Advertisement
π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦
*MATAR UBA*
π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦
_(A True Life Story_ )
*Short story*
“`Story and written by FADEELAH YAKUB (MILHAAT)“`
Follow me on Wattpad @milhaat
Join my group on Telegram
https://t.me/joinchat/IhnmqM7EjtZ02IV0
Advertisements
π *MANAZARTA WRITERS ASSOCATION* πποΈ
_(‘Kungiya d’aya tamkar da dubu)_ _____________________________
*MATAR UBA* Labarine Wanda ya faru dagaske banyi shi don cin zarafin kowa ba face don nayi wa Yan Uwa Mata nasiha, idan yazo dai dai to akasi aka samu, Allah ubangiji Ina rokon ka ka bani ikon rubuta abinda zai amfani Yan Uwa musulmai, kamar yanda na Fara lafiya Ina rokon ka kasa na gama lafiya AMEEN.
Dedicated to *MUHAMMAD KARIM MK* much Love.
CHAPTER 3
π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦
………… “Maza ku daina kallo na ku wuce ku cire uniform d’in Nan kusa wani Kaya, kun tsaya Kuna kallo na da ido kamar na mayu.”
Ba musu suka haura sama Tace “Minti biyu na Baku ku kifo Kar ku wuce Nan, Wai mummy zamuje makaranta da wani kud’i za a biya muku? Mtssws” bayan sun fito ne ta d’aura musu talla.
Advertisements
Sun dad’e a yawon tallaan sai wajen karfe uku suka dawo gida.
Karb’an kud’in tayi Tace “Masha Allah Ashe Kuna da amfani” Nan ta Shiga irga kud’in sai taga naira hamsin da bakin sa ya d’an gutsire ta kalli kud’in dakyau Tace “Toh wannan Kuma waya cinye?”
Basu ce mata komai ba sai kallon junan su kawaii suke.
Tace “banda rashin hankali ma Kuna ganin kud’i ba kyau ku karb’a, ku Shiga Ciki Ku huta,idan Allah ya kaimu gobe tunda Kun sayar da wannan duka zamu sayo wasu”
Kallon Juna suka yi cikin Rawar murya Asiyah Tace “Mummy yunwa muke ji”
“Yunwa kuke ji?”
A tare suka amsa da “Eh yunwa muke ji”
Gyara Zama tayi Tace “Kuna nufin yunwa yunwa na cin abinci?”
Suka amsa da Eh.
Langwabe Kai tayi Tace “Allah sarki kun ga abin da nake fad’a muku Kenan Nima tun jiya banci komai ba”
Anisah Tace “mummy na kasa fahimtar abinda ke faruwa mun talauce ne ko me?”
Yar karamar dariya tayi Tace “Eh mun talauce Amma Alhamdulillah tunda muna raye, to yanzu ya zamuyi Kenan tunda Kuna Jin yunwa?”
Kallon ta kawaii suke suna rarraba idanu, Murmushi tayi ta sa hannu ta d’auko naira hamsin d’in Nan da ya yage tace “me wannan zai saya Mana muci tunda Allah ya had’a Ni da monkeys?”
Anisah Tace “Mummy Dan Allah ki Kira Daddy muyi magana dashi”
Tashi tayi Tace “Kina nufin na Kira mijina? Baku girma bane ta yanda zaku Rika fita Kuna neman kud’in da zakuci abinci? Wato na Kira shi?” tana maganar tana nuna kanta.
“Eh please call our Daddy he promise us that we will never lack anything”
A tsawace Tace “would you shut up your dirty mouth,I should call him kuce Masa me? Idan Kika kuskura Kika sake fad’a min magana makamanciyar wannan Anisah sai na karya ki”
Anisah Tace “But mummy…”
Katse ta tayi a tsawace tace “Get out from here useless children” tana maganar had’e da ture robobin da suka dawo dashi.
“Ku d’auki robobin Nan ku fice min daga gani”
A tsorace suka bar pallon.
A garden na gidan suka zauna Asiyah Tace “Anisah Dan Allah na roke ki wata alfarma? ya kamata ki daina tan kamata idan tana magana”
“Meyasa kikace haka?”
“Sabida zata kashe mu wataran idan Kika cigaba da Mata Haka”
Murmushi tayi Tace “To Asiyah me banbanci mu da matattu, ba abinci, ba zuwa makaranta muke ba, ba kayan sawa kin San duk ta Kona Mana su,ba Uwa ba uba, har yaran da suke gidan marayu sun fimu da komai, to me Kuma ya rage? A raye muke dai Amma ta kashe mu”
“Na San da hakan Anisah Amma ya kamata ki d’auki magana ta Kinga nice gaba dake ko?”
“To shikenan zanyi yanda kikace”
Asiyah tashi tayi tace “Yauwa ko kefa Tashi muje muyi sallah muyi Shirin zuwa islamiyya”
“Gaskiya ni bazanje ba jiri ma nake ji Ina sallah zanyi bacci”
“To shikenan Nima baccin zanyi kawai.”
Ganin ta nayi ta fito daga kitchen hannun ta rike yake da plate, fried rice ne aciki da cinyoyin kaji manya manya, d’ayan hannun Kuma kwalin Hollandia ne, Kai tsaye dinning table ta nufa tana ajiye plate d’in wayan ta ya Fara ringing tana picking ta amsa da “Hello qawata”
Bayan sun gaisa Tace “Ke dai Bari kawai qawata nayi duk yanda zanyi Amma shiru kike ji na rasa meyasa ban haihu ba sai faman bauta nake wa yan iskan yaran Nan.”
Tana d’an yi shiru da alama tana Mata magana Wanda Ni na kasa ji sai ji nayi Tace “Ai wallahi Ina haihuwa Zan Kori monkeys d’in Nan a gida na, Kema kin sanni ai wallahi ba ruwana da inda zasu je suma mutu Mana”
“Okay to shikenan ki gaida min ‘yarki” kashe wayar tayi ta cigaba da cin abincin ta, suna shigowa suka tarar da ita ta na yagar nama ganin suna kallon ta banka musu wata muguwar harara had’e da fad’in “baza ku bar Nan ba?”
Da saurin gaske suka bar gun, a Haka suka kwana da yunwa sai Ruwan da sukayi ta Sha.
Yau ma tun safe suka fita don sayar da lemo da pure wata.
Wata bakar motar na gani kirar Benz tazo ta gifta su.
Cikin motar wata yarinya sa’ar su Asiyah tana kallon su Asiyah cike da mamaki Tace “Mom ya akayi na ga su Asiyah suna tallah?”
Murmushi tayi ta Maida hankalin ta sosai Kan tukin da take, sai Tace “Toh mene ne aciki don sunyi tallah akan su aka Fara ne?”
“Toh Amma Meyasa Ni bana yi”
A tsawace Tace “yimin Shiru Allah ya raba ki da tallah, Suma d’in kaddara ce kuma Kar naji kin sake fad’in Haka, kuma kar ki fad’awa kowa kina jina ko?”
“Toh bazan fad’a ba”
Shafa kanta tayi Tace “Yauwa Yesmiin ‘yar Albarka,Bari nayi sauri nayi dropping d’inki a makaranta Kar ki makara ko?”
Tace “To mommy”
Sai yamma liss suka gama sayar da komai da komai babu abinda ya rage, a galabaice suke tafiya Asiyah Tace “Anisah har yanzu zazzab’in Bai sake ki ba?”
Cikin kasala Tace “Eh jiri nake ji, ji nake kamar zan fad’i”
“Sannu bari na rike ki, mun ma kusa Isa gidan” rike ta tayi suna tafiya Kan ta Ankara Anisah ta zube a kasa, ihu Asiyah ta Fara yi tana kuka tana neman taimako dake a GRA suke unguwan Shiru ba kowa ta dad’e a Haka Kan ta hango wasu Samari su biyu da gudu suka nufota, d’aya daga cikin su yace “Me ya same ta Haka?” Cikin kuka tace “Suma tayi” chaak ya d’aga ta yace “Ina ne gidan ku?”
Tace “Yana chan ba nisa daga Nan” da gudu suka kaita gida Amma sukayi rashin Sa’a Baraka ta fita yawon gantalin ta da ta Saba, Asiyah ta musu godiya har parlor suka aje ta Kan suka tafi.
Ruwa ta d’ebo a roba tana sawa tana Kama Mata jiki don jikin ta yayi zafi sosai suna cikin hakan ne ta dawo tana ganin su tace “Ita Kuma wannan me ya same ta?”
“Sannu da dawo wa mummy ba ta da lafiya ne ya kamata akaita asibiti?”
Hard’e hannayen ta tayi ta ce “Asibiti? Kuma ana bukatar kud’i?”
Tace “Eh ai ya Zama Dole?”
Harararta tayi Tace “Dole? Cancer take dashi ne?”
Murya kasa kasa tace “A’a.”
“Good to bani da kud’in kaita asibiti”
“Toh mummy Dan Allah ki ara min wayar ki na Kira Daddy”
A tsawace Tace “bazan bayar ba, harda wani ya Zama Dole to ta mutu Mana ina Ruwana Kun ma ci Sa’a ban d’auke ku naje na sayar daku ba, useless children”
Tana maganar tana haurawa sama.
Cikin kuka Anisah Tace “So take na mutu”
Asiyah Tace “Shhhh Karki ce Haka baza ki mutu ba Allah ya baki lafiya tashi Muje ki kwanta a d’aki.”
Dakyar ta d’aga ta dake ratar shekarunsu kad’an ne Asiyah shekarunta Tara Anisah Kuma Bakwai sannan Anisah ta d’an fi Asiyah kauri, upstairs d’in su na da tsawo da kyar suka haura sabida gidan babba ne kud’i ya zauna anan.
Bayan ta Kwantar da ita ta fito ta zauna a corridor tana kuka ta had’a Kai da gwiwa tana fad’in “Mummy Ina kike Dan Allah ki dawo,mummy Kinga irin abinda ake Mana kin kasance mutumiyar kirki, mace ta gari Kuma Uwa ta gari kece irin uwar da ko wani d’a zaiyi fatan samu,ko Ina ana yabon kyawawan halin ki, Allah ya jikan ki yasa kin huta.”
Sai da tayi kuka Mai isarta Kan ta tashi ta koma d’aki,yau ma da yunwa suka kwana sannan Anisah zazzab’in yaki sake ta.
*WASHE GARI*
Qawartace ta kawo mata ziyara da alama fita zasuyi.
Qawarta ta naji Tace “Ina yaran ki suke?”
Kallon ta tayi cike da b’acin Rai tace “Kya jiki da wani zance yanzu Yan iskan yaran Nan ne zakice ‘ya ‘yana, na haifi mayu ne?”
Suna cikin magana ne Asiyah ta sauko daga upstairs cikin sauri, Qawar bakaraka Tace “Ganan d’ayar mayyar”
Wani irin kallo Asiyah ta Mata tace “Ni ba mayya bace”
A tsawace Baraka Tace “Ke don uwarki sa’ar kice maza ki bata hakuri”
Ba don taso ba Tace “Kiyi hakuri”
Tab’e baki tayi ta amsa da “Ya wuce”
Durkusa wa tayi a gaban ta Tace “Mummy Dan Allah ki taimaki Anisah ba tada lafiya jiya bamuyi bacci ba, mukai ta asibiti ko Kuma ki bani kud’i na kaita”
” bani da kud’i”
Qawar Baraka Tace “Kaai mummy Tace Miki Kuma naji kin amsa”
Harararta tayi Tace “Kinji na amsa ne bana son rashin mutunci, kin gama ne mu tafi?”
“Eh na gama” tashi sukayi da niyar fita.
Asiyah rike kafarta tayi Tace “mummy please”
Hankad’e ta tayi ta fita.
Suna tafiya Asiyah ta fara dube dube duk ta hargitse parlor Bata ga abinda take nema ba da sauri ta shige d’akin Baraka karkashin gado da ta Fara Dubawa ta koma ta d’aga pillow, ta koma Kan wall drop ta koma gaban mirror tsaki tayi ganin bata samu ba sai ta hango wata Yar karamar purse da sauri ta d’auka ta b’ude,Murmushi Naga tayi ta zaro duba d’aya da gudu ta fita ba ta zarce ko Ina ba sai chemist Mai chemist ganin yanda ta shigo da gudu ya sa ya tsorota Yana kallon bayan ta yace “Yarinya wa ya biyo ki?”
Sai sauke Numfashi take tace “Dan Allah malam magani zaka bani”
“Maganin me kike so?”
Tace “Zazzab’i yake damun Kanwata”
“Zazzab’i da Kuma me?”
“Ciwon Kai sannan bata da Karfi tana yawan Jin jiri”
Yace “Okay” karb’an kud’in yayi ya bata maganin ya fad’a Mata yanda zata Sha tana karb’a ta fice da gudu.
Da sauri ta haura sama tana Shiga d’akin ta ga Anisah na kwance cikin sanyin murya Tace “Anisah tashi Kisha magani”
Shiru bata amsa ba ta Kuma cewa “Anisah bacci kike ne?”
Bata amsa Mata ba.
Da sauri ta nufi inda take kwance tayi kokarin d’aga ta ta kasa dakyar ta samu ta d’ago kanta idon Anisah a kakkafe tayi saurin sake ta tana Kiran sunan ta “Anisah!!! Anisah” da sauri ta rike hannun ta tace “Anisah ki tashi, ki tashi Dan Allah” hannu tasa ta rufe idanun ta sannan ta gyara Mata kwanciyar ta, tana ambatan “Innalillahi wa Inna ilaihirraji’un”
π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦π¦
PLEASE SHARE AND COMMENTS
*MILHAAT CE YAR TERAWA*
GIPHY App Key not set. Please check settings