MATAR UBA 22

Advertisement

 πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦

     *MATAR UBA*

πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦

Daga Alkalamin ✍️

      

       *Milly*

                   Fadilah Yakub

Advertisements

                 *(MILHAAT)*

*🌍MANAZARTA WRITERS ASSOCIATIONπŸ“šπŸ–ŠοΈ*

                   *M. W. A*

 *Bismillahir Rahmanir Rahim*

 “`NOT EDITED“`

 “`CHAPTER 22“` 

πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦

Advertisements

Karfe Tara chip suka Isa asibitin a office d’inta ta ajiye ta kana ta fita don duba patient d’inta masu matsala irin na asiyah, bayan ta gama ta koma office, zaman ta ke da wuya ta ga Kiran hashim, cikin sauri tayi picking Bai jira tace komai ba yace “Kina Ina? Na shigo asibitin ku?”

Tace “Ina office d’ina gani nan zuwa”

” No ki fad’a min inda kike kawaii am coming” 

Nan ta Masa kwatance,ya katse wayar.

πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦

……….. Asiyah Tace “Aunty Ina Jin fitsari”

Tace amsa da to, da taimakon ta ta shiga ban d’aki kana ta fito tana jiran ta, knocking d’in kofan da akayi ne ya dawo da ita daga tunanin da ta Lula, da sauri ta bud’e kofar ganin muradin ranta sai da taji kirjin ta ya buga, Shima haka Hashim d’in yaji gani yayi a cikin shekara uku duk ta sauya ta Kara kyau kamar ba ita, gyaran murya yayi yace “Ina yarinyar take?”

“Tana ban d’aki, baza ka shigo bane?”

“Da na so ganin ta ne amma Shikenan kizo Muje mota na Baki cheque ko?”

Ta amsa da “toh, barina da duba ta”

” Okay idan Kun Gama Ina mota a parking space” ta amsa da “okay”

Yana kaina ya juya ya fita.

Asiyah shiru tayi tana sauraron muryar kamar tasan muryan nan, ta Kira sunan Badiyya Amma dake kofan a rufe yake shiysa Bata jiba, knocking kofar tayi Tace “Asiyah kin gama?”

Ta amsa da “eh”

Shigowa tayi ta fito da ita daga ban d’akin ta zaunar da ita Tace “d’an jirani Ina zuwa ko?”

Ta amsa da “Toh”

Bayan ta fito bud’e motar tayi ta zauna a gaba da sallama ta shiga ta zauna ya amsa chan chaki,kamshin tiraren jikinta ne ya buga hancin sa har Saida ya koma ya d’an kwanta, sun dad’e a Haka kana ya d’ago ya kalle ta yace “Million biyu zai ishe ku?” 

Chan ciki ta amsa da “Eh zai Isa”

Check ya zaro a aljihun motarsa ya rubata check d’in three million ya Mika Mata,mamaki ne ta kamata Tace “Hash 3 mil? yayi yawa fa”

“Wannan ba komai bane Badiyya, anything for you”

‘dago wa tayi da sauri tace “Anything for me?”

Kallon ta yayi Ido ciki Ido yace “Yes anything for you”

Marairaice fuska tayi Tace ” But why? Why Hashim baza ka yafe min laifin da nayi maka ba” idon ta fal da kwalla.

Kad’a Kai yayi idon sa Nan da Nan idon sa yayi jaa yace “Taya kike so na manta abinda idanuna suka gane min ba? Bazan tab’a manta da wannan ba”

” Hashim na fad’a maka wallahi ba abinda kake tunani bane ba”

” Look Badiyya, kin bukaci kud’i a wurina na baki, please get out of my car”

” Hash….”

” Get out…..” A tsawace,har Saida ta tsorota cikin sauri ta bud’e kofar ta fita,tana share kwallan da suka zubo Mata a ido.

Kai tsaye office d’inta ta nufa ta tarar da Asiya ta had’a Kai da gwiwa sai aikin kuka take, cikin sauri ta karasa inda take, Tace “Asiyah… Asiya me ya same ki?”

Cikin shesshekar kuka Tace “Aunty Ina tausayawa Rayuwata ne bani da kowa banda komai,mutum d’ayane ya rage min a rayuwa ta na tabbata Yana nema na, Ina son ganin sa Amma bana so ya ganni a haka”

” Wanene wannan ki fad’a min sunan shi ko zan Nemo Miki shi?”

” Hashim  Ahmad…..”

Kwankwasa kofar da akayine ya same ta kasa karasa maganar ta, Badiyya ce tace “Yes come in…”

Ganin Wanda ya shigo ya sa tayi saurin mikewa, gyaran murya yayi yace “Kin manta wayar kin motata” Yana maganar had’e da Mika Mata,har ya juya zai fita Tace “Hash ganan yarinyar da za’ayi wa surgery” 

A hankali ya juya ganin wacce idonsa ke nuna Masa yasa yayi suman tsaye, Badiyya Tace “Sunan ta Asiyah”

Ganin baya Jin ma maganar da take Tace “Hashim”

A razane Asiyah ta tashi ta tsaya, Badiyya banda kallon su ba abinda take Baki na rawa Asiyah Tace “Hashim? Aunty wani Hashim kike magana akai?” Ta karasa maganar tana kuka, Badiyya ta rike ta ta Maida ita ta zauna Tace “Asiyah lafiyan ki kuwa?”

Asiyah kasa Bata amsa tayi sai kuka, Badiyya kallon Hashim tayi cikin Rawar murya Tace “Kasanta Ne?”

Amma Bai Bata amsa ba,tashi tayi tana d’an tab’a shi a kafad’a ya d’an zabura Tace “Hashim ya ina magana kamin shiru?”

Kad’ai Kai yayi yace “bakomai” shi duk a tunanin sa Asiyah gizo take masa, kukan da yaji ne ya sa ya Maida hankali sa gunta sa hannu yayi a fuskar sa ya goge idonsa ya Kara kallon inda Asiyah take cikin murya Mai sanyi ya Kira sunan ta “Asiyah?”

Tana Jin haka ta fashe da kukan farin ciki, da saurin ya nufi inda take ta durkusa a gaban ta yace “Asiyah kece?”

Fashe wa tayi da kuka tace “Ya Hashim” riko hannayen ta yayi ya had’a da nasa ya sumbaci hannunta, ya sumbaci hannunta yafi a  irga Kuma cikin sauri yake hakan yace “Asiyah Ina Kika shiga,wa ya Miki haka?”

Nan ta bud’e sabon babin kuka,kuka take sosai kuka Mai tab’a ran Mai sauraro.

Rungumarta yayi tsam a jikin sa, Yana d’an bubbuga bayan ta kamar wata ‘yar baby, sun dad’e a Haka Bata daina kukan ba Shima Kuma bai sake ta ba,nitsuwane ya Zo Mata a lokaci guda da ta tuna cewa tana tare da Rabin ranta, Kara shigewa tayi jikinsa tana shesshekar kuka Saida ya tabbata hankali ta ha kwanta kana ya sake ta,ya riko hannayen ta yace “Asiyah Ina sauraron ki Dan Allah ki fad’a min me ya same ki? Wa ya Miki haka?”

Cikin kuka ta kwashe dukkanin abinda ya Faru ta fad’a Masa, huci yayi, ya Fara rarrashin ta Yana Mata nasiha a yayin da a zuciyar sa yana Shirin d’aukan fansa ne.

Badiyya ta karasa inda suke Tace “Dan Allah ki fad’a min wai me ke faruwane anan? Hashim dama kasan Asiyah ne?”

Kallonta kawaii yayi baice Mata komai ba, Asiyah da farin ciki ya Riga ya mamaye ta Tace “Aunty shine Hashim da muke maganar sa d’azo”

A zabure ta mike Tace ” Hashim? Kina nufin shine masoyin naki?”

” Eh Aunty…….. Akwai matsala ne?”

Cikin rawar murya Tace ” A….A’a ba bakomai bakomai,kwai dai shine Wanda ya biya Miki kud’in surgery da za a Miki”

Murmushi tayi Tace “Allah sarki nagode sosai Ya Hashim Allah ya saka” 

Ya amsa da ” ameen” babu Wanda ya sake Cewa komai Knocking d’in kofar da akayi ne yasa Badiyya tayi saurin share hawayen dake fuskar ta Tace “Come in”

Baba Mai gadi ne a gaba,Abban Yesmin na biye dashi”

Mamakine ya rufe Badiyya cikin Rawar murya Tace “Baba….baba Kaine? Asiyah ga baba”

Asiyah cikin sauri ta cire hannunta a cikin na Hashim ta Fara lalube tana ambatan sunan sa.

Cikin sauri ya karasa inda take yace “Na’am Asiyah gani Nan” Yana maganar ya riko hannunta fashe wa tayi da kuka Tace ” Baba Ina ka shiga? Ka barni ni kad’ai?”

Kad’a Kai yayi yace  “gani  na dawo ban barki ba”

“To Amma mun dad’e muna neman ka da Aunty Badiyya Amma bamu ganka ba”

” Bani da lafiya ne Asiya Amma yanzu Alhamdulillah naji sauki sosai”

Tace ” To Allah yasa kaffarane duk suka amsa da  “ameen” 

“Baba kaje gun Aunty Rukayya kuwa?”

Huci yayi yace “Eh naje” 

“Alhamdulillah ka same ta kuwa”

“A’a ban same ta ba”

Asiyah Nan da Nan fara’ar dake fuskar ta ya gushe Murmushi Baba yayi ya d’aura da fad’in “Amma da naje ta bawa Mai gadin ta sako a Baki,a fad’in sa Tace tasan Zaki Zo neman ta”

Murmushi tayi Tace ” wani sako ta bani?”

Iska Mai zafi ya hura kana yace ” Kiyi hakuri Asiya,motace ta buge Ni a wannar ranar Kuma wasikar na hannu na a wannan lokacin tun daga lokacin ban San inda nake ba sai shekaran jiya na farfad’o”

Murmushin gefen baki tayi Tace “Bakomai baba tunda kana da lafiya ai shi yafi muhimmanci a yanzu”

Abban Yesmin a Karo na farko ya yi magana yace “wasikar da kake magana akai d’azun Nan na d’auko shi a mota da niyar zan baka,Amma bara na Kira Matata ta kawo muga ko shi d’in ne” Yana maganar ya zaro waya ya kirata, tana picking yace  ‘dan kawo min envope “d’in Nan Mana a office d’in Dr Badiyya”

Ba ‘bata lokaci ta Karo dake bai da wani nisa, da Sallama ta shiga ta Mika masa,ganin Asiyah ta Kama Baki ta ambaci sunanta “Asiyah kece?”

Ta amsa da “eh Amma pley Wace Ce?”

Murmushin gefen baki tayi Tace “Haba Asiya har kin manta Ni?”

Dr Badiyya ce Tace “Ai ta makance Bata gani?”

“Eh na sani,baba Mai gadi ya fad’a min, na d’auka zata d’auki muryatane”

Murmushi Asiya tayi Tace ” Aunty Nana? Ko ba Maman Yesmin bace?”

Ita ma Murmushi tayi Tace “Eh nice nice”

” Hmm ai bazan tab’a manta dake ba Aunty Nana bazan tab’a manta ki da mummy ba”

Nana harkasa ta durkusa Tace “nasan bakya gani na,yanzu haka a gwiwowina na ke,Asiyah na cutar dake, na biyewa son zuciya ta,Amma wallahi yanzu na tuba ba Nanar da Kika sani bace yanzu haka na manta ranar da na sa Baraka a cikin idona Dan Allah na roke ki,ki yafe min,Kuma a shirye nake na taimaka Miki wajen ganin kin d’au fansar abinda Baraka ta Miki”

” Na yafe miki Aunty Nana har cikin zuciya ta dama chan ban kullace ki da komai ba”

” To nagode Asiya” tashi tayi ta mikawa baba Mai gadi wasikan yana gani yace “Tabbas shine wasikar ne,don ga sunan ta a jikin” Yana nunawa Abban Yesmin shi duk dad’ewar wasikar a gun sa bai San akwai sunna akai ba, mikawa Asiya wasikar yayi yace “Asiyah ga wasikar Nan”

Murmushi tayi tace “Baba da wani idon zan karanta? Kawaii ka karanta min naji”

“To bande ke da abinki Asiyah ai Ni ban iya karatu ba, sunan kin ma da nace Wanda ya bani wasikar ne yace min ga Nan sunan ki a rubuce” duk sukayi dariya sai ya ce ” To ai gaskiya ne,yanzu Ke gashi ki karanta Mana” Yana Miki wa Dr Badiyya, hannu buya tasa ta karb’a cikin girmamawa.

Karanta sakon ta Fara yi kamar haka.

 “`”Assalamu alaiki Asiya,da fatan kina lafiya, Kiyi hakuri Asiya da irin halin da Kika tsinci Kanki, ko kad’an bana Jin dad’in abinda ke faruwa daku,tun bayan mutuwar Anisa da Mahaifin ku Baraka take yin abinda ta ga dama har gidana tazo ta ci mutunci na da na Miji abin bai min dad’i ba Sam,har tayi ikrarin zata kashe ni idan na kuskura na Tako inda kuke shine dalilin da yasa na daina zuwa in da kike.

        Baraka Bata da imani Bata tsoron Allah, Asiyah ina ji Ina gani ta sawa Yar uwata Maryam (Mahaifiyar Asiyah) guba a cikin abincin ta Amma na kasa fad’awa kowa a wannan lokacin ma ta yi min barazanar zata kashe ku sannan Nima ta kashe ni idan na kuskura na fad’a wa kowa maganar Nan, wannan shine dalilin da yasa ban fad’awa kowa ba.

       A duk lokacin da sakon Nan ya iso gare ki,ga Nan number ta ki kirani Dan Allah ina Nan Ina zaman jiran kirin ki,sannan akwai Flash drive da na ajiye Miki acikin envelope d’in Video ne na lokacin da Baraka tasawa mahaifiyar ki guba sannan akwai recording na lokacin da take min bazarana” 

      Taki a kullum Rukayya

“` 

Asiyah fashewa tayi da kuka a yayin da, Badiyya tasa hannu ta Ciro flash drive d’in, Hashim ne yace “Alhamdulillah Allah ya kawo karshen azzuluamar Nan, yanzun Nan zan shigar da kararta kotu ba sai anjima ba” ya zaro wayar sa da niyar yin Kira.

Abban Yesmin yace ” Dakata Dakata bawan Allah, wannan ba abin gaggawa bane Baraka shu’uma ce Dole mu bita a hankali,ba abun mamaki bane ta kashe mu duka ko Kuma ta haukatar da mu” Maida kallon sa yayi ga Badiyya yace” Bani flash d’in Nan” ba musu ta mika Masa ya d’aura da fad’in “wannan zan Kai was aboki na babban lawyer ne Barrister Nabeel Yunusa nasan Kun San shi tunda shi ba ‘boyayye bane a garin gombe”

Hashim yace “Ni a gani na tunda an samu wannan opportunity d’in Kar muyi Wasa dashi gara a kamata kawaii a Mata hukuncin da ya dace”

Baba yace “Hashim Ina ga maganar officer na Kan hanya kasan Shima jami’i ne mubar maganar Nan a hannun sa”

Abban Yesmin yace “Hakane malam Hashim yanzu mu Maida hankali wurin ganin yarinyar Nan ta samu lafiya”

” Hakane yallab’ai goben Nan zan kaita England da kaina,yanzun ma abinda zai Hana baza mu tafi yau ba sabida Bata da passport Amma yanzun Nan zan had’a komai” Yana Kai Nan ya sa Kai ya fice.

Badiyya kanta ne ya d’aure ganin yanda Hashim ya rikice “Yana son d’aukar fansar abinda akayi mata,duk yanda akayi soyyayaar yarinyar Nan ta Kai kololuwa a zuciyar sa,bazan tab’a Bari yarinyar Nan ta kwace min masoyi ba”

Shiru tayi tana tunanin abubuwan da suka Faru shekaru biyu da suka wuce. 

 *SHIN MENE NE A TSAKANIN HASHIM DA BADIYYA?* 

Harvard University United State of America, Yana d’aya d’aga cikin manyan University a United States, anam courses da dama both art and science.

Zaune take ta a Kan stairs, jikinta sanye take da atamfa kalar curfew brown an Masa design da da milk color anyi Masa d’inkin girma, crystal stones aka zuba a gaban rigar daga sama har kasa,kanta kuwa d’aurin Aisha buhari tayi Ana iya ganin bakin gashin ta a waje, Rolling tayi da karamar gyalle milk haka ma takalmin da ke kafarfa, hannun ta rike yake da littafi da alama karatu take ganin yanda ta Maida dukkanin hankalin ta akai.

Da sallama ya Kara sa inda take ya zauna a gefen ta,a hankali ta d’ago kanta ta kalle shi Murmushi tayi Wanda ya bayyana dimple d’in dake fuskar ta,rufe littafin tayi tana kallon sa ba tare da ta ce masa komai ba yace “Angel dama anan kike tun d’azu nake ta neman ki?”

“Eh wallahi Ina d’an duba practical d’in da makayine d’azu”

” Shine akace ki manta da mijin ki? Wace irin matace haka da ba ta damu da mijin ta ba?”

Had’a hannun tayi with guda alamun bada hakuri Tace ” Tuba nake rankashidad’e”

‘daga kafad’a yayi Yana kwaikwayon muryar ta “A’a nikam ban hakura” dariya ta shiga yi sosai tana fad’in ” Na fad’a maka ka daina kwakwayona sai ka Zama kamar mace dama kamannin ka na Mata ne”

“laa Ni d’in kike cewa na Miji?”

Ya Kai hannu zai rankwashe ta,ta watsar da littafan dake hannun ta, ta gudu tashi yayi ya bi bayan ta sai guje guje suke acikin makaranta,Yan cikin makarantar inda Sabo sun Saba ganin wannan masoyan Wato Hashim da Badiyya soyyayar su ta Kai so sun Zama abin kwatance hakan yasa wasu ke Kiran su da Romeo and Juliet.

Karatun su suke sosai, soyyayar su Bata Hana su karatu ba duk da already an musu baiko, Hashim na karanta Business yayin da ita Kuma take karantar _ophthalmology_ (Likitan Ido). Shekarun su biyar Kenan suna soyayya basu samun sab’a ni idan kuwa kaga sunyi fad’a to kishin Hashim ne sila akwai wani Course mate d’in badiyya Mai suna Amma Khan, ba indiye ne Yana matukar kaunar Badiyya,Amma ganin yanda take son Hashim yasa ya hakura da ita idan kaga ya Mata magana to magana ce da ta shafi karatu, uwa uba Yana bala’in tsoron Hashim bazai tab’a manta dukan da Hashim ya Masa ba har sai da ya kwana a sume a school clinic.

Yau suke celebration na gama makaranta, ko wani department da inda suke nasu bayan sun gama a ka had’a general party dukkanin graduating students na ko wani department, Badiyya tun jiya take rokon Hashim Akan suje Amma yaki.

“Hash please Muje Mana Kaga jiya akayi departmental celebration Amma baka je ba,yau general me Dan e Muje Kar kace baza Kaje ba”

Rai a d’an b’ace yace “I have told you bazanje bazanje ba Ana Dole ne idan kina son zuwa kije Mana ban Hana ki ba,Amma Ni bazan je ba”

Rai a ‘bace ta fice daga cafeteria d’in.

Hashim ko a jikin sa,komawa yayi d’akinsa ya kwanta abinsa.

Badiyya kuwa zuwa tayi ta shirya yau kananann Kaya tasa,bakar pencils skirt da farar T-shirt an ruba Opthalmologist a gabar rigar bayan ta Kuma Badiyya Hash aka sa, rawa ake Ana ci ana Sha, Badiyya na matukar son rawa hakan yasa ba a bar ta a baya ba tana tsakiyar dance floor,Ammar na ganin ta ya taso da niyar yi Mata magana Bata ankare ba ta buge shi a ido,cikin sauri ta juya don ganin wanda ta buge “Ammar oh Am so sorry please”ganin  Yana murza idon Tace “hold on let me see” ganin idon yayi jaa ta Fara hure Masa idon, a dai dai Nan Hashim ya shigo daga nesa ya hango bayan ta, ransa ne yayi mugun ‘baci gadan gadan ya nufo su fince ke ta yayi ya hau dukan Ammar dakyar aka shiga tsakanin su, wurin ne yayi shiru a fusace Badiyya Tace “hashim what do you think you’re doing? What’s the meaning of this?”

“What’s wrong with me? What’s wrong me? You’re here kissing this thing and you’re here asking me what am I doing?  tell me what you’re doing with him? Why are you quit?” A tsawace yake maganar

Cikin rashin fahimta Tace ” What? Are you kidding me?”

πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦

PLEASE SHARE AND COMMENTS

MILHAAT CE

YAR TERAWA

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like

MATAR UBA 35

Advertisement  πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦      *MATAR UBA* πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦ Daga Alkalamin ✍️               *Milly*  …

MATAR UBA 30

Advertisement πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦      *MATAR UBA* πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦ Daga Alkalamin ✍️               *Milly*  …

MATAR UBA 21

Advertisement πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦      *MATAR UBA* πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦ Daga Alkalamin ✍️               *Milly*  …

MATAR UBA 10

Advertisement   πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦           *MATAR UBA*  πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦        _(A True Life Story_…

MATAR UBA 33

Advertisement   πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦      *MATAR UBA* πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦ Daga Alkalamin ✍️               *Milly*…

MATAR UBA 13

Advertisement  πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦           *MATAR UBA* 🌎 *MANAZARTA WRITERS ASSOCATION* πŸ“šπŸ–ŠοΈ  _(‘Kungiya d’aya tamkar da…