MATAR UBA 8

Advertisement

πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦

          *MATAR UBA* 

πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦

       _(A True Life Story_ )

            *Short story* 

 “`Story and written by FADEELAH YAKUB (MILHAAT)“` 

Follow me on Wattpad @milhaat

Join my group on Telegram

https://t.me/joinchat/IhnmqM7EjtZ02IV0

Advertisements

🌎 *MANAZARTA WRITERS ASSOCATION* πŸ“šπŸ–ŠοΈ

 _(‘Kungiya d’aya tamkar da dubu)_ _____________________________

*MATAR UBA*  Labarine Wanda ya faru dagaske banyi shi don cin zarafin kowa ba face don nayi wa Yan Uwa Mata nasiha, idan yazo dai dai to akasi aka samu, Allah ubangiji Ina rokon ka ka bani ikon rubuta abinda zai amfani Yan Uwa musulmai, kamar yanda na Fara lafiya Ina rokon ka kasa na gama lafiya AMEEN.

Dedicated to *MUHAMMAD KARIM MK*  much Love.

πŸ’¦πŸ’¦ *MATAR UBA* πŸ’¦πŸ’¦

     _(A True Life Story)_

           *Short story*

 “`Story and written by FADEELAH YAKUB (MILHAAT)“`

Follow me on Wattpad @Milhaat

Join my group on Telegram https://t.me/joinchat/IhnmqM7EjtZ02IV0

Advertisements

🌎 *MANAZARTA WRITERS ASSOCATION*πŸ“šπŸ–ŠοΈ

 _’kungiya d’aya tamkar da dubu_

https://www.facebook.com/107980080946102?referer=whatsa

_____________________________

 *MATAR UBA* Labarine Wanda ya faru dagaske banyi shi don cin zarafin kowa ba face don nayiwa Yan Uwa Mata nasiha,Allah ya bani ikon gama shi lafiya kamar yanda na Fara lafiya ameen.

Dedicated to *MUHAMMAD KARIM MK* Much Love.

 *BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*

Not Edited

CHAPTER 8

πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦

……….. Asiyah jiki ba Karfi ta tashi ta mike ta haura bedroom d’inta, a galabaice ta Shiga bathroom ta Watsa ruwa had’i da alwala, tana fitowa ta shafa Mai sannan ta  d’auko doguwar Riga da doguwar Hijab d’in da take sallah ta zurma sannan ta tada sallah bayan ta idar ta jero addu’o’in neman tsari da ga sharrin Baraka da Kuma nema mata gafara  da Kuma neman gafara wa Daddy, mummyn ta da Kuma Anisah.

Jiki a Sanyaye take saukowa daga step din ganin ba kowa a parlor hakan yasa ta kusa kanta a cikin kitchen, dube dube ta Shiga yi ko zata Samu sauran Abinci Amma babu duk an wanke kwanukan, girgiza Kai tayi Had’i da rike kwankwason ta a fili Tace “Ya Allah ka kawo min karshen wannan abun” Nan ta hangi wata bakar leda akan dakalin kitchen d’in tayi saurin bud’ewa ganin garin kwaki ne a Ciki hakan yasa ta San shine abincin ta gashi d’an kad’an ne tasan bazai koshar da ita ba murmushin gefen baki kawaii tayi ta nufi washing hand basin ta d’auki roba ta juye a ciki, ba b’ata lokaci ta jika ta Shiga Sha sai da ta Shanye,ji tayi kamar bata Sha komai ba amma ko ba komai ya tare Mata wani gun, d’akin ta ta Koma ta gabatar da sallar la’asar bayan ta idar ne ta d’auko uniform d’in islamiyar ta sannan ta d’auki jakarta ta fice daga gidan, dake ba nisa daga gidan su Bata d’au lokaci ba ta Isa, bayan sun tashi suna tsaye da shamsiyya sai ta ga wucewar motar gidan su ya shigo, wani irin muguwar harara safiyya tayi musu had’i da tskai Mai Kara sannan ta shige motar suka fice daga makarantar.

Shamsiyya mamaki ne ya rufe ta baki a bud’e take kallon bayan motar har suka fice ta daina ganin su sannan ne ta Maida kallon ga Asiyah Tace “kamar safiyya na gani ko? Ko ba ita bace?”

Murmushi tayi sannan tace “Eh itace” tana maganar ne tana kokarin b’oye abinda ke damin ta, Kai shamsiyya ta girgiza Tace “Kina so kice min har yanzu Mummy Baraka Bata daina abinda take ba?”

“Shamsiyya sai ma abinda ya karo kawai ki cigaba da sani a addu’a”

“Ina kai Qawata Amma Ni abinda ya bani mamaki shine naga har safiyya ta wuce ba tare da ta mana Magana ba sai ma wani irin kallo da ta mana”

“Ni kaina lamarin safiyya na d’aure mini Kai, daga jiya zuwa yau ta sauya min na rasa dalili”

Tab’e baki tayi Tace “Ai nasan Dole za a Rina, ta yaza a yi mummy ta zuba Muku Ido bayan irin son da safiyya take Miki Kuma ta barku, idan ba ta Mata muguwar hud’u ba, to tabbas ta Mata wani abun”

“Ke dai Allah ya shirye ki baza ki canza Hali ba ya kamata ki sani shi fa zato zunubine ko da ya kasance gaskiya ne”

“Zaki Fara wannan wa’azin naki” karar horn da ta ji ne yasa su juyo was a tare, shamsiyya Tace “Zo Muje ganan driver d’in mu sai mu ajiye a hanya”

“A a Kar ki damu zan taka da kafa na ai ba nisa” shamsiyya tayi tayi da ita Amma ta ki hakan yasa sukayi sallama ta shige motar, Asiyah Kuma ta nufi hanyar gida.

A nitse take tafiya damuwar duniya ta had’u ta Mata yawa hakan Shiyasa ta Fara tilawar haddar ta acikin zuciyar ta.

Wani handsome guy na hango zaune yake a cikin mota black kirar Ferrari 2020 sai sheki take,baki a bud’e ya ke kallonta taka birkin motar yayi Wanda shi kansa Bai sai yayi ba abokin tafiyar ji yayi ya buge goshin sa sabida irin taka birkin da yayi da saurin ya dafe kansa Yana ambatan “Innalillahi wa Inna ilaihirraji’un” d’ago kansa da yayi yaga har ya fita, da saurin gaske ya Sha gaban ta, yace “Emmata ji Mana” wani irin kallo tayi Masa daga sama har kasa, dogo ne,Fari ne tass fuskan sa d’auke yake da gemu irin Wanda samari ke yayi bai cika Masa fuska ba Wanda shi ya Kara kawata Masa fuskar say, hancin sa dogo ne sosai har b’aka, sai d’an madaidaicin pink lips din sa wanda ya Dace da fuskar, kunnen sa sanye yake da earpiece sannan yasa pea cap, sanye yake da farin T-SHIRT had’i da Wando Jean Mai Ruwan Navy blue, sai da ta Kare Masa kallo Tass Kan tayi kokarin tafiya.

Da sauri yasha gaban ta yace “Please am sorry, my mistake Sallama ya kamata na miki, Assalamu Alaiki” Yana maganar hannayen sa a hard’e guri gudu, fuska a d’an tamke ta amsa da “Wassalam”

Yace “Dan Allah Emmata idan baza ki damu ba zan iya sanin sunnanki?”

Kallon sa kawaii tayi sannan ta sake kau da kanta, a Karo na biyu ta sake fad’in “Tun da na ganki naji zuciya ta ta kamu da sonki, na ga bazan iya barin ki ki wuce ba tare da na Miki magana ba ji nake kamar bazan iya Rayuwa babu ke ba”

Ganin tayi Shiru ba ta da niyar bashi amsa sai yayi kokarin matsowa kusa da ita, Asiyah ganin hakan tayi saurin bin ta gefen ta sa arce da gudu, magana yake Amma ina bata saurare shi ba.

Hannu ya d’aura a kwankwason sa sannan ya girgiza Kai huci yayi Had’i da fad’in “Kiyi iya gudun ki insha Allah sai na Nemo ki” murmushin yayi Had’i da girgiza Kai a Karo na biyu, sai ya nufi motar ya Shiga ya zauna.

Abokin tafiyar tasa yace “Kai Amma anyi soko wallahi yanzu akan wanchan Yar Yarinyar chan kake kokarin hallaka Ni?”

 A hankali ya juyo ya kalle shi ganin yanda bakin sa ya kumbura yasa shi fashe wa da dariya yana nuna fuskar abokin tafiyar nasa sai da yayi Mai isar sa yace “Faisal kaga goshin ka kuwa?”

Rai a b’ace yace “Ina zan gani tunda makahone Ni, Amma wallahi Hashim ka Raina min wayo tsabagen mugunta da rashin tausayi irin naka ka ji min rauni Kuma ka tsaya kana min dariya?”

Wanda aka Kira da Hashim na gani Yana kokarin rufe bakinsa da hannun sa ganin ran abokin nasa ya soma b’aci yace “Am sorry my man wallahi baka yanda yarinyar Nan ta tafi da imani na bane ba, kasan wani irin shock da naji kuwa?”

Tunda Hashim ya Fara magana Faisal yake kallon Adams Baki a bud’e hannun sa Kuma a Kan goshin sai sai da ya Bari ya ida maganar dake bakin sa kana yace “Hashim Kenan kana da abin mamaki, naga Kaine kullum kake fad’in baka da lokacin Mata Kuma baka ga yarinyar da zaka bud’i Baki kace kana sonta ba?”

“Eh Haka nace Amma yau na gani tunda gashi ka gani na Mata magana Kuma na fad’a Mata Ina sonta”

Dariya Faisal ya Shiga yi Yana tafi yace “kaji mahauci waya ce maka Haka ake tinkarar mace daga had’uwa sai kace kana sonta, meyasa baza ka bari na saka a hanya ba?”

Tsaki Mai Kara yayi sannan yace “Amma ai kaga sanda na fita ko?”

“Ina na gani ji nayi kawai na buge goshina”

“Ina zakaji ka tsaya kana sana’ar chatting da Emmata”

Murmushi Faisal  yayi Yana shafa kasumabar sa sannan yace “Alhaji baka San d’adin chat da Mata bane wallahi shiysa”

“Kai ware dalllah, Ni yanzu Taya za a yi na sake ganin yarinyar Nan?”

“Oh Allah Kai Kuma abin ta Kan kwaila ka Fara”

“Eh d’in kasan yarinyar Nan tafi Wannan mahaukaciyar budurwar ka”

Kama Baki yayi yace “Babyn tawa kake Kira mahaukaciya?”

“To mene ne in ba mahaukaciya ba, yarinya tayi kwalli kamar Mai aljanu?”

“Lallai Hashim one zero kaci tuwo a kaina Amma ba komai zan Rama”

Dafe Faisal Hashim yayi sannan ya Shiga girgiza shi had’e da fad’in “am sorry am sorry yanzu dai please help me out, ya kake ganin za’a yi?”

Kau da fuskar sa yayi ya d’an yi shiru kana yace “Let’s follow her muga gidan su, don alamu sun nuna a unguwar Nan take”

Cikin murna yace “Good advice” Nan ya murd’a key suka bi bayanta.

Asiyah tunda ta bar gun bata daina gudu ba har sai da ta Isa bakin gate na gidan su, Kan ta dai daita nitsuwata sannan ta bud’e karamin gate ta shige Ciki.

Hashim da Faisal sai dube suke Amma Shiru kake ji basu ganta ba Yar karamar tsaki Hashim ya ja had’e da buga steering motar sa kan kana yace “Kamar aljana ta b’ata baat?”

Yana maganar Yana leka waje.

“To wa ya sani ko aljannar ce , don nayi mamakin yanda ka damu da ita a lokacin guda haka in……”

Hararar da yayi Masa ne yasa Faisal ta kasa karasa maganar da yake.

Sauka yayi a Kan titin yayi parking a gefen, Faisal yace “Kar ka damu tunda dai tana zuwa islamiya ta kwana gidan sauki gobe ba sai mu dawo ba?”

Murmushin samun nasara yayi yace “Thanks Abokina” Nan ya tada motar suka bar unguwar dropping d’in Faisal yayi Kan ya wuce gida bai tsawon lokaci ba ya Isa gida dake gidan nasu ba nisa.

πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦

Kuyi hakuri da wannan, sabida na Koma maranta.

Wattpad bana ganin vote an Comments d’inku alamu sun nuna Baku Jin d’adin book d’in sabida zan daina d’aurawa kawaii.

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like

MATAR UBA 33

Advertisement   πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦      *MATAR UBA* πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦ Daga Alkalamin ✍️               *Milly*…

MATAR UBA 4

Advertisement  πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦           *MATAR UBA*  πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦        _( CHAPTER 4 πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦ ……..…

MATAR UBA 36

Advertisement  πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦      *MATAR UBA* πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦ Daga Alkalamin ✍️               *Milly*  …

MATAR UBA 21

Advertisement πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦      *MATAR UBA* πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦ Daga Alkalamin ✍️               *Milly*  …

MATAR UBA 32

Advertisement   πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦      *MATAR UBA* πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦ Daga Alkalamin ✍️               *Milly*…

MATAR UBA 12

Advertisement  πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦           *MATAR UBA*  πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦        _(A True Life Story_ )…