Advertisement
****************
‘Dan shiru afia tayi Dan Kamar Bata fahimci abinda farhat din tafada ba ta sake Kiran sunanta tana tadota gabaki daya ta zaunar da ita tana cewa”
Ina aunt dinki tashiga bangantaba.
Mutsitsika idanuwa farhat tayi tareda budewa tana ‘yar guntuwar hamma ta baccin yasaketa ta kalli afia din tace”
Bata Nan jiya jekadi tace Daddy na Kiranta tatafi.
Advertisements
Shiru afia tayi tana neman dauke wuta sbd wani dumm dataji kunnuwanta na dauka saidai har lokacin takasa fahimta gwari gwari takeson ayi Mata Dan Haka
tasake kallon farhat din tace”
Dad ya Aiko Kiran jiya da dare?
Data tafine haryanxu Bata dawoba kokuwa tadawo yanzu tasake fita??
Saukowa gadon farhat tayi tana cewa”
Bata dawoba.”toilet ta nufa ta shigewarta tabar afia daskare agurin tana dulmiya cikin wani irin dogon nazarin tunanin
Shin lafiya dai??kokuma tace menene zaisa NURU kwana gurin dad?kodai wani abin yakuma faruwane Dan ita Sam Bata kawo wani alaqar aure a tsakaninsu sbd sanin
Advertisements
yanda auren ya wakana da sanin Koda dad dinta da mum sun rabu har abada NURU sa’ar’yarsace ko kallon Mata baya Mata bare har wani Abu da Mata ke iya yiwa
Miji Dan Haka Bata kawo wani tunaninba bayan na wani abun yafaru ita babbar damuwarta yanzu lokaci na tafiyar Mata.
Dagowa tayi tana kallon agogo kafin ta miqe tsaye ta fita zuwa Palo tana duba wayarta cikeda takaicin yanzu ko waya NURUn batada bare ta kirata.
Da jekadi dazata kitchen da Akira gefenta daukeda wani qaton tray da abubuwa akai saidai rufe da wani farin kyalle me adon zaiba ta kallesu ta kalli tray
din ta maida kallonta kan jekadi tace”
NURU fa???
Kallonta jekadi tayi cikin Dan Bata nata girman tace”
Batanan saidai ko Zaki dawo zuwa anjima ko gobe.
Anjima ko gobe???”tafada cikin mamaki da Dan daga sauti kafin ta Dora da cewa”
Yanzu nake buqatan ganinta uzurine me girma.
Murmushin manya jekadi tayi cikin ranta kafin ta kalli afian tace”
Uzurin gabanta ya zarce kowane uzuri idan Kuma a matse kike da magana da ita ki Fadi sakonki Zan isar mata.
Da kaina nakeson isarda saqon tana Ina?
Kai tsaye jekadi tace”
Ki nemi maleek zai sadaki da ita.
Wucewa jekadi tayi Akira tabi bayanta suka wuce kitchen Dan fara hadin kayan dasuka zo dasu Wanda musamman na NURUn ne.
Kamar wawuya Haka afia ta tsaya agurin harsuka bace Mata
Take taji tashin hankali na neman shigarta sbd Bata fatar abin dazai kawo matsala akan fitar mum dinta hakama takasa yadda Sam da cewa Wai NURU gurin dad
dinta takwana
Shin dama tana zuwane itace Bata saniba kokuwa yaune zuwan na farko?
Sashenta Takoma ta zauna tana sake duba agogo saura AWA daya da mintuna atafi can din
Bata tsaya tunanin komaiba ta daga wayarta ta Nemo numbern dad dinta Kai tsaye ta Danna kiransa.
Kiran duniya tayiwa wayoyinsa Babu me Shiga karshe ta Nemo numbern Mr Omar ta saka Kira tana fatan shi tasamu tasa wayar.
Ringing din dataji wayar tafara yasata sauke ajiyar zuciya tana fatan Yana tareda dad dinta duk da tasan da wuya idan takalli lokacin.
Cikin nutsuwa ya dauka Yana cewa”
Good morning princess.
Morning Mr Omar
Inason magana da dad ga wayoyinsa duka akashe.
Shiru Mr Omar yayi kafin ya Dan gyara murya cikin nutsuwa da basarda zancen yace”
Wayoyinsa suna kashe ne sbd ayyukan da suka Dan Sha kansa kwanakin Nan musamman akan wannan case din kiyi hkr zuwa anjima idan yasamu kansa zai kunna
wayoyin Zaki samesa Inshallah.
Cikin damuwa da Dan daga murya tace”
Maganar mum dinace ta Yaya Zan iya Bari zuwa anjima lokaci na tafiya Ina buqatan mgn dashi Akan NURU ne.
Ajiyar zuciya Mr Omar yasaki Yana sake daidaita murya Kai tsaye yace”
Maganar dayan lawyern miss lailah cikin dare anrigada an Samar muku wani lawyern sbd dayar lawyern da kuka dauka banajin zata samu damar zuwan Dan Haka ki
nemi Imran jalal Kai tsaye Dan nahadashi da lawyern
Ki huta lafiya princess.
Kashe wayar yayi yabarta zaune tana fadawa cikin sabon tunanin abinda yake faruwa data kasa fahimtar komai amma dai babban abin dayafi Mata komai yanzu
maganar mum dintace tunda anbasu lawyer abin yazo Mata da sauqi sauran zancen sayishi daga baya tsakaninta da NURU taji inda tashige.
Ahankali ta Dan motsa tana bude idanuwanta dasukai Mata nauyi sosai sbd rashin bacci da mutuwar da dukkanin jikinta yayi
Akan fuskarsa dake daf da tata idanuwanta suka sauka ta lumshe ido tana budewa ahankali kan bakinsa zuwa dogon hancinsa da idanuwansa dasukafi komai narkar
da kuzarinta
Da Alama baccin yakeyi har lokacin be tashiba ta sake motsawa ahankali daidai fararen idanuwansa da gabaki daya suka sauya zuwa wani sabon yanayi na budewa
ya zubasu akanta
Ta rufe Bata ahankali tana shigar da kanta jikinsa dake manne da nata
Ya motsa ahankali tareda matso da fuskarsa ya hade hancinsa da nata yana sakar Mata numfashinsa me dumi ya bude Baki yace”
Good morning.
Bude idanuwanta tayi tana kallonsa a kasalance da kunyar gaisuwar saidai gabaki daya bakinta ya mutu murus batada qarfin iya magana
Ganin kallon datake masa kwayar idanuwanta na bayyana sirrin zuciyarta akansa ya riqo hannuwanta Yana sarqewa da nasa suka sauke ajiyar zuciya atare
Ya matso da fuskarsa Yana zura kansa cikin wuyanta dake bayyane ba Kaya ajikinta har lokacin sbd bayan tasamu tayi sallar asuba daqyar ya sake rabata da
komai ya qarasa bude hanyarsa dabai Gama budewaba Dan Haka baccin wuya da muguwar kasala ya dauketa sai yanxu data farka
Tanajin dumin lips dinsa cikin wuyanta Yana saukar Mata da wasu irin kisses tareda numfashinsa me dumi da sauti ta lumshe ido tana sake Rena kanta Dan kuwa
ita kadai tasan irin tsananin wuyar datasha tsakanin Daren zuwa safiyar sbd ko qafarta daqyar take iya motsata
Tanajin hannuwansa na yawo tsakanin wuyanta zuwa kirjinta zuwa cikinta da bayanta ta qanqamesa cikin tausayin kanta Dan kuwa Babu inda baya ciwo ajikinta
musamman kirjinta daganan numfashinsu ya sarke Yana daukan sauti musamman nashi dayake fita sosai Yana fada Mata wasu kalmomi cikin yarensu acikin
kunnuwanta wainda suke Bata qwarin jure Masa.
Baccin wahalane yakuma daukanta wannan karon wuyar dataci a bayyane take qarara sbd ko numfashinta ahankali yake fita cikin sanyi datake baccin
Ya kalleta Yana gyara Mata kwanciya ajikinsa tareda shafa fuskarta Yana lumshe ido.
Qarfe goma Sha daya harda mintuna ya farka ya zare jikinsa ahankali daga nata ya gyara Mata rufa Yana shafa lips dinta dasukai kaman sun bushe alamar
tsutsan dasuka kwana suna Sha ya saki guntun numfashi tareda Dan rankwafowa yai kissing dinsu ya juya ya shige toilet.
Bayan fitowarsa shiryawa yayi cikin wasu fararen Armani kaftan dasukai matuqar daukan fatarsa dake glowing fuskarsa a kame yafito Yana kunna wayoyinsa Kai
tsaye ya nufi palonsa na farko daya ganawa da Mr Omar Yana Isa Mr Omar na palon tsaye Yana waya da commissioner daya tabbatar musu da ankama yakoob Wanda
yaqi fadar komai sai cewa komai duk azabar da ake bada.
Kashe wayar Mr Omar yayi ya waiwayo yayiwa MALEEK kallo daya ya Dan sauke kansa cikin ‘yar sakewar murya yace”
Barka da fitowa MALEEK.
Zama yayi Yana amsawa tsananin kwarjininsa da qamshinsa na cika palon da idanuwan Mr Omar din
Ya matso ya zuba Masa lemon tea me zafi ya ajiye gabansa Yana Dan fara Masa wasu bayanin sama sama shikuma Yana sauraronsa batareda yace komaiba.
Shigowar jekadi ne daukeda tray na silver me Dan girma daukeda dafaffiyar Nonon raqumi da wani ruwan madaran na musamman sai Dan breakfast Mara nauyi
Sai wata kyakkyawar qaramar jaka dake hannunta na akayan NURUn dake ciki wainda ayau din akai odarsu aka kawosu
Cikin girmamawa tace”
Allah ya qarawa maleek lafiya da walwala
Barka da tashi.
Da Kai ya amsa Yana daukan wayarsa dake ringing ta sudada ta wuce cikin palonsa na gaba ta ajiye komai akan dining ta koma palondasu maleek din suke shima
ta zuba Masa breakfast kadan yafara ci Mr Omar naci gaba da koro Masa bayanai.
Sai Sha biyu ta farka ta bude idanuwanta dasukai mugun nauyi fuskarta harta Dan kumbura kadan ta dafa ta tashi zaune tana sauke ajiyar zuciya ahankali
tareda rufe ido ta bude tana zuro qafafunta qasa saidai abinda takeji batajin zata iya tashi tsaye.
Shiru tayi agurin zaune tana kokarin miqewa cikin dauriya taji anbude kofar dakin
Bata buqatar dagowa sbd tasan shine yashigo
Jin shiru yasata dagowa daidai isowarsa dab da ita ya rankwafo baice komaiba ya dauketa gaba daya
Tayi qasa da Kai tana rufe idanuwanta yakaita har cikin toilet ya kwantar cikin ruwan dumi ya kalleta tareda shafa gefen fuskarta ya matso da tashi fuskar
yakai bakinsa kunnenta ahankali ya furta”
Sorry.
Zamewa tayi ta kallesa ya sake shafa fuskarta ya juya ya fice yabarta da mamakinsa Bata fito daga mamakinba sai ganin jekadi tayi cikin toilet din da sauri
ta zame cikin ruwan tana shigarda jikinta ruwan tana rufe ido
Kenan shine yake cewa tayi hkr.
Cikin nutsuwa jekadi ta qaraso gurinta tana cewa”
Ni tamkar uwace karki ji komai magani kawai zanbaki wannan sirrinkine da mijinki Nima sbd baisan yazaiyi mikin bane kisamu kyakkyawar kulawa.
Ruwan zafi ta kunna ruwan da NURUn take ciki suka dauki zafi Sosai
Ta bude wata babbar kwalba cikin kayan data shigo dasu ta zuba cikin ruwan take toilet din yadauki wani qamshi NURU kuwa tanajin ruwan na shigarta ta koina
jikinta yafara Dan sakewa Yana Mata wani iri
Jekadi taqara zuba Mata wani abun daban kafin ta dibi ruwan zafin ta zuba cikin wata roba tayi hade hadenta ta ajiye Mata tace”
idan kingama wankan kiyi tsarki da wannan.
Juyawa tayi ta fice sbd tausayin NURUn takeji sbd alamun dasuka nuna tana cikin mawuyacin hali.
Wanka tayi sosai taji dadin jikinta tayi tsarki da ruwan da jekadin ta jiye Mata tun alokacin taji wani irin sauyi Sosai agurin ta Gama tafito ahankali
daureda towel ta nufi gaban mirror dinsa ta shafa mansa tareda spray ta dauki kayan data gani an ajiye Mata Wanda da Alama jekadi takawo ta daga kayan tana
kallo dukkaninsu Babu me nauyi duk na Shan iska ne
Bata wani damuba sbd jirin datake gani ta saka wata doguwar qaramar riga Mara nauyi tayi drying gashinta daqyar ta ‘daure da sabon band fito palon tana
tafiya ahankali jekadi dake tsaye dining tana jiranta tai Mata sannu tareda ja Mata kujera ta zauna tana gabatar Mata da abubuwan dazata fara Sha kafin
komai.
Daqyar ta daure Tasha duka ko abincin Bata iya tsayawa taci ba Takoma daki ta kwanta
Jekadi ta tattare kayan ta fice dasu
tana fita Mr Omar ya sulale yabi bayanta Dan bawa maleek lokacin hutawa
Ya miqe ya koma ciki Yana duba lokacin sallah da yayi.
##MAMUH#*_Mamuhgee 47_*
Bacci takeyi har lokacinda ya Shigo din,ya kalleta tareda sauke boyayyar ajiyar zuciya ya juya ya nufi toilet yayo alwala yazo ya fice batareda ya tada ita
ba Dan baccin Yana Bata nutsuwa da damar yanayinda takeji.
Yana fita bada jimawaba ta farka ahankali ta tashi zaune itama tayo alwala tazo tayi sallar Takoma ta kwanta tanajin zazzabin datake ji na qara shigarta ta
lumshe ido tana sake shigewa bargo idanuwanta a rufe.
Qarfe goma aka Isa da lailah airport acikin wata sirrantacciyar mota
Lokacin afia tafi mintuna ashirin agurin tana jiran isowarsu Dan Haka tana ganinsu ta fiddo doguwar jallabiya da Dan qaramin mayafi da goggles datazowa da
mum din Tata dashi ta nufi motarsu itama tata fuskar Bata bayyanataba yanda za’a gane itace ta bude motarsu ta shiga baya inda mum dinta ke zaune tana
kakkama jikinta tayi wani duhu cikin kwana biyu ga wani irin tsamin dauda da wahala na tashi ajikinta
Cikin tsananin baqin cikin ganinta Haka da kaunar mahaifiyarta me qarfi afia ta rungumeta gabaki daya tana cewa”
Mum.
Zarewa Lailah tayi ta kurawa afia ido idanuwanta na cikowa da hawayen tsananin baqin ciki da dumuwa tarema da tsoron halinda rayuwarta tashiga kokuma ma
Wanda tariga tashiga,
Ahankali ta bude Bakinta dake rawa wani tsamin Baki ya feso yacika motar Amma afia ita Sam batama jisa sbd Babu abinda uwarta zata zama ta gujeta da rawar
murya tana hawaye tace”
Afia,afia my baby,afia my little princess I’m sorry baby ki yafewa mum dinki Amma ki yarda Dani bantaba aikata kisa ba Kuma bazan taba aikatawaba…ban
aikata ba…bazan taba iya aikatawaba…ban aikataba…banyiba…
Riqota afia keyi tana cewa”
Mum mum na yarda Baki aikataba
Mum na yarda
Na yarda mum”.ganin mum din takasa daina fadar Bata aikataba cikin firgici Kamar lokacin abin ke faruwa yasa afia rikicewa tana korarin kwantar Mata da
hankali cikin kulawa hankalinta na neman tashi sbd ganin alamun kaman mum din har lokacin tana cikin shock saidai Kuma….
Imran ne cikin hali na damuwa daya shiga akan lailan tun lokacinda Mr Omar yayi Masa bayanin komai gameda Dan tabuwa da kan lailan yayi sbd Shiga hali na
shock lafiya zata ringa komai Kamar yanda take sai dai idan ta tuno abindaya faru na kisan abin zai dawo Mata zata fara fizgewa tana fadar ba ita tayiba
cikin tsananin tsoro da firgici,
Shi kansa bazaiso afia tasaniba sbd hankalinta zai tashi yakoma kan kula da neman lafiyar mum dinta bazata taba maida hankali kan karatuntaba Kuma Dan Haka
shima ya shirya kula da al’amarin bazai Bari tasaniba yanzu sai tagama kammala karatunta tsaf yanama fatan zuwa lokacin lailan tasamu lafiya Dan Haka shima
ya yanke shawaran komawa Vegas gabaki daya zai zauna da lailah Dan nema Mata lafiya ta dawo daidai ta gyara rayuwarta ta ingantata yanzu kan tunani da
hanyar dazata bullar da ita sbd Lailah tamkar uwa ya dauketa Dan kuwa itace wadda tafi sonsa aduniya bayan iyayensa sbd itanema yake Paris baibi iyayensaba
Koda tabar maleek dasu afia Basu rabu ba shida ita Kuma sbd itane yake tareda maleek Yana aiki a qarqashinsa farko sbd ya kula dasu farhat dasuka shaqu.
Ajiyar zuciya ya sauke ahankali tareda fitowa ya zagayo yashigo bayan ya zauna dayan gefen lailan suka sanyata tsakiyansu ya dago ya kalli afia data fara
shiga firgici cikin kulawa da kwantar Mata da hankali yace”
Tana cikin damuwar abin daya faru sbd case na zargin kisa wani abune da bakowa ne zai iya daukaba
Dole zata shiga wannan halin musamman yanzu data fito Kuma taganta agabanki Dole zataji wannan damuwar da shauqin son sanar dake ba halinta bane.
Hawayene suka gangarowa afia ta rungumeta tana sakin siririn kukan tausayin mum dinta ta dago tana kallonta tace”
Mum Inshallah komai yariga ya wuce bazai sake dawowaba
Ki yarda da wannan wata jarabawace Allah yayi Miki danki gyara Kuma Inshallah nasan kin gyara mum kimin alqawarin bazaki sake zuwa gizah ba sbd bakida
abinda yarage Miki anan sai tarihi.
Kallon afia kawai lailah keyi da idanuwanta dasukai jajir tanajin radadin abubuwa da dama data rasa arayuwarta sanadin son zuciya da son Rai,
Ta rasa MALEEK namijin da bazata taba samun kamarsa ba a fagen komai Dan kuwa ya nuna Mata so da kauna da gata da kulawa da komaima Amma duk ta watsar ta
tsallake a tunaninta zai zauna dakon jiranta,
Ta rasa Farhat dinta yarinyar da Bata morewa komai na soyayya ko kulawar mahaifiyaba da shaquwa Dan kuwa tasan NURU tariga tashiga ran farhat ta yanda
bazata iya rabuwa da itaba ko yiwa wani kallon uwa idan ba NURUn ba,
Ta rasa darajarta,sunanta,mulkinta, dukiya da career dintama gabaki daya
Afia ce kawai abindake gareta yanzu sai Imran datasan har abada shima bazai gujetaba adaidai yanzu datafi buqatan masoyanta atareda ita.
Kama hannun afia tayi ahankali hawayenta suka gangaro kan fuskarta ta kalli afian tareda gyada Mata Kai tace”
Nayi alqawarin Inshallah bazan qara zuwa gizah ba sbd Nima na tabbatarda banida sauran komai anan sai tarihi Wanda bana alkhairi ba Dan kowa zai ringa
tunoni amatsayin wadda tayi kisa labarinta ya Bata.
Sake karyewa zuciyar afia tayi da tausayin mum dinta ta yanda lokaci daya ta rasa komai Kuma tana fatan zatai tawakalli ta karbi hakan.
Kayan data shigo Mata dasu ta Sanya Mata tareda rufe Mata fuska ta Sanya Mata goggles din ta bude motar suka fito dukkaninsu ta sake damke hannun mum din
cikin kulawa da qauna ta tsakanin ‘da da mahaifi tace”
Mum ki kula da kanki Zan ringa kawo Miki ziyara lokaci lokaci kinji¿
Ajiyar zuciya lailah tayi tareda kallon afian akaro na farko rayuwarta tace”
Allah yayiwa rayuwarki albarka afia
Allah yabaki ‘yayan dazasu San darajarki irin Haka da Miki biyayya.
Amin tace ahankali tana dagowa ta kalli Imran tace”
Mum na hannunka.
Guntun murmushi ya saki Yana gyada Kai yace”
tana hannu mekyau.
Murmushin yaqe tayi tana cewa”
Thank you.
Kama hannun lailan dake waiwayen afia tana daga Mata hannu yayi suka wuce itama afian tana musu har suka bace Mata ta saki numfashi a hankali tanajin
nutsuwa ta juya ta fada motar da kanta ta jawo ta tada taja tabar airport din.
Ko data koma sashenta ta nufa sai alokacin tasamu nutsuwar cin abincin data manta rabon dataci
Taci ta koshi ta miqe ta wuce bedroom dinta tayi sallar azahar ta kwanta Dan tasamu baccin dazai qarasa wargaza damuwarta Dan kuwa dukkanin damuwarta ta
yaye takeji.
NURU zazzabi yakamata sosai Wanda ya Hana musu bacci da daddare daga ita har maleek din sbd sosai jikinta yayi zafi tana kwance cikin jikinsa Yana rage Mata
zafin jikin da nasa Dan kuwa yanajin yanda dumin jikin nata ke shigarsa Yana saukan Masa da kasalar sake shigar da ita jikin nasa itakuma tana lafe tana
sauke numfashi ahankali cikin sanyi.
Kallonta yayi cikin Dan qaramin hasken dakin Ya shafa bayanta ahankali Yana sake ce mata”
_Azinalehu_ (Sorry) cikin kunnenta da wata sirrantacciyar muryarsa da tsakanin jiya zuwa yau tasanta.
Ahaka yayita lallabata suka samu bayan sallar asuba tasamu bacci ya dauketa me nauyi sai alokacin yasamu nutsuwar kansa ya gyara Mata kwanciya tareda fitowa
Palo sanyeda milk jallabiya me taushi ya zauna Yana daukan wayoyinsa ya kunna sbd yau yakeson Kai qarshen matsalar komai tunda sungama hada dukkanin
shedodinsu dasuka tabbatar musu da zarginsu Akan Wanda suke zargi
Yana buqatan komawa Paris kodan rashin lafiyan Nan daya sameta.
Mr Omar yakira Kai tsaye yace”
A bayyanarda duka shedu akan yakoob a cikin kotu yau.
Cikin girmamawa Mr Omar yace”
Maleek haryanxu Yana maganar son ganin ‘dansa Kuma idan aka bayyanar a kotu cewan ‘dansa ne ya mutu zai iya bayyana komai a gaban kotu Wanda zai taba gizah
da Kuma Anneti sbd al’amarin zaizo Mata da tashin hankali tunda Bata taba tsammanin hakan ba daga Wanda take aure
Kana ganin yakamata mu fitar da zancen duka a kotu?
Yan media zasu yada abin fiyeda komai ta yanda zai Yi Muni.
Shiru maleek yayi na wasu mintuna kafin yace”
Yanada damar yasan mutuwar dansa saidai baida damar fadar komai bayan abubuwan daya aikata da wannan za’a yanke Masa hukunci basai anbari yafada komaiba
bayan wannan…..
Shiru yayi Yana kokarin daure abin dayake ji a zuciyarsa dasuka bayyana a idanuwansa yaci gaba da cewa”
Neges Kuma sbd daraja ta auren Anneti zanji da matsalarsa ta cikin gida batareda duniya tasan abin daya aikataba sauran haqqin Rai dake kansa Kuma
tsakaninsa da ubangijinsane.
Cikin yanayi na sanyi shima Mr Omar yace”
Allah ya kyauta ya sake tsare imaninmu
Allah Kuma yaqara maka tsarkin zuciya.
Ba Haka suka so ba duk su dukan Amma Kuma wani lokacin kanayin abinda shine zaman lafiyar kowa da Hana fitina.
Lokacinda aka tafi da yakoob har mortuary aka jawo gawa tareda yaye Masa yaga gawar ‘dansa amed datai fari tas sbd ajiya da sanyi.
Sarewa qafafuwansa sukai sbd firgicin ba zata daya fizgesa lokaci daya da wannan mugun ganin dayayi
Cikin tashin hankali ya zube gaban gawar Yana ihun Kiran sunan”
Amed Amed Inidēti ibakíhìni¿
Yaushe wannan mummunan Abu yasameka batareda nasaniba?
Amed katafi kabarni Banda kowa sai kai.
Dagowa yayi cikin ficewa hayyaci da tashin hankali ya kalli Mr Omar Yana cewa”
Meyasa???meyasa??
Ta yaya?
Yaushe kuka kashesa?
Meya muku?
A Daren ranar daya tafi aikin neges yamun saqon cewa Yana lafiya tafiyan gaggawa yayi…..ko shekaran jiya yamun sakon Yana lafiya Dana kira..yaushe kuka
kashesa…..
Kukan tashin hankalin masifa yakeyi sbd sanin tsaf wannan umarnin maleek ne ya sake gangaro da hawayen baqin ciki jikinsa na daukan rawar Shiga tashin
hankalin rashin tsammani na wannan afkuwar dabai taba kawowa aransaba ya rasa dansa kwalli kwal Wanda duk suke wannan fafutukar rayuwar dansu tsira su Tara
abin kansu su gudu wani gurin su Gina rayuwa.
GIPHY App Key not set. Please check settings