Advertisement
Halin Girma
24
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
Advertisements
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
Sai da rana ta daga sosai sannan ta farka, da sauri ta mike tana mamakin dadewar da tayi tana bacci ita da ya kamata ta koma wajen su Mamma. Sakkowa tayi tana jin jikin ta da dama-dama, ta shiga takawa a hankali zuwa toilet din dakin,ta wanko fuskar ta, ta fito ta gyarata sannan ta cire jallabiyar tasa ta maida kayan ta, ta ajiye masa a gefen gadon ta fito zuwa falon. Tunanin yadda zata iya komawa wajen su Mamma take da kuma yadda zatayi da kunyar da take ji daga zuwa ta dawo sai kwana bayan ba haka ya kamata ba a ganinta. Abin takaicin ma bata dauko wayar ta ba balle ta kira, tana tsaye tana tunanin yadda zata fita taji maganganu a kofar part din,wajen window ta isa, ta daga curtains din tana son ganin komai. Gabanta ne ya fadi, tayi saurin cika window din a daidai lokacin da taji suna karasa maganar su. Kyakkyawa ce ajin farko, kana ganin ta kaga bafulatanar adamawa, yau ba kamar jiya da ta soma ganin ta ba, tana cikin shiga me kyau harda Alkyabba, tayi kyau fuskar ta fes alamun tana cikin farin ciki. Kokarin daidaita kanta tayi sanda taji an turo kofar an shigo, idonsu ya hadu lokaci daya, wani banzan kallo Lailan ta watsa mata tana karaso wa ciki a gadarance, ta samu saman daya daga cikin kujerun falon ta hakimce baiwar ta,ta gyara mata k’asan rigar sannan tace ta fita ta basu wuri. Tana fita ta kalli Iman irin kallon sama da k’asa kafin tace
“Barka da rana amaryarmu.”
“Sannu.” Kawai Iman din tace ta juya zata bar wajen amma sai ta dakatar da ita
Advertisements
“Nace ba, ya kika ji da kwanan bakin ciki? A ranar farkon ki a dakin mijinki?”
“Bakin ciki kuma? Na me kenan?” Ta tambaya Kai tsaye kamar bata gane me Lailan take nufi ba
“Na abinda kika gani mana, bakin gani, kinga true color din so called mijinki ko?.”
” Ohh, wannan wasan kwaikwayon wai? Yayi kyau sosai ya kuma tsaru yadda ya kamata, sai dai shi actor din be san kan wasan ba dan be ma san me yake faruwa ba, shine kawai matsalar film din amma yayi kyau.”
“Me kike nufi?” Tace a hasale tana mikewa tsaye
” Abinda kika sani shi nake nufi, kin dauka zan yarda da banzan plan dinki? I’m not an illiterate, I can tell when someone is lying, beside mijina ba zai taba aikata abinda kika ikirarin ya aikata, and i trust him yadda bakya tunani.”
“Wow! Wow!! Wow!!! Sannu da kokari, I love your confidence, amma wanne irin sani kikayi masa haka? Da har zaki bashi irin wannan yardar? Kinsan waye namiji kuwa?”
” It doesn’t matter yaushe na sanshi, all that matters now shine, miji na ne, kuma nayi trusting nashi, dari bisa dari.”
” Shikenan, sai muga yadda zakiyi depending mijin naki at this critical condition, let’s see how far you can go….”
” Kwana hudu kachal kike da, idan har baki samu way out ba. Ki shirya karba ta a matsayin kishiyar ki, sannan na fitar dake ta karfin gaske, dan baki da waje a gidan nan, captain nawa ne right from the start kuma he will always be mine.”
Murmushi Iman tayi mata, tana jin wani irin tsana da haushin Lailan, tana jin zata iya komai, idan tace komai tana nufin komai domin taga ta fitar da shi daga koma menene, akwai babban kalubale a gabanta, amma ba zata karaya ba, duk wanda ya rik’e Allah da addu’a ya gama, da ikon Allah sai tayi galaba akan duk wani makiyin su. Ta daina shiru, duk wanda yace mata kule! Zata ce masa chas! Ita kanta bata san tana da courage din da zata iya maida mata martani ba, sai gashi.
Juyawa tayi ta koma bedroom din dan ba zata cigaba da bata lokaci akan wadda bata tunanin tana da hankali ko kad’an. Wayarta ta gani ajiye a saman chest of drawers ta dauka ta kira Mamma da k’yar, sukayi magana ta ajiye ta zauna tana lissafin rayuwar da zatayi a irin wannan gida, tuna sanda ake mata fad’a irin na bankwana tayi, wata Babar su Abba tana ta jaddada mata hakuri da kuma shirya wa duk wani kalubale na gidan sarauta, karta bari a takata kar kuma ta cuci kowa, akwai makirci sosai wanda zata gamu dashi amma idan ta nutsu tayi hakuri da karfin addu’a Allah zai bud’e mata komai.
Bata jima a zaune ba taji ana mata knocking, ta tashi ta bud’e ta fito, russunawa tayi har k’asa da sauri ta gaishe ta, kunya ta kama Iman din ganin Matar da zata yi kusan sa’ar Mama tana gaishe ta a haka. Kaya ta mika mata cikin girmamawa tace ta chanja zata rakata bangaren Fulani (Ammi) juyawa tayi ciki, dan dama kayan jikin ta sun dame ta sosai. Sai da ta shirya tsaf sannan ta fito, ta lura Laila ta jima da barin falon sai dai mayen kamshin da take yana nan a falon. Kai tsaye shashen Ammi suka wuce wanda sai a sannan ne ta sake karewa fadar gani sosai. Anan suka tarar da su Mamma da wasu mutanen wanda da yawan su kana kallo zaka gane alakar su da gidan saboda yanayi na kama da suke da juna. Shigowar su ya saka kowa maida hankali kanta kowa na son ganin amarya, tunda jiya babu wanda ya samu ganin ta saboda dare. Kanta a k’asa taki yarda ta dago saboda yadda take jin kamar ta nutse, a tunanin ta duk sun san daga in da ta taho, bata san Mamma bata fad’a ba sun dai barshi a zuwan sun barota ne tana shiryawa. Sai da duk suka lafa ne aka zazzauna sannan ta gaida Mamma da take kallon ta da murmushi, murmushin da ita kadai ta san ma’anar sa, hakan ya sake saka Iman din cikin jin kunya.
Sanda ta shigo Ammi bata falon, tana zaune suna magana da Amaani ta dawo, da sauri Iman din ta zamo daga kujerar ta gaishe ta, ta rik’e ta, ta mik’ar da ita tsaye tana amsawa a sake sosai, sannan ta saka a raka Iman din part din Kilishi.
Hannun ta cikin na Amaani suka shiga, babu kowa a falon farko sai wata baiwa guda tana goge-goge,wadda ta rako su ce tace su zauna sannan ta nufi kofar ciki don sanar da zuwan su. Jim kad’an ta dawo ta tsaya a gefe, zuwa wani lokaci Kilishin ta fito, fuskar ta kadaran kadahan ba zaka gane komai ba, Iman bata kalle ta ba, ta gaishe ta cikin girmamawa ta amsa a yatsine bata ma zauna ba.
“Hari wannan din itace sirikar tamu?”
“Itace ranki ya dade.”
“Lallai sannu yarinya, shi ko Muhammad ya rasa wa zai dauko mana sai yar karamar yarinya haka? Ko da yake ra’ayin sa ne ai, ba kuma a san ya akayi ba dai, ko da yake dama dai yaran talakawa sai a hankali, idon su idon me arziki sai in da karfin su ya kare, sannu kinji? Allah ya bada zaman lafiya.”
Sai ta juya
” Hari naga amarya, ki gaida uwar dakin naki.”
Wani abu ne ya tokare wa Iman a makogwaro, idan har ta fahimci maganganun matar tana nufin asiri tayi ta aure shi kenan, a fakaice ta ci mata mutunci babu gaira babu dalili, bayan bata san ta ba, idan banda jiya sai yau ne karo na biyu da ta taba ganin ta. Ajiye ta tayi a daidai mazaunin da da ajiye Laila, ta kuma kuduri aniyar zama dasu daidai da yadda suka zaba.
Daga nan sai suka wuce bangaren Aji da Hajja, amma a mota saboda tazarar dake tsakanin bangarorn biyu, sosai taga karamci da girmamawa dan Adam, Hajja kamar ta goye ta saboda murna, ta dinga tsokanar ta da ta kwace mata miji da rana tsaka, murmushi kawai Iman din take, hakan ya janyo suka dade sosai a bangaren har zuwa sanda taji sallamar sa, ta dago suka hada ido sanda yake shigowa ciki, jamfa da wando ne a jikin sa kalar sararin samaniya, ya tsaya iya kar guiwar sa, kansa sanye da hula me kalar duhu, yayi kyau sosai, da sauri ta janye idon ta kunyar abinda ya faru daren jiya na hasko mata, murmushi yayi me kyau ya karaso ya zauna kujerar dake fuskantar ta. Hajja dake nade a saman wani cushion me laushi ta tabe baki tana dubanss
“Saboda rashin kunya shine ka biyo bayanta ko?”
“Toh ya zanyi? Kin rik’e min ita kin hanata tafiya.”
“Ah lallai, shine ka biyo baya kazo kaga ni, toh ba zan cinye ta ba ai.”
“Kai yar tsohuwar nan kin fiye rikici wallahi, kishi ne nasan yake damunki ba wani abu ba.”
Dariya tayi tace
” Ai na bar mata kai tuntuni, kuje ku karata nima Amadu na ya ishen.”
A tare duk suka yi dariya, ya kashe mata ido daya tayi saurin dauke kai kamar bata ganshi ba.
” My wife!”
Yayi kiranta a hankali karaf sai a kunnen Hajja, ta banka masa harara ya sosa kai
“Dan nema, kin hadu da aiki kinji Fatima, mijin nan naki bashi da kunya sam, bari kiga na tashi, taso yan mata muje na baki wani abu ki bar wadannan.”
Tashi Amaani tayi tabi Hajjan, suna shigewa yayi saurin komawa kusa da ita.
“Ka ganka ko?”
“Me nayi?” Ya tsare ta da ido yana marairaice fuska
“Gashi nan ka kori Hajja.”
“Rigimar tace kawai fa, mun saba irin haka da ita.”
“Toh ka koma chan ka zauna.”
” Wai kunya ta kike ji? Ko kunyar Hajja?”
” Both!” Tace tana kauda kanta
Murmushi yayi kawai
” Kinsan me? Bubu ya bani kwana hudu na kawo masa gamsasshiyar hujja, idan ban kawo masa ba, zai aura min Laila.”
Sak tayi, duk da Laila ta riga ta fad’a mata amma ji daga bakin sa ya sakata shiga yanayi,
” Karki damu, hakan ba zai faru ba, I promise you that!”
” Allah ya bada sa’a.” Tace a sanyaye
” Zan je Abuja anjima ko gobe da safe zanyi kwana biyu, na dawo”
” Tafiyar ba zata bamu matsala ba?”
” In sha Allah.”
” Shikenan, Allah ya kaimu ya dawo da kai lafiya.”
Tayi shiru tana tunanin yadda zata taimaka masa ta taimaki kanta dan ba zata taba iya zama da Laila ba a yanayin ta.
***Idan tace tayi bacci a ranar tayi karya, tun bayan fitar matar gidan da kawayenta bata sake nutsuwa ba, kuka take tun tana yi da hawaye har ya zama babu hawayen sai suya da zuciyar ta, take kamar zata fito. Da asubar fari taji ana buga kofar dakin amma a hankali, tashi tayi da k’yar tana jin jiri jiri saboda yunwar da ta kwaso ta zare sakatar dakin. Da sauri ya shigo ciki ya maida kofar ya rufe yana kallon ta, matsawa tayi baya tana masa kallon tsana
“Karka matso nan wallahi zan iya illataka, ka maida ni gidan mu wallahi ba zan zauna anan ba.”
“Rage muryar ki dan Allah, kar taji, kiyi hakuri zan yi kokari naga na lallabata ta bar mu, mu koma gidan mu dan wallahi a matse nake, kinsan dai mutum da sabuwar amarya.”
“Wallahi bazan koma ko wanne gida ba, gidan mu zaka mayar dani ka sake ni kuma, ba zan zauna da kai ba na tsane ka.”
Saurin damkota yayi, ya toshe mata baki yana hade jikin su waje daya
“Idan kina daga murya wallahi zamu dade a haka, idan ta gano na sato hanya nazo ni dake duk ba zamu fita ba, yanzu ki kwantar da hankalin ki, ki bita duk yadda tace zan dinga shigowa nan din da asubah tunda bata tashi da asubah sai gari yayi haske sosai.”
Fizge kanta tayi tana masa mugun kallo
“Na tsane ka, na tsane ka Bashir har bansan iya adadin tsanar da nayi maka ba, Allah ya isa cutar dani da kayi, kasan dama kana da mata amma shine ka auro ni, wallahi sai ka sake ni ko na jawo maka abinda zaka dade kana dana sani.”
“Baby!” Yaji muryar hajjajun tasa tana k’wala masa kira, jikin sa ne ya hau rawa yayi hanyar fita hankalin sa a tashe,kafin ya karasa ta turo kofar cikin shigar kayan bacci masu shegen kyau, tayi musu wani kallo kafin ta kama hannun sa tana murmushi
“Kana nan ashe, toh wuce muje ko?”
“Toh;” yace yana yin gaba.
“Ke kuma, ki fito ki fara min aiki kafin gari ya gama wayewa, akwai menu na kalolin abincin da nake son gani kullum a saman dining bana kuma so ki wuce karfe goma baki gama komai ba.”
Ta juya tana karkada mata mazaunanta ta buga kofar. Hawayen bakin ciki ne suka sakko mata, ta share tana shiga dan kurkutaccen bandakin da ke gefen dakin ta dauro alwala da k’yar sboda yadda yake wani shegen wari ta shinfid’a dankwalin ta, tayi sallah akai sannan ta bi ta hanyar zuwa kitchen din dan ta tabbata idan har ta sake muguwar matar ta dawo bata fito ba zata iya nada mata shegen duka babu abinda ya dameta gashi babu me kwatar ta dan shi kansa Bashir din ba abakin komai yake ba.
Menu din ta dauka tana kallo, babu abu daya daga cikin kalolin girke-girken guda biyar da ta iya a ciki, tasan dai tabbas Iman tana yi musu dukka a gida amma ita bata taba ko da sha’awar gwadawa ba, daga indomie sai tea sune kadai take yi, sai yar taliya ko macaroni shima ba kullum ba, duk wani girki me wahala kamar su tuwo da sauran su.
*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*
*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*
_SO DA ZUCIYA_
*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI’AR ZUCIYA_
*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_
*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_
*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_
*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k
*_Zaku tura kudin a_*
6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*
*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇
08184017082
*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇
09134848107
GIPHY App Key not set. Please check settings