UBAYD MALEEK 48

Advertisement

 

Mamuhgee 48_*

Kallon yakoob Mr Omar yayi Yana gyara tsayuwa yace”

Allah ya yafe Masa kurakurensa tareda Kai mahaifinsa daka dorasa akan irin wannan rayuwar da batada hanyar bullewa ko a duniya ko agurin ubanginka,

Son Rai da bin zuciya qarshensa baida Dadi yakoob Amma tunda kune kuka zabi hakan hakan shine daidanku,

Babban kuskuren daka aikata yakoob shine sako ‘danka da baida kwarewa acikin wannan harkar dakai ka Jima da dadewa acikinta Dan kuwa gashi kuskurensa 

yakaisa ga Haka kaima yakaika ga hakan.

Advertisements

Allurar meriz ce ta kashesa kaman yanda kukai amfani da ita Dan kashe tsohon NEGES mahaifin maleek Kuma kukaso kashesa da ita,

Kun aikashi kashe padima saidai kun manta cewan a sashen maleek ne take 

Kuma a sashen Babu wani lungu da Babu camera a maqale Wanda idonku da zuciyarku sun rufe da aikata hakan kuka saka Amed disconnecting dinsu Wanda ko karatun 

addini bayadashi bare na zamani Dan Haka ta Yaya kuke tunanin zainiya ciresu.

Ranarda muka samu labarin zuwan lailah gizah muka tabbatarda akwai dalilin zuwan nata Wanda anyi kirantane Dan ayi amfani da ita hakan yasa muka sauya 

tunani ta hanyar Dena shayarda padima meriz sbd ga hanyar sauki tazo Mana,

Tunda neges yayi magana da lailah tafara bibiyar jekadi Wanda jekadi tagane hakan ta sanar Mana daga lokacin mukasan meyake faruwa har lokacinda muka 

Advertisements

tabbatarda amed na bibiyar lailah itama bamui wani motsiba muka barku Dan ku aiwatar da naku Shirin dazai bamu tamu damar.

Kaf gizah Babu Wanda yasan da padima na cikin masarautar shiyasa muka kyaleku Dan munsan Dole bazaku barta ba duk da batasan ainihin waye yasakata aikin 

daya sakata ba ahaka rashin nasararku yakaiku aika amed kashe padima wadda taji sauki da kanta zata iya Kare komai kuma a Daren ranar jekadi ta miqa Mata 

allurar meriz a hannunta ta sanarda ita duk Wanda ya shigo kawo Mata farmaki ta tabbatarda ta kwaci kanta da allurar Wanda hakan zai fidda ita daga wannan 

rigimar gabaki daya har abada.

Padima na son ranta fiyeda masoyinta amed Wanda shima yakeson dukiya fiyeda rayuwarta Dan Haka a Daren ranar abindaya faru shine bayan yaja lailah da dubara 

zuwa gurin Dan kisan ya hau kanta mun gani Kuma mun sanarda jekadi komai kafin isowarsu gurin Dan Haka jekadi tasake nanatawa padima tana sane ya fito 

lailah ta doketa saidai bamuyi tsammanin amed yaqara doke jekadin ba yasamu ya qarasa dakin ya bige lailah ta hanyar kwada Mata katako akai Wanda ganinsa 

yasa padima shiga tashin hankali saidai Bata Bari tsoronta yabarta barin amed yasamu sa’ar kashetaba tayi amfani da matsayinta na mace ta nuna Masa kanta 

amatsayin su Raya darensu na qarshe kwadayin Zina yajasa ga rasa ransa batareda yasamu abinda yake kwadayinba.

Babu Wanda yasan padima na kasar tayaya Yan jaridar suka San waye aka kashe bayan Babu Wanda yaga gawar da idanuwansa wannan shine babban kuskurenku na biyu 

daya kawo karshenki batareda ansha wuyar hakan ba,

Padima ta kashe amed sbd Kare Kai itama Allah yabata nata sakamakon ta hanyar rasa cikakken hankalinta kamar lailah Da Haka kowa zai girbi nasa aikin.

Allah ya tsare Mana imaninmu yabamu kariya daga mutane kamarku Wanda suka Tara arziki ta hanyar kisa da miyagun ayyuka gashinan dukiyar Zaki tafi ku barta 

abawa mutane suna Kuma tsine muku.

Juyawa yayi ya fice yabar yakoob din tsaye cikin rashin sanin makamar tunanin Yi sbd dukkanin gangar jikinsa da jininsa sun tsaya cak Babu abinda yake motsi 

ajikinsa bayan zuciyarsa dake bugawa ahaka aka jasa Yana tangadi aka fice dashi

Take ‘yan jarida aka sakar musu labarin suka fara yadawa cewan 

Yakoob amintaccen bawan neges ne ya kashe tsohon NEGES na gizah 

Take aka bayyanarda shedu dasuka hada da garin meriz dake ciki sarkar da padima ta taba boyewa da aka samu a sashensa gurin bincike.

Hankalin jama’ar gizah ya tashi tareda girgiza matuqa sbd kishin kishin fara zargin NEGES da akai Wanda yasa akai gaggawar yankewa yakoob hukuncin kisa ta 

hanyar cire kansa sbd kada ragewa fitinar tsayi 

Amma duk da hakan ba a daina bayyanarda zargin NEGES ba Wanda yasashi kasa fitowa sbd tsananin kunyar kansa da baqin ciki me nauyi daya lullubesa sbd Kai 

tsaye ko an boye laifinsa saidai yasa jama’a yin shiru Amma wannan zargin da laifinma gabaki daya bazai rufu ba musamman da kaleeb da maleek sukai shiru 

sunki saka Baki a maganar sai hakan yasake bawa jama’a kwarin gwiwa aka fara kishin kishin sauke neges jama’a da jinin sarautar gizah da ‘yan delah gabaki 

daya kowa yafito ya nuna sha’awarsa ta sauyin neges sbd kobabu saka hannunsa zamtowar bawansane ya aikata hakan to tabbas hakan ya shafesa Dan Haka gabaki 

daya kusan ya rasa girmansa da mutuncinsa a idon jama’a

Musamman Anneti da yakejin Kamar bazai iya hada idanuwa da itaba sbd girman kunyar abindaya aikata Wanda yasan itama yagama fahimtar komai saidai kawai tayi 

shiru sbd wani abin basai kafadaba Allah ya kyauta kawai yafi maka saukin fada

Da wannan ya kebe kansa da kansa a sashe dabam bayan ya fitar da wasiqar sauka mulki da kansa ya aika har delah gurin kaleeb Wanda har lokacin yaqi cewa 

komai bare maleek daya fara Shirin barin qasar bayan ya bayarda sunan Mohan YONAS (autan kaleeb) amatsayin Wanda za’a nada sabon NEGES na riqon kwarya kafin 

lokacinda zai karba Dan haryanzu Yana buqatan wani Dan lokaci kadan kafin yadawo gabaki daya ya karba gizah din.

******

Zazzabinta yayi sauki sosai ba laifi Dan kuwa Daren tasamu tayi bacci sosai sbd wani magani da jekadi ta kawo Mata Dan Haka gari na wayewa tun karfe shida 

da mintuna ta fito cikin doguwar jallabiya data rufeta koina ta nufi sashenta tana Isa ta wuce bedroom dinta tashige tana sauke numfashi ahankali kafin ta 

dago ta kalli farhat dake kwance kan gadonta tana bacci cikin nutsuwa 

Ta qarasa gadon ta zauna tana kallonta tasaki murmushi ahankali tace”

Sweetie nayi missing naki da surutunki sosai.

Miqewa tayi ta zare rigar jikinta ta jefa cikin wardrobe ta nufi toilet ta shige.

Kodata fito komawa gadon tayi ta haye ta kwanta gefen farhat ta gyara musu rufa Takoma bacci sbd baigama isartaba.

Qarfe tara ta farka lokacin har farhat ta Jima da farkawa ta bude idanuwanta ahankali tana kallon farhat dake Kiran sunanta cikin murna da farin ciki tace”

Aunt NURU yaushe kika dawo?

Tashi zaune tayi tana gyara gashinta da murmushi akan fuskarta tace”

Sweetie na barci nadawo

Ya kike?

Fadawa jikinta tayi ta rungumeta tana cewa”

Next time idan zakije tare Dani Zaki Zan biki kinji Aunt NURU.

Wani irin Murmushi ne ya saukowa NURUn ta kalli hancin farhat din zuwa bakinta dasuke Zak Zak Dana dadynta saita sake sakin murmushi tana saukowa gadon 

tace”

Kinyi brush?

Biyota tayi tana cewa”

Eh nayi nace next time zakije Dani??

Tsayawa tayi tareda juyowa ta kalli farhat din ta kamo fuskarta taja hancinta ahankali tana murmushi tace”

Wannan hancin Ina sonsa sosai kaman yanda nake son sweetie dan haka kidainama tambayan idan zanje wani guri ba dakeba ok¿.

Cikin murna tace”

I love you too lewa.

Knocking kofa akai ahankali tareda bude kofar aka shigo 

NURU ta dago tana waiwayowa kofar sukai ido biyu da afia dake kallonta da dukkanin hankalinta tana nazarin NURUn da akace batada lafiya saidai bataga alamar 

ciwo atareda NURUn ba jikinta ba inda ya nuna alamar akwai ciwo tareda ita ta karaso ahankali cikin ‘yar kulawa da alamar tambayarta tace”

Jekadi tace bakida lafiya da fatan dai ba wani serious ciwo bane ko??

Murmushi NURU tasake tana matsowa gaban afia din tace”

Naji sauki kawai gajiya ce da rashin isashen bacci Amma yanzu lafiyana kalau.

Kallon cikin idanuwanta afia tayi tana kokarin karanto idan da akwai ciwon atareda NURUn tace”

Mezaisa ki kasa samun isashen bacci bayan kina samin hutu sosai bakida aikin komai a gabanki….

Aiki dad dinku yabani Wanda duk ya kawo hakan yanzu dai inason Baki hakuri akan rashin samun damar zuwana gurin mum dinki I am really really sorry for that 

Kuma Ina fatan komai yatafi yanda ake fata?

Ajiyar zuciya afia ta sauke tana qarasawa bakin gadon dakin ta zauna tana cewa”

Komai yatafi yanda akeso mum Dina tana Las Vegas tareda Imran Wanda yakoma can yanzu da zama da aiki sbd su manta rayuwarsu ta baya su fara sabuwar rayuwa 

Mara damuwa da Danasani.

Numfashi NURU ta sauke cikin ahankali tareda ajiyar zuciya tana kallon Afia da taushin murya tace”

Ina musu fatan kyakkyawar rayuwa me Dadi da amfani.

Thank you afia tace tana kallon fuskar NURUn data sauya Mata gabaki daya.

Wanka NURU tashiga ta fito cikin nutsuwa ta shirya cikin doguwar riga golden me sequence ajiki suka zauna dukkaninsu su ukun anan sashenta sukai breakfast 

tare suna gamawa suka dawo Palo suka zauna NURU na Shirin zuwa gurin Anneti afia ta kalleta tareda dawowa gefenta ta zauna cikin nutsuwa ta kalleta tana 

tattaro abinda zata fada Mata tace”

Shin kinsan case din kisan da mum take ciki padima ce wadda ake cewa ta kashe……

Wani irin kallo NURUn juyo tanayiwa afia din da dukkanin fararen idanuwanta.

Wata ajiyar zuciyar afia takuma saki tana dafa hannun NURUn tace”

Padima ce wadda dukkanin labarai da duniya ta shedarda an kashe….

Hawayen dasuka ciko fararen idanuwanta dasuka koma ja Nan take suka gangaro kan fuskarta ta sake kallon afian da kyau tana kasa gasgata zancen sbd bazai 

yiyuba babban zance irin wannan a boye Mata

‘yar uwarta jininta aka kashe ace Bata saniba sai yanzu bayan wadda tayi kisan har ansaketa ta tafi Kuma maleek na sane da hakan,wane hali iyayenta suke 

ciki gameda wannan mummunan al’amarin na rasa padima itakuma Bata tareda dasu a lokaci irin wannan miqewa tayi zuciyarta da idanuwanta na rufewa da wani 

irin yanayi Mara Dadi da damuwa

Afia tayi saurin riqota tana Miqewa tsaye cikin nutsuwa da kulawa tace”

NURU ki kwantar da hankalinki anyi bincike angano komai da cewan ba padima bace kawai yan media ne suka juya zancen sbd basusan ainihin wayeba aka kashe 

angano komai yanxu tareda gano Wanda sukeda hannu a komai har kisan tsohon NEGES wato mahaifin dad dinmu komai ya wuce yanzu Inshallah…

Girgiza Kai tafarayi ahankali hawayenta na tsananta gudu cikin wani irin yanayi na toshewar Kai tace”

Bani wayanki inason Kiran abal Dina Ina buqatan Jin halinda suke ciki,

Ina buqatan magana da padima 

Mezaisa padima ta zauna Nan har irin wannan Abu yasameta,

Ni gabaki daya ban fahimta ba,abal nakeson magana dashi yanzun Nan……

Cikin sanyi da son kwantar Mata da hankali afia ta miqa Mata wayarta tana cewa”

Dan Allah ki nutsu kada ki dagawa su abal din naki hankali idan har Basu saniba, ki tambayeshi ta yanda bazaki daga hankalinsu ba muji idan padiman na 

taredasu.

Bata tsaya sauraren sauran bayanin afia ba ta hau saka numbobin abal dinta ta Danna Masa Kira zuciyarta na  rawa.

Kamar zata tsinke saigashi ya daga cikin nutsuwa da kwanciyar hankali yayi sallamar data Sanya NURU saurin riqe numfashinta tana seta muryarta tace”

Abal.

Jin muryar NURU yasa abal din tashi zaune daga kishin giden dayake Yana kallo a tv cikeda kewarta da kaunar ‘yarsa yace”

NURU kece?

Kina lafiya?

Ya kike?

Yaya maleek da yaransa?

Shiru tayi zuciyarta na sake bugawa ahankali muryarta na rawa tace”

Abal Ina padima?

Leave your vote

-2 Points
Upvote Downvote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like