Advertisement
Halin Girma
17
Hafsat Rano
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK๐๐พ_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
Advertisements
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK๐๐พ_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK๐๐พ_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK๐๐พ_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
****************
“Sarki!” Ta zaro ido cikin tsananin kaduwa
Advertisements
“Laifin ki me, duk laifin ki ne, da baki yi min karya ba, da baki boye min abinda kika gani ba, da nasan abinda ya kamata nayi tun a lokacin.”
“Haba Yaya Hajara, komai fa da kika gani ya faru toh dama chan haka yake a rubuce.”
” A ah Maimuna, wannan kam sakaci na ne, ni ce duk na jawo komai, gashi yanzu bansan yadda zan ba, komai ya kwabe min.”
” Hakuri kawai zamuyi mu tayasu da addu’a, kudi ba shine kwanciyar hankali ba,rufin asiri shine, idan har Bashir din zai kula da ita ai shikenan, a hankali sai suyi kudin su.”
” A ah, ba zai yiwu ba, shegen yaron nan da har zai iya yaudarar mu, ya ha’ince mu ke kinsan ba mijin kwarai bane, dole Dr yazo a sake sabon zama, wallahi ba zan bawa yata mayaudari ba.”
” Toh wai yama akayi? Kika ganshi a fakiri sannan kuma ya koma dan sarki? Ta yaya hakan ta faru? Bayan babu wani abu da ya nuna hakan tun farkon zuwan sa?”
” Salamu alaikum.” Habib ya yi sallama kafin ya shigo dakin, su i su ne a ciki shiyasa ya shigo kai tsaye, ya gaida sisters din Mama sannan ya kalli Zeenat dake gefe tana matsar kwalla, yayi kwafa ya zauna akan kujerar gaban mudubi yace
“Kiyi hakuri Mama dan Allah, amma ni da kaina na fad’a miki Bashir ba mutumin kirki bane, yanzu dai hakuri kawai za’a yi tunda lokaci ya riga ya kure, dan Allah karki yiwa Abba wata magana kinsan dai ba zai saurara ba, dan Allah ki kwantar da hankalin ki, kiyi musu addu’a arziki ai na Allah ne. “
Wani kallon banza Mama tayi masa, kafin ta nuna masa kofa
” Fice ka bani waje bana bukatar maganar ka. “
Mikewa yayi, yana jin babu dadi abinda Maman take yi, tun daga irin rikon da tayi wa Iman din wanda sun sha haurawa sama a kai idan yayi mata magana, daga baya sai ya daina kawai ya watsar amma kuma ya kan yawan yiwa abokin sa sadeeq maganar ta akan zai bashi Iman din saboda yadda yaga zaman da take yana so yaga ta samu yanci, akwai ranar ma da hira ta saka ya kwashe komai ya sanar wa sadeeq din duk da yasan kamar tonawa mahaifiyar sa asiri yayi amma kuma ya zai? Baya jin dadi sam.
Kofar ya ja musu ya bar gidan ma gaba daya dan ba zai zauna ya cigaba da kallon bacin rai ba. A waje suka hadu da Abba ya aike shi karbo wasu kaya sai kawai ya biya ya dauki sadeeq suka wuce tare.
***Har dare Abba be shigo ba, idon Mama kamas tana jiran sa, Zeenat ma idon ta biyu sun shirya samun Abban ita da Maman ayi magana dan da gaske take ba zata kuma auri Bashir ba yanzu, musamman bayan taga kayan da aka ce wai nata ne, toh wai mana, dan bata saka rai ko hasashen irin su ba ko kad’an.
Kamar Abban yasan za’a yi haka yaki shigowa da wuri har sai da suka soma kosawa, gaba daya duniya bata musu dadi sam, Bashir sai kiranta yake amma sam taki dagawa dan bata da lokacin sa balle ta wayar sa.
Wajen sha biyu Abba ya shigo bayan ya gama kallon kayan iman din a bangaren Gaji duk da be iya kallon komai ba sama-sama shima don sun matsa masa ne, Gaji ce ta kirashi daki tace ko me Maman zatayi kar ya yarda ya biye mata, ayi a gama komai lafiya shine kawai.
Yana shigowa ya gansu a falon Zeenat na rakube a k’asan kujera tana cigaba da matsar kwalla, yi yayi kamar be gansu ba, yayi hanyar dakin sa Mama tayi saurin tare shi
“Dr.”
“Kinga dai a yadda na shigo kinsan akwai gajiya, ki bar duk wata magana zuwa gobe da safe idan ALLAH ya kaimu.”
“Ba zai yiwu ba, idan na bari aka kai gobe na samu matsala, yanzu zamuyi ta mu san abinda muke ciki.”
Kada kansa yayi ya dawo ya zauna sannan yace
“Ina jinki.”
“So nake a fasa auren Zeenatu, ba zata auri Bashir ba.”
Wani banzan kallo Abban yayi mata, kafin ya hade rai sosai yace
“Ashe ma ke mahaukaciya ce ban sani ba Hajara, Ashe baki da tawakkali ma, ashe ma baki san komai game da rayuww ba, bari kiji.”
Ya juyo yana kallon ta
“Dama shi sharri dan aike ne da kike ganin sa, duk in da yaje sai ya dawo, dan haka Wallahi, Wallahi kinji ma rantse ko?”
” Ba zan karya alkawari na ba, ba kuma zan zama mutumin banza ba, sai dana jaddada muku ke da ita gata nan, nace kunji kun gani? Sai yanzu da ya rage yan awowi shine zaku zo min da maganar banza? Saboda bansan me nake ba ko?”
” Idan kana kaunar Allah Dr ka rufa min asiri a fasa auren nan dan Allah!”
” Lallai Hajara kin haukace, wallahi babu abinda zai hana auren nan sai dai idan cikin mu biyu babu wani, ko ni na mutu ko ita Zeenat din ta mutu, amma in dai da ranmu da lafiyar mu wallahi sai an yi, kinji ma na gaya miki.”
” Abba dan Allah kayi hakuri, wallahi zan iya mutuwa.”
” Allah ya jikan ki.”
Ya tashi yayi shigewar sa daki ya saka key kar ma ta samu damar biyo shi dan a yadda ya hangi tashin hankali a idon ta, zata iya jure su kwana a tsaye akan maganar da babu komawa baya.
Wani irin marayan Kuka Zeenat ta fashe dashi, bata san ba son Bashir take ba, kwadayin abun sa da kuma kishin Iman ya sakata ganin kamar son nashi take, sai yau ta gane kawai bakin cikin da take wa Iman ne ya sakata amince dashi.
A zaune suka kwana, babu kalar tunanin da Mama batayi ba akan washegarin, har da tunani ko ta dauki Zeenat ta gudu da ita? Kafin gari ya gama haske tuni hayaniyar gidan ta cika ko’ina wanda ta tabbatar da gangan suke yi don a kular da ita.
Da k’yar taayi sallah ta saka Zeenat ma tayi lokacin yan uwa har sun tashi sun fara gyara shashen Maman.
Dakin Abba Mama ta shiga, ta same shi ya fiddo sabbin kayan sa da zai saka ya ajiye a saman gado, yana waya da Maman Iman, duk da ta shigo amma be daina wayar tasa ba, ya cigaba da yi mata bayani
“Masu zuwa daurin auren su taho da ita, kinga anan dinma za’a so a ganta, in yaso daga nan sai a wuce kawia da ita.”
“Owk shikenan.”
Ta amsa sannan ta kashe wayar. Haushi ya sake turnuke mama amma ta share dan ba abinda ya dameta bane a yanzu, matsalar da take ciki yanzu tafi wannan.
“Ina kwana?” Ta durkusa a k’asa ta gaishe shi,
“Lafiya lou.” Ya amsa a gajarce yana cigaba da duba sakwannin wayar sa.
“Dan Allah Dr kayi hakuri, hannun ka baya taba rubewa ka yanke ka yar, kar ka hukunta yar ka akan laifin da ni na aikata, naji duk hukuncin da zaka yi min kayi min amma dan Allah a fasa auren nan.”
” Kinsan Allah?” Yace yana ajiyewar wayar hannun sa
” Ba zan fasa auren nan ba, iyayen yaron nan sun zo na karbi maganar su nayi komai har sun kawo lefe sai yau ranar kawai kice a fasa? Nace musu me kenan? Tun farko ban fad’a muku ba? Ban nuna muku illaar abinda kuka nace akai ba, kuka nuna min ku ba zaku fasa ba, har kika saka zeenatu ta watsa min k’asa a ido ina mahaifin ta, ko da ace Bashir yaron kwarai ne idan nace ta hakura dashi ba zaki taimaka wajen ganin ta yi min biyayya ba? Amma me kikayi? Sannan sai yanzu, sannan zaki zo min da maganar banza, ya kike so nayi?”
” Dan Allah nidai kayi hakuri ka yafe mana,dan Allah ka taimaka.”
” Wallahi Hajara babu abinda zan iya akai, kinji ma na rantse, ki barni dan Allah.”
Zama tayi dabas a k’asa, sai kuma ta tashi da sauri ta fice ta nufi shashen Gaji, ta same su a falon yan uwa ana ta shewa, ta wuce su zuwa ciki kamar wadda ta zare. A k’asa ta tsuguna ta gaida Gaji wanda rabon da tayi haka an dade.
” Dan Allah ki taimaka ki saka baki Dr ya fasa auren nan, wallahi idan akayi auren komai zai iya faruwa, nasan ke kadai yake jin magana dan Allah.”
” Yana ina?”
” Yana gida, dan Allah ki taimaka min.”
” Kije kice idan ya gama ina neman sa, Allah ya kyauta ya rufa asiri, sai a hakura kawai.”
Tashi tayi da sauri, ta manta ko godiya bata yi ba, ta fice kowa ya bita da kallon mamaki cike da jin haushi. Ko da ta fadawa Abban be ce mata komai ba, da ya fito ya shiga wajen Gajin bata yi masa maganar ba, ya gaisa da kowa sannan yayi breakfast da masa ya wuce wajen yan uwan sa.
***Daren ranar Moh be runtsa ba, duk wasu bakin da zasu iso sun gama isowa a lokacin kowa an sama masa masauki na alfarma. Abokan sa da sukayi karatu tare suke kuma aiki tare sai dai kowa wajen da take daban ne suka sauka a cikin gidan a bangaren Moh din, kafin a daura auren su wuce adamawa sannan su sake dawowa Kanon saboda events din da za’a yi a Kanon.
Raba dare sukayi ana hira, anan suke fad’a masa suma fa sun shirya masa kayataccen bikin sword crossing amma a abuja saboda suna so manyan su na wajen aiki su ma su zama sun samu halarta. Abubuwan sun so suyi ma Moh yawa saboda shi dai tsakanin sa da Allah zai fi so ace da an daura auren kawai su yi tafiyar su shi da ita,amma kowa kokari yake ya shirya wani abu da zai sake rik’e su, shi dai kawai dan kar ya fito fili yace baya so ne, amma har ga Allah da kowa ya hakura.
Da suka tashi da safe ma wasu suka dora da hirar in da Musaddik da wasu ciki suka tafi karasa abubuwan da basu samu gamawa ba, duk da sai bayan sallar juma’a za’a daura auren kuma komai da ya kamata su yi an ma riga an gama amma suma zasuyi nasu kokarin ko yaya ne.
Tun wajen sha biyu Takawa ya saka aka kira masa Muhammad, ya same shi da manyan mutane har da Mr President sai Bubu da tasa jama’ar. Aji dan tsoho ma ba’a barshi a baya, yaji dadin ganin su musamman Aji da be saka ran zuwan nasa ba. Bin su yayi daya bayan daya ya gaishe su dukka, kowa ya kawo kyautar bangirma ya damka masa, harda masu blank cheque duk dan a birge Takawa.
Godiya yayi musu dukka ya koma wajen jama’ar sa, suka dauki duk abinda zasu dauka suka wuce gidan Moh din dake Lamido Crescent yadda zasu fi yin komai a tsare.
***Wanka na wajen uku kenan idan tayi ta gama da wannan hadin ruwan sai Mamma ta sake bata wani, gaba daya wani irin sulbi fatar jikin ta take yi, tayi wani irin haske me kyau fatar ta sai glowing take kamar fuskar ta taji labari.
Tun da aka soma mata gyaran jiki ta tabbatar da komai nata ya sauya, hatta lallen da aka yi mata da gyaran gashi na daban ne, bata kara tabbatar da gatan da take dashi ba sai a event din da aka yi jiya taga tarin mutanen da suka zo domin ita, kowa don ya ganta kawai. Tasha kyaututtuka daga kawayen Mummy da yan uwa kowa burin sa ya yi mata abinda zai burge mummy din.
Sosai kuwa Mummy taji dadi ba kad’an ba, duk kuwa da miskilancin ta amma sai da yanayin ta ya sauya sosai.
Bayan an yi taron an gama ne da daddare take bawa Iman din labarin yadda akayi suka rabu da mahaifin ta.
“Kinsan aure rai ne dashi, idan lokaci yayi sai an rabu, amma har gobe ina son mahaifin ki, kaddara ce kawai ta raba mu, a lokacin alhajin mu yayi fushi sosai akan auren da mukayi ba da sanin kowa ba. Alhajinmu me kudi ne sosai kuma dan siyasa ne, yana matakin senate president a lokacin, hakan ya saka dole Ibrahim ya sake ni akan kar abinda mukayi ya shafi mutuncin sa, dan wasu ba zasu taba yarda da cewa munyi aure ba, ko bayan an haife ki nan ma yace a dole dole sai ya karbi yarsa, ya rik’e ta dan baya son ko kad’an mutuncin sa ya tabu. Hakan ya saka Ibrahim yin fushi, ya karbe ki ya kuma yi alkawarin ba zai bani ke ba, nasha kuka nayi ta rokon sa ina masa magiya karshe yayi min alkawarin idan da rai da lafiya zai kawo ki idan kin isa aure.”
” Amma fa ko bayan nan Alhaji yazo daga baya yayi regretting abinda yayi har ya nemi Ibrahim din da kansa ya kuma roke shi ya bashi ke, dan a lokacin girma yazo gashi yana son gyara, Mamma ce babbar mu gashi har lokacin Allah be bata haihuwa ba ,amma sai Abban naki yaki yace yayi hakuri ba zai iya ba.”
” Ni banga laifin shi ba dan nasan shi da Zuciya idan har aka taba shi,karshe dai nima nayi aure bayan na kammala wani course da nake na auri wani dan siyasa Babba, na dade sosai a gidan kafin karshe Allah ya bamu haihuwa daya, na haifi yan biyu Amaan da Amaani, daga nan kuma sai muka rabu.”
Shiru Iman tayi tana harhada maganganun.
“So kinga kowanne bawa baya wuce kaddarar sa, ni dake haka kaddarar mu take, dole ne kuma mu karbe ta hannu bibiyu mu gode wa Allah.”
“Haka ne mummy, wallahi na zata so Amaan yaran Mamma ne.”
Murmushi tayi
“Yaranta ne kam, tunda dai ni ban wani san komai akan su ba, Itace komai dinsu, Allah be bata haihuwa ba shiyasa ta dauki son duniya ta dora akan su.”
“Hajiya fa?”
“Step Mom dimu ce,itace ta haifi Zayd.”
“Allah sarki tana da kirki.”
” Sosai, kirkin ta yayi yawan da karyar mutum ya shigo gidan nan yace ba ita ce ta haife mu ba, ita ta kula da koman mu, Itace kuma a matsayin mahaifiyar mu har gobe.”
” Ashe akwai step moms masu kirki?”
” Akwai su da yawa Iman, ba dukka aka taru aka zama daya ba, wasu kuma zaki ga yaran ne basu da kirki sam, sun takura mata sun hana ta sakat, komai dai da kika gani akwai good side dinsa akwai bad side haka rayuwar take.”
” Haka ne.” Tace tana tuna Mama da Zeenat
Shirya ta aka yi cikin wasu yan ubansu kaya, kayan da ta tabbatar ba kananun kudi aka kashe wajen samar dasu ba, komai na jikin ta unique ne, me kyau da ya dace da ita. Sarkar gold din da Mummy ta siya mata Mamma ta saka mata, sannan ta zaunar da ita a gefen gado ta dauko mata abinci, ta zauna da kanta ta taimaka mata ta ci dan ta tabbata idan suka tafi babu batun cin wani abinci a wajen amarya. Ci tayi sosai sannan ta dauko wayar ta tana duba misscalls ko ya kirata, be kira ba, ajiye wayar tayi akan cinyar ta har lokacin tafiyar su yayi, text message ta tura masa ta saka wayar a jaka suka fito gaba daya, wajen Hajiya aka kaita tayi mata nasiha sosai kafin su nufi airport da su Ya Mubarak da sauran jama’ar da zasu halarci daurin auren, sai kuma su Amaani, Mamma da yan uwan su da zasu je a karasa bikin da su a matsayin dangin Mamanta.
Mintuna kad’an suka isa dasu Kanon, dan ma basu taho da wuri ba, Abba ne ya saka aka je aka taho dasu daga airport din, aka sauke su a bangaren Abba babba, ita kuma Iman aka wuce da ita ta gaida Gaji sannan suka shiga wajen Mama.
Gabanta ya fadi tun shigowar su, ko wanka bata yi ba, duk da ta dan samu nutswa bayan ta samu Gaji, tana da yakinin zata hana Abban kuma ya hanu, amma kuma jikin ta duk yayi sanyi tana dai zaune ne tana kallon kowa, masu kaya-kaya ma a cikin yan uwan ta haushin su take ji, gani take ai kamata yayi su tayata alhini. Kawayen ta kuwa da sun kirata take dagawa tace an daga bikin zata neme su, abinda bata sani ba zance ya gama zagaya ko ina wasu ma da gayya suke kiran dan su tabbatar.
Gaishe ta Iman take amma ta tsura mata ido ta kasa amsawa, tsabar bakin ciki ta kasa boye shi, mamakin yadda yarinyar ta sauya take, Ashe haka take da kyau bata sani ba? Ko Kuma dai yanzu ne kyawun ya fito. Kayan jikin ta kawai ta kalla tasan an kashe kudi, idon ta ya sauka akan sarkar wuyan ta, tana ta sheki da kyalli kana gani zaka gane zallar gold ne. Tari ne taji kamr zai sarke ta, duk suna lura da ita da suka ga kamar bata hayyacin ta sai kawai suka tashi suka koma in da aka sauke su.
Lokaci lokaci Iman na kallon wayar ta, ta matsu suyi magana ta san halin da ake ciki, ba zata kirashi ba dan tasan yana cikin hayaniya amma taso ko yaya ne ya kirata.
Daidai lokacin da aka saka na daurin auren yayi, ta kwanta kawai lamo tana jin faduwar gaba, wani iri kamar tace ta fasa, ba’a gidan ake daura auren ba, a babban masallacin Kano ne da yake kusa da gidan sarki shiyasa basu san abinda yake faruwa ba.
Ji tayi gidan yayi tsit, kamar babu mutane, ta dinga jin wani tsoro tsoro yana shigar ta, Mamma ce ta taba ta, tayi mata murmushi tace
“Kowacce mace ta kan ji irin haka idan za’a daura mata aure, kiyi addu’a kinji yata?”
Da kai ta amsawa Mamman, ta soma karanta hasbunallahu wa ni’imal wakil, a hankali taji nutsuwa na saukar mata. A daidai lokacin suka ji karar tsayawar motoci, kafin gidan ya kaure da wata irin guda me karfin gaske.
Wani maroki ne me muryar tsiya, ya shiga kirari cikin muryar sa da ta shiga har kwakwalwarta, ta tsaya chak da tunanin abinda kunnen ta yaji
“Alhamdulillah, Allah mun gode maka, an daura auren Yarima Muhammad da amaryar sa Gmbiya Fatima, dan sarki jikan sarki, kuma sarkin gobe idan Allah ya kaimu.”
Farin ciki ne ya kama su Mamma suka hau murna, bata fuskantar komai, a daidai lokacin sakon sa ya shigo wayar ta,
“Duba whatsapp dinki amarya tah.”
Da sauri ta shiga whatsapp din har ta mantawa bata kunna data ba ,kunnawa tayi messages din suka shigo tayi saurin bud’e nasa. Hotuna ne masu yawa, ta hau bud’e su tana kura idon ta, hoton farko ya saka numfashin ta tsayawa na dan sakanni
“Capt Muhammad Ahmad Santuraki.”
Yayi captioning hoton, yana sanye da nadi irin na sarauta, da kunnuwan sa guda biyu a sama da yake nuna yadda tsarin sarautar take, gaba daya gani tayi an sauya mata shi,shine sai wasu abubuwan da yawa da suka dauke ta zuwa wani tunani na baya tana kokarin alakanta abubuwan da tayi ta shakku akan sa. Kwanciyar fatar sa, da yadda yake magana yana bata mamaki matuka.
Sauran hotunan ta shiga bubbudewa, duk akwai shi aciki tare da manyan k’asar da ma ketare, hoton sa da Takawa da yadda Takawan ya rik’e shi says alot. Ji tayi gaba daya ya goge mata hadda, ya bar kanta blank bata ma san wanne irin tunani zatayi ba.
Wasu mata ne suka dinga shigowa, wanda kana ganin su zaka san su din hadimai ne daga gidan sarauta, duk suka taru waje daya cikin girmamawa suka hau gabatar da kansu.
Kayan hannun su Mamma ta saka suka ajiye a gefe sannan ta aika wata bangaren Gaji akan wasu suzo a cikin dangin Abban, hakan ya bawa Iman damar sulalewa ta shige dakin Umma, sannan ta kira Ya Maryam ya waya tace dan Allah tazo dakin Umma. Sai gata tazo har da saurin ta, murna fal fuskar ta dan suma ba karamin mamaki suka shiga ba.
Hotunan ta soma nuna mata, sannan ta hau mita kamar zatayi kuka, katse ta Ya Maryam tayi,
“Yarinya kad’an ma kika gani, sai kin ga uban lefen da aka kawo miki, wallahi Iman Allah ya baki miji, miji na kere sa’a me sonki tsakani da Allah, kinyi sa’a, halin ki ne ya jawo miki amma.”
“Amma me yasa zai rufe ni?”
“Haka tasa salon soyayyar yake, kin ganshi kuwa? Salo,aji kyau ga kudi.”
Turo baki Iman tayi, ta rasa me ma zatayi, Itace zata shiga gidan sarauta? Sarauta ma babba irin ta Kano? Katse mata tunani yayi da wani sakon nasa
“Meet me a seat room din Abba, na matsu na ganki, I want to feel you right close to me.”
Da sauri ta kife wayar,. Maryam da taga komai ta kyalkyale da dariya
“Su Iman an shiga sahun manya, jeki dan Allah yaji duminki, halal dinsa ce ke yanzu ehe.”
Duka ta kai wa Maryam din ta manta ma basa yar haka da ita, ta sake kwanshewa da dariya tana tsokanar ta
“Saura kije ki dinga wannan nuku nukun naki, tashi ki sake gyara jikin ki, bari naje na karasa jin drammer da ake a gidanku, Zeenat na chan ta tada aljanu wai ba ta yarda ba, kinsan an riga an daura itama.”
“Kamar ya?” Tace cikin mamaki
“Jeki ke dai wajen aikin Allah, bari zan baki labari in details.”
Ta juya da sauri ta fice bayan ta sanarwa da Mamma cewa Iman zata je yarima na seat room suyi hotunan tarihi.
Rano๐๐
#Note edited
*_ZAFAFA BIYAR 2022๐ฅ_*
*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*
_SO DA ZUCIYA_
*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI’AR ZUCIYA_
*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_
*_HAFSAT RANO_*
_1aHALIN GIRMA_
*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_
*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*๐๐
Dโaya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k
*_Zaku tura kudin a_*
6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*
*Sai shedar payment dinki a*๐๐๐
08184017082
*Kokuma katin waya na MTN anan*๐๐
09134848107
GIPHY App Key not set. Please check settings