Advertisement
π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦
*MATAR UBA*
π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦
Daga Alkalamin βοΈ
*Milly*
Fadilah Yakub
Advertisements
*(MILHAAT)*
*πMANAZARTA WRITERS ASSOCIATIONπποΈ*
*M. W. A*
*Bismillahir Rahmanir Rahim*
“`NOT EDITED
CHAPTER 26“`
“Aunty you’re like an angel to me, I just want to see you”
Murmushi kawaii tayi,yayin da Hashim yake mamakin irin shakuwar dake tsakanin Asiyah da Diyya, Ammar fita yayi awa d’aya na cika ya shigo da nurses guda biyu a biye dashi.
Advertisements
Ba Asiyah kad’ai ba hatta Diyya da Hashim Saida sukaji kirjin su ya soma bugawa.
π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦
………. “Are you ready?”
Ammar ke wa Asiya wannan tambayar Murmushi tayi ta d’aga Masa Kai alamun eh, Shima Murmushin yayi ya kalli Hashim yace “She likes laughing”
Murmushi kawaii ya Masa.
A hankali ya Fara cire bandage d’in Diyya da Hashim duk hankalin su na kanta , sai da ya rage bandage d’aya Ammar ya ummurci Diyya da ta tsaya a gaban Asiyah hakan kuwa akayi, bayan ya cire idanun ta a rufe yace “Open your eyes slowly and carefully”
A hankali take Bud’e idanun ta tana ganin wuri bashi bashi ba idanunta na wassakewa ta sauke su akan wata kyakkyawar halitta fara, ba doguwar bace sannan ba gajera bace Murmushi tayi Mata ita ma Maida Mata “Aunty Diyya kece?”
“Eh nice” idanun ta ya cika faal da hawaye mikewa Asiya tayi ta rungume ta kyam a jikin ta cikin kuka take Mata godiya.
Gyaran murya Hashim yayi “Wato ni ba a damu dani ba ko? kin ma manta Dani?” Yadda yadda maganar ne ya sanya ta dariya Yana magana Kamar d’an shekara biyar harda langwab’ar da Kai, Kare Masa kallo tayi ganin yanda ya canza ya Kara haske ya Kara kyau.
Karasowa yayai gaf da ita Diyya ganin zai iya ture ta, ta matsa ta basu wuri, kallon kallo sukeyiwa juna, wani irin wutar son junnan su ne ke tafarfasa a cikin zukatan su, hannu ta ya riko yace “Nayi matukar murna da idanun ki suka dawo Baki ji yanda nake ji ba ba yau”
“Hmm nago….. ” Saurin rufe Mata Baki yayi da lausassan hannun sa ya gyad’a Mata Kai had’e da fad’in “Ban bukatar kalmar godiya daga gare ki, Nayi wannan ne a matsayin ki na wacce na fiso, wannan kad’an ne, sannan kofa a Bud’e take idan kina bukatar wani abu just tell me”
“Ko wacce irin bukatar da Zama maka dashi zaka min?”
“Eh insha Allah just name it”
Diyya har ta Isa kofa zata fita Asiyah Tace “Aunty Dan Allah kizo”
Ba musu ta karasa inda suke, kallon sa tayi Tace “Inaso ka had’a ni da Aunty Diyya ma’ana ka aure mu”
Zaro Ido yayi yace “Amma wasa kike ko?”
“Dagaske nake”
Iska ya hura Mai zafi yace “Na amince” ya Maida kallon sa ga Diyya “Da fatan zaki amince da hakan My Diyya?”
Saurin ‘dago kanta tayi tana kallon sa cike da mamaki sakin hannun Asiyah ya nufi inda ta tsaya Murmushi yayi yace “Kina mamaki ne?”
Kai kawaii ta d’aga Masa Murmushi yayi yace “Maganar aure ne ya baki mamaki ko Kuma Kiran ki da nayi da My Diyya?”
Kai a kasa murya chan ciki Tace “Duka biyu”
“To ki daina mamaki kinji”
Kai ta d’aga Masa idanun ta hawayene ,d’aga habarta yayi yace “Kuka? Please ki daina” ai kuwa kamar ce mata yayi ta kara, ganin kukan yayi yawa ya rungume ta, a tare suka sauke wani ajiyar zuciya.
Asiyah sai Murmushi take (Ni ko nace Asiya Murmushi Kuma ko Yar kishin Nan babu) Diyya da Hashim sun Lula wata duniyar,dama gogan naku Yana so Yana kaiwa kasuwane a kunne ya rad’a Mata “I miss you Bae”
“I miss you too” Kara kankame ta yayi a jikin sa kamar zai Maida ta cikin cikin sa.
Gyaran muryar da ammar yayi ne suka tuna Basu kad’ai bane yayi saurin sakinta kamar wani Mara gaskiya.
Dariya Ammar yayi yace “Congratulations Asiyah”
“Thank you Dr”
Hashim yace “Is there anything left?”
“No I have already discharge her”
“Good in that case we are going back to Nija tommorow”
” What so soon?”
“Yeah what will we wait for?”
“you’re right, but Amma gonna miss you guys”
“Same here bro, you’ll attend our wedding right? Cos you’ll be our guest of honor”
“Insha Allah, ill be there.”
A motar sa ya Maida su har masukin su, sannan yace zai dawo da yamma su fita cin dinner, Hakan kuwa akayi karfe takwas ya dawo ya d’auke su suka fita,tare da matar sa suka zo, Sunci sun Sha har sai karfe goma saura ya dawo da su, sannan ya musu alkwarin Kai su airport.
Baccin su suka Sha Mai dad’i Amma Banda Asiyah tana ta tunanin abinda zata tarar indan ta koma gida sai kusan karfe uku amba dare ya barci ya sace ta,karfe biyar saura ya kwankwasa musu kofa, tashi sukayi sukayi sallah sannan suka shirya, karfe biyar da Rabi Amma ya kirasu cewar Yana waje, already sun so jakar su kawaii suka d’auka suka fita, Hashim na ganin jakar hannayen su yasa hannu ya karb’a.
Hira suke Sha duk su ukun har suka karasa inda motar Ammar yake,ban kwana suka Masa,shi kuwa yace Yana Nan Yana zaman jiran IV.
Suna shiga jirgin ko wannen su ya duba sit d’insa wannan karon shi ya zauna a tsakiyar su, kallon shi sukayi sai ya d’aga musu gira kallon juna Asiyah da Diyya sukayi suka tuntsire da dariya, Zama sukayi Sabida Ana sanarwa jirgin zai tashi,Hira suke sama Asiyah ce ta Fara bacci, ba a d’au lokaci Mai tsawo ba Diyya ma bacci ya d’auke ta sai zuba surutu yake Jin ba mai bashi amsa ya Dubai yaga duk sunyi bacci,ganin yanayin baccin nasu zai iya sanya musu ciwon wuya ya rungume Diyya da hannu d’aya kana ya kwantar da Asiyah a cinyar sa, daga bisani Shima baccin ya d’auke sa.
Diyya ce ta Fara farkawa, Murmushi kawaii tayi ta sake komawa baccin ta, basu farka ba har sai da jirgin su ya sauka Nija, a hankali Suma fara Bud’e idanun su. Idanun shi ya sauke Akan Diyya dake ta kallon sa gira ya d’aga mata Yana Mata kallon lafiya, Murmushi tayi Masa ya sa hannu ya shafa fuskar ta, Asiyah kuwa Mika ta shiga yi “Wayyo bayana”
Dariya sukayi yace “Allah ya bani hakuri Ni da kuka danne Ni”
Asiya Tace “hakkin Kane kula da mu,ko ba haka bane aunty?”
” Hakane Kanwata”
“Au had’e min Kai zakuyi lallai sai nayi da gaske”
Dariya kawaii sukayi,suna fita suka Tarar da Faysal na jiran su,Gidan su Diyya suka wuce yace “Zan zo Hira anjima” sukayi wucewar su.
Umma tayi matukar farin cikin ganin su musamman da yanzu Asiyah tana gani “Haba Badiyya tunda Kuka tafi ba Kira shiru haka gashi Ni ko na kira ba samun ki nake ba”
“Yi hakuri Ummu wallahi tunda mukaje muke ta fama da zuwa asibiti ban zauna ba shiyasa”
“Tunda an Samu abunda aka je nema ai Shikenan”
“Yanzu Asiyah ya ake ciki da maganar Baraka take da suna ko?”
“Eh umma Baraka,ban San yanda ake ciki ba,Amma insha Allah gobe zanje Ni gidan maman Yesmin naji yanda ake ciki”
“Har sai mun jira gobe? Ai ki tashi mu tafi kawaii yanzu,baza ki gane yanda na damu da aka Mata ba”
“Aunty daga dawowar mu sai mu fita ga gajiya ko hutawa ba muyi ba,ki Bari sai gobe kawai”
“Gaskiya Asiyah take fad’a ku bari sai gobe kuje d’in” umma ke wannan maganar.
“To” kawai Diyya tace don taso su je a yau d’in nan.
Mummy tayi mutukar farin ciki duk da Bata San dalilin sa na tafiyar ba, kwata kwata kwanaki biyar yayi baya gidan Amma ji take kamar ya fi wata,bayan ya huta ne ta zaunar da ita duk abubuwan dake tafiya, Kama daga kan Maganar Shirin auren da yayi na karya da Safiyya, har izuwa ‘batan da Asiyah tayi da samun lafiyarta da Kuma Shirin da suke na kama Baraka, har izuwa alkawarin auren da yayi wa Asiyah da Diyya
“Oh Hashim duk wannan abubuwan dake faruwa Amma baka sanar Dani ba sai yanzu? Dama da Badiyya kuka yi tafiyar?”
“Eh da ita mukayi,sabida itace take kula da ita, Am sorry Mom naga Sam Baki kaunar yarinyar ne shiysa”
“A’a Hashim ba Haka bane kawaii dai naga yanda duk baka damu da kanka bane sai ita shiysa Kuma kasan bani da wani buri da ya wuce ka koma Kan aikin Mahaifin ka”
” Insha Allah Mom satin Nan zan Fara zuwa aiki”
” Aiko da na ji dad’i, yarinyar Nan Badiyya Yar Albarka ce duk irin Soyayyar da take maka kishi bai hanata kula da Asiyah ba”
“Hmmm mom Diyyata Kenan”
” Dan Allah rufe min baki wai Diyyata kamanta irin rashin mutuncin da kq shuka Mata ne, yarinyar Nan taxo gidan Nan don Kai yafi a irga”
“To Mom ai komai ya wuce yanzu ko,mun dai daita”
“Masha Allah,nafi kowa farin ciki,na tabbata da Mahaifin ka na raye ba karamin dad’in had’in Nan zaiyi ba,duk da ka bajire Masa a baya”
“Oh nikam na shiga uku”
“Tara ka shiga ba uku” dariya kawaii yake mikewa yayi yace “Ni zan fita”
“Ina Kuma zaka je,da Daren nan?”
“Hira zanje”
“Lallai Son Amma baka duba time ba ko?”
Agogon hannun sa ya duba “Inna lillahi wa Inna ilaihirraji’un”
“ya da salati Haka?”
“Mom karfe Sha biyu saura fa, gaskiya banji dad’i ba”
“Oh da Kai tunda ka cika Mara kunya gidan su Diyya zaka je da way zakayi Hira a cikin su?”
“Duk su biyun”
Mom yarfa hannu ta shigayi tana salati “A ina aka tab’a yin Haka Hira da Yan Mata biyu?”
“Ni Zan Fara mom”
Hab’ar ta ta rike Baki a Bud’e take kallon sa, dariya kawaii yayi yace “Ni zan kwanta sai da safe” ya haura d’akin sa Yana dariya.
“Oh Ni yasu,wani abu sai wannan zamani ko a littafin ban tab’a ji anyi haka ba,Amma da sauki tunda da amincewar su” tana Kai Nan itama ta haura d’akin ta.
Asiyah da Diyya sunyi ta zuba Ido don ganin Hashim Amma Shiru kaje ji, Diyya ta Kira layin sa yafi sau biyar bai d’aga ba, a Lokacin Yana parlor da mummy ya bar wayar a d’akin sa.
Yana ganin missed call d’in yabi baya ya Kira har sau uku ba a d’aga ba sai ya Kuma Kira har ya kusa yankewa a ka ‘daga cikin muryar bacci Tace “Hello!!!”
Ajiyar zuciya yayi yace “You can’t imagine how much I missed this voice”
Murmushi kawai tayi ya d’aura da fad’in “Am so sorry Diyya for not giving you the chance to explain yourself to me”
“Is okay kasan komai mukaddarine daga Allah, idan da a Lokacin Nan mukayi aure na tabbata baza ka had’u da Asiyah ba, Asiyah kaddarar kace ko ince kaddarar muce,gaba ki d’aya”
“Hakane, ke d’in ta dabance Queen, Nagode sosai da kike kula da kanwarki”
“Ban bukatar godiyar ka nayi ne don Allah sannan Asiyah yarinya ce Mai hankali manya,tun farkon Haduwar mu da ita naji ta shiga Raina,da Kuma nasan itace farin cikin ka sai na kud’iri a niyar kyautata Mata Sabida Ina son abunda kake so King”
“Kin San yanda nayi missing sunar Nan da ga bakin ki kuwa?”
“hmm a a sai ka fad’a”
” Ke dai Bari don bazai kwatantu ba”
” To Shikenan rankashidad’e na bari”
” kanwar taki tayi bacci ne?”
“Eh tayi bacci”
” Okay kema ya kamata ki Samu ki kwanta ko?”
“Har ka gaji da Jin murya ta?” Cikin muryar Shagwab’a take maganar, wani yaaarrr yaji a jikin sa Nan da Nan yaji wani irin shauqi ya kamashi.
“am sorry queen, nasan kin gaji sosai Kuma gobe nake so mu Fara processing yanda za a kama Baraka”
” Kamar kasan abinda ke cikin zuciya ta,gobe insha Allah Zamuje gidan Abban Yesmin”
“Allah ya kaimu to ku d’auke Ni driver Mana nazo Ni na Kai ki”
“Hahaha to Shikenan, an gama”
“idan Kun shirya goben sai Ku kirani”
“Toh Insha Allah”
“ki shafa min Kan karamar Queen”
Hannu tasa akan Asiyah tace “Na shafa maka”
” Toh saura na My Queen” tasa hannu a kanta ta shafa Tace “Done”
“Thanks Love,good night,ki kula min da Kanki kinji?”
“insha Allah, please do same”
“I’ll bye”
A tare suka katse wayar.
Murmushi kawai take tana Jin wani irin dad’i, Asiyah ma Murmushi take yi don tun Fara wayar su har suka gama tana Jin su,Amma tayi kamar bata ji ba. (oh ni Milhaat ina ganin ikon Allah ,ni kam bazan iya irin wannan Soyayyar ba).
WASHE GARI
……….. “Safiya Ni sa’ar kice ina magana kina Maida min magana?”
“Mummy me na Miki Kuma ,Wai ke meyasa kike son takurawa rayuwatane ke Baki da aikin yi sai masifa haba”
Tashi tayi ta wanka mata maruka biyu masu zafi Tace “Idan Kika sake ina magana kinayii sai na datse miki harshe Kuma na kashe ki”
“Mtswww akwai wani abunda Kika kware Akan sane Banda kisa to sai me idan kin kashe ni?”
Ganin tayi kanta tasa gudu tana biye da ita har Saida ta shige d’akin ta ta kulle kofar ta ciki.
A tsawace Tace “Safiya….. Safiya open this door”
“Baza a Bud’e d’in ba”
“safiya ni kike cewa Haka? Innalillahi wa Inna ilaihirraji’un,wai me ke Shirin faruwane,asirin Nan na kokarin karyewa dani kike zancen yarinya idan kin San wata baki San wata ba”
Ta shige d’akin ta.
Wani Kullin magani ta dauka a cikin Waldrope d’in ta, fridge ta Bud’e ta d’auko yoghurt ta juye Rabin maganin a ciki,ta girgiza da kyau ta Maida ta ajiye, Jakarta ta d’auko ta shige mota tayi ficewar ta.
Safiyya na Jin karar motar ta gane ta fita ne tsaki ta jaaa, ta fito fridge ta nufa ta d’auki wannan yoghurt din da Baraka tasa Abu a ciki, tana Bud’ewa ta kafa Kai ta shanye tass ko bismillah batayi ba,wani irin bacci ne taji ya kamata,har ta Fara haurawa Kan stairs taji baza ta iya ba ta dawo kan sofa ta kwanta.
π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦
Please comment and Share
Milhat ce
Yar Terawa
GIPHY App Key not set. Please check settings