta dauka ta Kara a kunnenta tayi turancinta Juhud ta juyo da sauri ta kalleta sai taji ta burgeta tanason mutumin da ya iya turanci a rayuwarta a fili tace “lah gwaggo kin iya turanci nima zaki koyamin?” 

Dariya abin ya bata ta Harareta tace “saboda yar iskance niba me zai hana na tsaya koyawa bakin da bai iya ko A ba turanci qazama dake” bataji haushi ba domin ko dukanta zatayi indai akan turanci ne to zata jure “qwalqwal tayi da ido tanason yin mgn ya turo qofar gabanta ya Fadi tayi saurin zubansa ido sai yanzu ta ganeshi tace “lahhhh Kado dama kaine ashe kaine wanda ka siyemin nono na ranar da su Baffa Ribado suka qonemin Innatu na….” Shiba ma’abocin dariya bane hakan yasashi shafa sumarsa yace “dan uwarki waye Kadon?” Nandanan ta nutsu ganin ya nufota yace “wato ke dama da ganinki zakiyi raini nace kiyi wanka shine saboda kin quna kamar yanda aka qone Innatu kikaqi yi salon ki qara sani amai jibi babu abinda yake tashi sai qarnin manshanu a dakin nan” 

Kallon Christy tayi idanunta sun ciko da qwallah da sauri Christy ta dauke idonta tace “baby kace qanwarka ne Kuma naji tana mgnr tallar nono ya haka?” Harara ya maka mata ya juya ga fast din tea din ya dauki cup ya hada mata ya miqa mata da biredi sai soyayyen qwai da dankali, tea din ta karba hannunta na rawa dama yunwa takeji sai bread din ta soma turawa yanda takecin abincin a yunwace yasashi zama ya zuba mata ido ta cinye bread din ya sake yaga ya bata ta Kuma cinyewa tama manta da shayin Saida taji ta qoshi sannan ta kora da shayin ta ajiye kofin tayi gyatsa ta rinqa kallon qwan tana girgiza kai.

“Ya sunanki?” Abinda taji ya fada kenan ta juyo da sauri tace girogal….. Da mamaki da takaici ya  dubeta yace “sunanki kenan girogal?” Dagansa kai tayi tace “ayyah Kado tausayinta nakeji yanzu shikenan kun cinye mata qwanta da kinbar mata da ta haihi yaranta ta rinqa jansu suna tahiya kiwo” wata muguwar dariya ce ta qwacewa Christy lkcn da taga ya dafe kai ya juya ya galla mata harara ta gimtse dariyar kawai taga yakai hannunsa ga wandonsa ya fara zaro belt dinsa nandanan ta nutsu ta saita hanya tasan dukansa sai tayi wata guda tana jinya Juhud nacan tana sharar kwallah tana cewa Allah sarki girogal Allah shine zai saka miki kamar yanda zai sakamin nima…..” Qara ta saki lkcn daya zumbuda mata belt din tayo qasa ta fadi aikuwa ta shige qarqashinsa tana ihu ya qwace qafarsa yace “ina tambayarki kina yimin hauka” da sauri tace “Aminatuh Juhud Baffa Haro Innatu Indo…..” Jefar da belt din yayi ya dafe kansa ya fice daga dakin ya nufi gidansa yana shiga ya zube a kujera yace “Rasheed ka daukowa kanka da shegen kwashe²nka fitowa Christy tayi daga daki kasancewar ta rigashi shigowa ta zauna tana matsa masa qafa tace “baby anya yar qauyen nan qanwarka ce?” Cikin hassala yace “bansani ba kada ki Kuma tambayata game da ita meye damuwarki da sanin wacece itan?” Jan bakinta tayi ta tsuke yaja tsaki ya miqe ya shiga dakin da baya amfani dashi a gdan ya soma gyarawa kasancewar shima kamar dakinsa yake da katifa da wardrobe da TV na bango sai bathroom,

Gyara yayi masa na sosai sannan yayi wanka ya fito ya fice daga gdan cikin gari ya shiga ya nufi wani Mall ya siyowa Juhud kaya bazai iya tantance tsayinta ba Amma ya qissimata da Ya’isha qanwarsa duk kayan daya diba mata qananu ne sai hijjaban sallah ya koma gda ya tarar da Christy a kitchen tayi masa sannu ya Amsa Yana shigewa dakin daya gama gyarawa ya zuba kayan a wardrobe ya dauki mukulli ya fito Christy ta tareshi da cewa “ga abincin petiant din nan am naji kamar tace sunanta Aminatu ko?” Warmer din kawai ya karba ya fita ya nufi asibitin lkcn ta shiga wankan da Nurse Karima ta takura mata tayi kasancewar an kwance bandejin saura dinkin ta Nina mata yanda zatayi wankan sannan ta barta koda ta gama wankan ta dauki riqarta ta mayar ta fito riqe da towel din da Nurse Karima ta bata domin daurowa.

Da sauri tayi baya jikinta ya kama tsuma tana ganinsa ta tuna da dukan da yayi mata dazun ya kuwa daure fuska yace “kici abinci na kaiki gda na gaji da yawon asibitin nan ba Mai martaba ne babu lfy ba ba Mom ba” ajiyar zuciya tayi ta rinqa takowa da sanda dariya kecin Karima babu halin yi, a haka harta iso ta karbi doguwar riga ta rinqa juyata a hannunta tana kallon duwatsun jikinta sai ta ajiye ta Kuma daukar wata taga har tafi ta farko kyau a haka Saida ta gama qarewa kayan kallo  duk ta ajiye ta dauki rigarta ta Fulani zata mayar Karima tayi saurin riqewa tace “meyesa bazaki Sanya wadannan ba?” 

Turo baki tayi tace “dagawa da almubazzaranci niba yar kowa ba haka kawai nasa kayan sarakai salon  asani a wutar jahannama …….. Kallon da ta dago taga yanayi matane yasata rufe bakinta da hannunta yayi Alama da yatsansa Karima ta dauki wata milk ta miqa mata ya kafeta da idanu babu yanda ta iya hakansn ta karba tasa tana qunquni tana hawaye ita a dole anyi mata laifi ansata almubazzaranci.🤣

Flat ya dauka ya zuba mata tuwon shinkafar da miyar agusi da tantaqwashi da qashin rago ya aje mata a qasa ta ya sake kafeta da idanunsa tayi qasa da nata tare da zama a qasan ta Sanya hannu tana jajjagula tuwon tana gutsurar gaya tanaci idan ta dauki saita goge miyar sannan takai bakinta, Karima ce taga abin yayi yawa tace “meyesa bakicin miyar” kamar me jiran kadan kuwa ta fashe tace “bayan mun fada muku kudaina cinye kaza da shanuwa da tumaki Amma kunqi ku Kadawan nan bakuda Imani nikam bazanci nama ba idan naci sai Allah yayi Mana hisabi” 

Ba Karima ba shi kansa Saida ya murmusa ya zubanta ido yanda take tsakurar abincin take karkade miyar abin yaso bashi dariya saidai bazaiyi ba ta samu fuskar rainashi haka ya tsaya akanta Saida ta cinye tuwon sannan ya zauna yana karkada qafa yace “uhum maza cinye naman ki shanye miyar….” Yanda ta zaro ido yaso yasa dariya ta kubce masa ya maze yace “idan kinqi” hannu yasa Yana qoqarin zare belt dinsa tayi saurin daukar kwanon ta kafa baki ta shanye miyar tas sannan ta rinqa yagar naman kamar tana yagar jikinta har Saida ta cinye ya miqe ya dubi Nurse din yace “tayata fito da kayan nan zata koma gda ta rinqa zuwa ganin likitan kafin ta qarasa warkewa” ficewa yayi Karima ta debi kayan ta fita ta miqe tabita da sauri ai tana zuwa jikin motar ta cake taqi gaba taqi baya tsoro ya kamata ta janye ta koma gefe ta rakube bayan sun gama zuba kayan ya juyo ya kalleta tayi wani kalar tausayi ta sakeyin raurau da fuska yar fara’ar da yakeyi ya daina yace “kizo ki shiga mu wucce malama” girgiza masa kai tayi ya cije lebe a fili yace “ciwon kai wannan yarinyar zatayi taurin kan tsiya” itadai bataji me take cewa ba Kuma bata bar inda take ba Saida ya daka mata tsawa tayi saurin nufar  motar tana zuwa gabansa ta zube cikin in…Ina tace “ka rantse bazaka saidani ba Baffa’am yace masu sulluwa suke sace mutane suna kaiwa burnin Kano da Lagus suna saidawa anayin fate²nsu………….

*THIS BOOK IS NOT FREE… REGULAR GROUP 300  VIP 600 VIA BANK ACCOUNT  0255526235 FAUZIYYA TASIU UMAR GTBANK OR CARD FOR THIS NUMBER  09013718241 ONLY WHATSAPP OR VTU ONLY FOR DIS 09031307566*

*Shares Please*

*Oum Hairan*

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like

JUHUD 10

Advertisement  *JUHUD* *(OUM HAIRAN)* Advertisements *(Pure love sex nd romantic story)* *LAST FREE PAGE TEN 10* *Qarshen Free…

JUHUD 2

Advertisement  *JUHUD* *(OUM HAIRAN)* *(LOVE AND ROMANTIC STORY)* Advertisements *FP TWO* *SUBSCRIBE* _DUNIYAR LITTAFAN HAUSA TV_ Advertisements https://www.youtube.com/channel/UCcAjVQ74qod9_dL0e_AqkiQ…