TAYI MIN KANKANTA 10

Advertisement

 ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€

 *TAYI MIN ฦ˜ANฦ˜ANTA*

๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€

*Zahra Surbajo*

*10*

Advertisements

Murmushi mummy tayi ta dafo kanta tace “ษ—iyata sauฦ™i yasamu kenan?”

  Murmushin itama zahra tayi ta sunkuyar da kai ฦ™asa,

Daddy ne ya ฦ™araso gurin ya zauna sannan yace”dama wannan lokacin nake jira kuma gashi Allah ya kawo mu,zamu so ki sanar damu ko ke wace ce,dan musan taya zamu taimakeki ki koma ga danginki”

Hawayene ya zubowa zahra tasa hannu ta goge,sannan tace”ni bani da dangi,baffana yayi hatsari ya mutu,innata ฦดan bindiga sun kasheta,tade taษ“a shaidamin muna da ฦดan uwa a gombe,kawu modibbo amma sun bar gomben kuma batasan inda zata gansu ba”

Kallon kallo suke tsakanin hajiya da Alhaji,bakinsu har rawa yake gun jefo mata tambayar”ya sunan innar taki na Aynihi?”

“hauwa’u sunanta”ta basu amsa.

Advertisements

Rungumota hajiya tayi jikinta tana hawaye tace”tunda nake kallon fuskarki naga kamar nasanki,amma na kasa gasgata hakan,ashe ko ikai fuskar hauwa nake gani ataki fuskar,Allah mungode maka”

Daddy sosai yake murna da ganin ษ—iyar ฦดar uwarshi,hotunan inna nada ya nunawa zahra ayko murmushi take tana faษ—in”innata ce wannan dama kunsanta”

Daddy ya gabatar mata da kanshi da iyalinshi a matsayin dangin nata yamata bayanin komai,ayko itama kuka tasa najin daษ—in ganinsu.

Shide Muhammad abun koma masa yayi kamar a film,daga neman shawarar akaita gidan mahaukata shikenan abu ya juye ta komo ฦดar uwarsa.

Basu bar falon ba se da dare yayi sosai anata hira,sosai daddy yasaki jiki da zahra wacce yake kallo amatsayin sauran danginsa da suka rage masa a duniya.

Washe gari da safe bayan muhammad ya duba zahra,cire safar hannunshi yayi ya janyo kujera ya zauna yana fuskantarta,ita de tunda ta fahimci shine ke dubata kunyarshi takeji,da ฦ™yar take iya haษ—a ido dashi.

“zahra kin bada labarin komai naki,amma  baki sanar damu wanda kuma ya miki fyaษ—e ba?wanda a matsayinmu na ฦดan uwanki zamu so musani”muhamnad yace cikin tattausar murya.

Hawayene ke biyo idonta a hankali tace”na barshi a matsayin sirrina,don Allah karka kuma tambayata”ta faษ—i cikin kuka.

Taษ“e baki yayi sannan yace”bazan kuma ba,amma kisani in ni baki faษ—a min ba dole zaki faษ—awa mijinki ay”yana kaiwa nan ya fice daga ษ—akin.

Hankalin zahra yayi ฦ™ololuwar tashi jin furucin muhammad,tabbas dole zata sanar da mijinta wannan mugun labarin,duฦ™ar da kanta tayi ฦ™asa tana kuka me tsuma zuciya.

A  haka mummy ta shigo tasameta,sosai hankalin mummy yatashi janyota tayi jikinta tashiga tambayarta abinda yafaru,cikin kuka zahra tace”mummy yanzu rayuwata a haka zata ฦ™are kenan,bazan taษ“a aureba,in ko zanyi auren dole sena cewa mijina anmin fyaษ—e? inde hakane nida aure har abada”ta ฦ™arasa maganar cikin kuka.

Tausayintane ya kama mummy ta shiga rarrashinta da duk wata kalma me daษ—i,da ฦ™yar tayi shuru.

Mummy ษ—akin daddy taje tasameshi yana shirin fita,ganinta cikin yanayin damuwa ne yasa ya nemi guri ya zauna yace”hajiya lafiya kuwa?”

Cikin damuwa tace”Alhaji yarinyar nan na cikin damuwa gameda fyaษ—en da aka mata, baka ganin akwai buฦ™atar a binciko ko waye a hukuntashi sannan asa shi dole ya aureta?”

Shuru Alhaji yayi na ษ—an lokaci sannan yace”nemo ko waye beda wani amfani,fyaษ—e de anriga an mata,ba abinda ze sauya hakan,kuma ni modibbo inde na isa da Muhammad to tabbas shine ze auri Zahra,dan shi kaษ—ai ze rufa asirinmu”

Mummy itama ta gamsu da bayanin na alhaji,dan haka kwarin guiwa ta ฦ™ara bashi kan ฦ™udirin nasa,sabida Allah yasani tana tausayin zahra matuฦ™a.

Alhaji be samu zama da Muhammad ba seda dare bayan ya dawo daga gun ayki.

Lokacin daya sanar dashi hukuncin daya yanke akanshi da zahra muhammad kaษ—anne beyi fitsari a wando ba sabida firgici,bakinsa har rawa yake yace”daddy don Allah kayi haฦ™uri kabar maganarnan,nifa bana sonta,gaba ษ—aya zahra nawa take da har zaay batun aurenta,ni tayi min ฦ™anฦ™anta daddy pls”

Yafaษ—i kamar zeyi kuka.

“muhammad ba shawara fa nake nema ba,hukuncin dana yanke nake faษ—a maka,wannan duk raayinka ne,ba nawa ba,nan da wanne lokacine zahra zata iya warkewa gaba ษ—aya” daddy ya buฦ™ata cikin haษ—e rai.

Jikin Muhammad a sanyaye yace “wata guda”

“nasa lokacin auranku nan da watanni biyu masu zuwa,na ษ—auke maka komai,kaje ka fara shiri”daddy ya faษ—i sannan ya miฦ™e yabar gurin.

Muhammad na zaune kamar wanda aka dasa,yama rasa me zeyi yaji sanyi aransa,da ace ze iya kuka to ba shakka kukan ze ta rusawa.

A Hankali ya miฦ™e ya nufi ษ—akinshi jiki a sanyaye ya faษ—a gado yana nazari,shide gaskiya tayi mishi ฦ™anฦ™anta a aure to in ya aureta yace ya auri wa?shi fyaษ—en da aka mata ba damuwarshi bane kawai de shi yafi son mace ฦ™atuwa ne.

Muje zuwa

Surbajo for life.

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like

TAYI MIN KANKANTA 7

Advertisement   ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€  *TAYI MIN ฦ˜ANฦ˜ANTA* ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€ *Zahra Surbajo* *7* Advertisements *Bayan shekara ษ—aya* “Modibbo ษ—iyata zata mutu…

TAYI MIN KANKANTA 34

Advertisement  ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€  *TAYI MIN ฦ˜ANฦ˜ANTA* ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€ *Zahra Surbajo* Tayi min ฦ™anฦ™anta bafa na kuษ—i bane,shimfiษ—ar aurena shine na…

TAYI MIN KANKANTA 33

Advertisement   ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€  *TAYI MIN ฦ˜ANฦ˜ANTA* ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€ *Zahra Surbajo* *Tayi min ฦ™anฦ™anta bafa na kuษ—i bane,shimfiษ—ar aurena shine…

RAYIMIN KANKANTA 23

Advertisement ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€ *TAYI MIN ฦ˜ANฦ˜ANTA* ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€ *Zahra Surbajo* Advertisements *23* Likitocine suka rufu akanta dan gano meke damunta,…

TAYI MIN KANKANTA 14

Advertisement  ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€   *TAYIMIN ฦ˜ANฦ˜ANTA* ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€ *Zahra Surbajo* *ayi haฦ™uri ina tare da mara lafiya ne,shiyasa,* Advertisements *14* Tana…

TAYI MIN KANKANTA 27

Advertisement  ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€  *TAYI MIN ฦ˜ANฦ˜ANTA* ๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€๐ŸŽ€ *Zahra Surbajo* *To sabon sauyi acikin tafiya,๐Ÿ˜Šakwai sabon novels ษ—ina dazan saki…