Advertisement
*HALIN GIRMA*
*_Hafsat Rano_*
*5*
*_Last free page!_*
****
Advertisements
Tana zaune ta idar da sallah, bata tashi daga kan abun sallar ba taji shigowar sa shashen Gajin, gabanta taji ya fadi, tayi kamar bata ji sallamar da yayi ba, tayi tsam a kan sallayar tana kallon gabanta. Da kallo ya bi bayan ta ya samu waje ya zauna a cikin kujerun falon yana kokarin daidaita yanayin da yake ciki. Gajin ce ta fito,
“Wa nake gani kamar Ibrahim?”
“Nine nan wallahi Hajiya.”
“Lale marhabin, barka da zuwa. Saukar yaushe?”
“Dazu na shigo, mun same ku lafiya?”
“Lafiya lou wallahi, yasu Hajiyan da yan uwanka?”
Advertisements
“Kowa lafiya suna gaida ku.”
“Muna amsawa, sannu da zuwa.”
” Yawwa.” Yace yana yawo da idon sa akan ta,
” Iman ba magana?” Yace yana son Gajin ta tanka
“Kaji sokonci, wai bata gaishe ka ba?” Tayi maganar da sauri
“Ina wuni?” Tace a gajarce
” Lafiya lou, kina lafiya?”
Shiru tayi bata amsa ba, Gaji ta hau sababi tana mata fad’a, tashi yayi hannun sa cikin aljihu ya zaro wayar ta
“Gashi na tsince ta a kitchen.”
Ya mik’a mata sannan yayi wa Gajin sallama ya fice yana raya ta yadda zai bulowa Iman din, ya gama gane yanayin ta ba irin nasa bane, shirun ta yayi yawa amma duk da haka shi ba damuwar sa bace, yadda ya shiga zuciyar kowa a gidan nan da hakan zaiyi amfani ya kafa kansa, ba zai wani ja lokaci ba zai gabatarwa Gaji da kansa, baya jin ma zai wuce gobe, zai sai fara tuntubar Yaya Hajara idan yaga ba ta goyi bayansa ba zai yi gaban kansa, iya ka tayi masa fad’a shikenan ya wuce. Be koma shashen ba, sai ya fice daga gidan a kafa yana adana number da ya dauka a wayar ta ta, so yake ya saka number a truecaller yaga ko zai samu wani information akai.
Cikin call log dinta ta shiga ta duba amma bata ga number da aka kirata ba, taji babu dadi dan bata so yaga kamar tana sane ta bayar aka daga wayar tasa. Ko da tafiyar su ba zatayi daya ba, ba zata so yaji a ransa dan yana lacking wani abu bane shiyasa hakan ta faru. Kwantar da kanta tayi a saman hannun kujerar ta rufe idon ta tana tariyo zuwan da yayi wajenta, akwai wani abu me girma a muryar sa sai kuma abu daya da ya tsaya mata shine kamshin turaren da taji yana yi, wanda yayi kama da me tsada ne irin ajin farko, domin Allah ya hore mata kaunar kamshi, shiyasa ta kan yi saurin ganewa. Sai dai akwai irin tuurare yan durin nan da suke da kamshi me dadi har ka kasa tantance su, kila irin su ne, abunda ya kara burgeta dashi kenan, duk da yana cikin yanayin da zaka ce kai tsaye babu, amma be bar kansa a wulakance ba. Juya kanta tayi daya gefen ta dora wayar a saman cinyarta ta cigaba da tunani.
***Kiran sallar magriba ya sashi fita daga sashen nasa zuwa masallaci, achan yayi alwala ya shiga sahun farko sukayi sallar. Bubu na ganin shi yaji dadi sosai. Bayan an idar ya wuce bangaren nasa domin ya jira shi, yana zaune sai gashi ko ya shigo, ya tashi tsaye har sai da ya zauna sannan ya zauna shima a k’asa cikin girmamawa ya sake gaishe shi, ya amsa masa sake yana nazarin sa.
“Muhammadu!” Ya kira sunan sa, gyara zaman sa yayi ya tattara hankalin sa waje daya cikin son ganin be yi wani abu a gaban Bubun ba
“Kana ji na Muhammad?”
“Inaji Bubu.”
“Madallah, Muhammad ka san dai a tsarin gidan nan kana cikin lokacin da ya kamata ace ka ajiye iyalin ka kaima, ka nutsu waje daya a kalla hakan zai taimaka maka wajen cikar kamalarka.”
Kansa a kasa yana jin Bubun yayi ta bayani yana gida kansa cike da gamsuwa,
**A kofar ta tsaya tana kallon takalmin Muhammad din dake zube a wajen, ta samu labarin zuwan sa a wajen Kamal amma bata tsammaci irin wannan ganawar da Maimartaba ba, shiyasa ta kasa hakuri tazo ta nemi iso wajen Maimartaba din wajen sarkin kofa amma sai ya nuna mata ba zai yiwu ba, domin an gargade shi akan barin kowa ya shiga shashen maimartaba din har sai ya kammala ganawar sa da Muhammad din, ranta a matukar bace ta koma sashen ta tana jin wani irin tashin hankali, tana tsoron kar Muhammad din ya amsa tayin mahaifin nasa a wannan zaman da zasuyi.
Safa da Marwa tayi tayi, har wajen sallar isha basu fito ba, tana hangen bangaren ta cikin nata shashen, ta kasa zama tana da yakinin ko menene suke tattaunawa haka me muhimmanci ne sosai.
Tana tsaye jikin window taga fitowar su, fuskar Muhammad din a sake yana takewa mahaifin nasa baya. Tsaki taja ta saki labulen tana juyawa zuwa gefen gadon ta, ta zauna tana sake jan wani tsakin, tsakin haushin Muhammad din da ya zame mata ciwon ido shi da mahaifiyar sa.
“Ranki ya dade, Maimartaba ya aiko yana da bukatar ganin ki bayan ya dawo sallar isha’i.”
Bata amsa ba, sai ma juya fuskar ta da tayi wani sashen tana sake sakin siririn tsaki.
***Bangaren sa ya koma, ya tattaro abunda ya san zai bukata ya fito, sai kuma ya tuna da maganar Maimartaba ta karshe da suka tattauna, yana son ganin sa da safe kafin ya fito fad’a, komawa yayi ba dan yaso ba, ya ajiye komai ya zauna yana kirga lokacin zuwa wayewar gari. Nisan yayi yawan da yake jin kamar yayi loosing idan har ya kyale shi tsawon wannan lokacin.
Wayar sa dake ajiye a gefen sa ta dauki sowwa, ya daga ganin kiran da yake ta jira ne tun dazu,
“Oga na duba maka number din, akwai bayanan sa da komai har da wajen aikin sa, hoton sa da kuma location dinsa a yanxu, na tura maka ta mail sai ka duba.”
“Ok! Thank you, zan neme ka. “
Ya katse kiran ya shiga mail dinsa, ya hau kan message din ya bud’e. Hoton sa ya bud’e yayi zooming sosai, sai kuma ya fita ya karanta information din. Karamin tsaki yaja ya ajiye wayar yana jin a ransa wannan din karamin kwaro ne be kamata ya hana shi walwalar sa ba, abu daya zai masa ya kama shi a hannun sa, sai dai ba zai hakan ba har sai ya je ya tabbatar da zargin sa.
***Anan sashen Gajin ta shirya, ta wuce islamiyya tana tafe tana satar kallon hanyar ko zata ganshi tunda yace mata yana zama ne domin yaga wucewar ta, har ta isa makarantar bata ga ko me kama dashi ba, sai kawai ta share tayi abinda ya kaita. A dawowa ma haka ta sake yi shima bata ga kowa ba, ta dawo gida ta chanja kayan ta kenan aka shigo aka ce tazo inji Muhammad, Hijab ta dora a saman kayan jikinta ta fito. A tsaye yau ma ta hange shi wajen kujerar, ya rataye hannayen sa a bayan sa yana tsaye kyam akan kafafun sa.
“Assalamu alaikum.” Tayi masa sallama tana jan kujerar.
“Sannu da zuwa, nan akwai rana bari na saka maka a chan.” Taja kujerar zuwa k’asan wata yar bishiya ta ajiye,
” Bismillah.” Tace masa tana nuna masa kujerar, be zauna ba, ya zaro hannun sa daga bayan sa, ya dawo dasu gaba ya rungume su a kirjin sa,
” Bismillah.” Ya nuna mata kujerar da baki
” Zauna babu matsala.” Yace mata
” A ah dan Allah ka zauna, be kamata na zauna kana tsaye ba, ance bakon ka…”
” Kyale fadar hausawan nan, zauna dan Allah.”
Allah da taji ya ambata yasa ta zauna a kunyace, ya zura mata ido har sai da ta dan ji wani iri.
” Na cika kallo ko? Kiyi hakuri.” Yace mata yana murmushi,kallon ta kadai yayi jin sa yake kamar yafi kowa sa’a a duniya
” Ba komai.” Tace tana gyara wayar hannun ta
” Ina wuni?” Ta gaishe shi yana dan zamowa
” Lafiya lou, sai kika jini shiru, tafiya nayi zuwa kauye Baba ya kira ni, naso ma na zo kafin na wuce toh tafiyar ce tazo a gaggauce, sauka ta kenan ma.”
” Allah sarki… Allah yasa lafiya.”
” Lafiya lou, sai godiya. “
” Ka baro su lafiya?”
” Alhamdulillah. Nagode da kulawa.”
” Ba komai.” Tace tana wasa da hannun ta.
Turo gate din akayi, Habeeb na gaba yana bin sa a baya, wani irin daukewa yaji ganin sa na neman yi. Iman zaune tare da wani suna hira, a cikin gidan kuma? Be san sanda ya isa wajen ba, sai ganin mutum sukayi a gaban su.
Wani kallo Moh yayi masa, yayi murmushi yana taune gefen lips dinsa na kasa
“Yaya sannu da zuwa.” Yace yana mika masa hannu, kin bashi hannu Khalil yayi, sai Habeeb ne suka gaisa, ya daki kafadar Khalil din
” Muje ko?”
” Yi gaba ina zuwa.” Yace masa,
“Ok.” Ya wuce ya bar Khalil din a tsaye
” Iman shiga gida.” Yace a gadarance, ta dago ta kalle shi da sauri, ya hade girar sama data k’asa tamau irin ba wasa din nan.
“My heart, ki shiga gida ki huta dama naji ba zan iya zuwa gida ban zo na ganki ba, shiyasa na taho nan kai tsaye, zan kira ki anjima ki ajiye waya a kusa dake kinji?”
Kunya ce ta kamata ta noke, ta mike da k’yar tace
“Ka gaida gida.” Sannan ta wuce ciki, tana barin wajen ya hade fuskar sa sosai.
” Da tsakar ranar nan ka taso yarinya, kazo zaka ishe ta da uban surutu, ku dama talakawa haka kuke, da kunga yar hanya sai kuzo kuce kuna so, kai kanka kasan ba sa’ar ka bace, ba sa’ar auren ka bace shishigi dai, toh ita din matata ce, ni zan aureta an gama magana, sai kaja tsumman kafafunka a koma in da aka fito, ka samu daidai da kai.”
” Zaka ga tasirin talaka da talauci kuwa, baka da ikon tsarawa kowa rayuwa, haka arziki ba wani abu bane face fitina, wadatar zuciya itace mutum…” Ya dan matso gaban sa
” Mark my word, a gaban idon ka, right under your noses, talaka zai baka mamaki, mamakiin da har ka kare rayuwar ka zaka fita daga cikin sa ba, count down dinka ya fara daga yanzu.”
” 1,2,3!” Sai na jika.
Ya juya ya fice daga gidan cikin takun da ya tsayawa Khalil a rai, cikin wani irin yanayi yayi cikin gidan yana jin yanzu ba sai anjima ba, zai yi abinda ya dace, gida be koshi ba, babu yadda za’a yi a bawa dawa.
**A tsaye ya tarar da Habib yana ganin shi yace
“Kaiko me ka tsaya yi ina ta jiran ka.”
“Abinda ka kasa yi, kana ganin kanwar ka da mutum a tsaye, kana ganin sa kaga mara gaskiya, wa ya sani ma ko dan boko haram ne da wannan uban kasumbar, amma baka damu ba kayi tafiyar ka, hakan ba daidai bane.”
Kallon sa Habib yayi, mamaki na kamashi,
” Yaushe hakan ya zama ba daidai ba khalil?”
” Habib, maganar gaskiya ina son Iman, son da ni kaina bansan adadin sa ba, zan iya komai akan na sameta, dan haka ba zan iya jure ganin ta da kowa ba, musamman mutum irin wannan da ya nuna alamun rashin gaskiya, gashi fakiri jibi shigar jikin sa, no ba zan iya ba, rakani wajen Gaji ayita ta kare.”
” Idan har kai din jinina ne, idan har na isa da kai babu kai babu Iman Khalil, na rasa kafiya irin taka, na rasa dagiya irin taka, bayan maganar nan mun dade da gama ta, na gaya maka ba zai taba yiwuwa ba.”
” Akan me? Dan Allah Anty ki gaya min hujja me karfi a musulunci da ya haramta min auren ta, na daya ni ba muharraminta bane tunda ita din ba ke kika haife ta ba, toh sai menene? Akan dalili mara tushe?”
” Akan duk abinda zaka kira shi Khalil ka kirashi, amma idan har ina numfashi ba zamu hada jini ba wallahi, ga mata nan bila adadin, me yasa sai ita, wannan da yazo shi ya dace da ita, shine daidai da matsayin ta, inaso auren da zatayi ya zama sakayyar aure min miji da uwarta tayi, ta saka yayana samun yan Uba!.”
” Ohh shit! Kin kasa fuskanta ta Anty, kiyi hakuri wannan karon zabin raina zan bi, zanje na samu Gaji na sanar da ita, gwara kowa ya sani a san me yakamata ayi.”
” Khalil!”
Ta k’wala masa kira, ya juya da sauri yayi hanyar fita, wayar sa tayi kara, ya tsaya chak jin layin da yake ajiye numbers din manyan mutanen sa ne, ciro wayar yayi sunan Sir ya bayyana a wayar, ya daga da sauri yana daidaita numfashin sa
” Kana ji Ibrahim? Sako ne daga sama ba daga ni bane, an dakatar da kai aiki zuwa wani lokaci, za’a neme ka idan bukatar hakan ta taso.” Be jira yace komai ba , ya katse kiran. Da sauri ya dafe bangon da yake kusa dan ji yayi jiri na neman kadashi, gaba daya rayuwar sa akan aikin ta dogara, yana da passion sosai a Kai sannan yana iyakar kokarin sa wajen aikin sa, maganar promotion dinsa ma ake idan har ya kammala wannan assignment din da ya kawo shi Kano, shikenan sai dakatarwa haka nan ba wani dalili?
” Ya akayi?! Habib ya matso ya taba shi ganin kamar ya shiga coma
🔥🔥🔥🔥🔥
*_LAST BONANZA_*
*_farincinku shine namu,ZAFAFAN DAI,sun sake amsa kokenku,sun sake rage muku kaso 20 cikin 100_*
*_Daga yau 29 ga wata,har zuwa 31 ga watan nan,xaku iya biyan 800 a amadadin 1000 na kudin litattafai biyar_*
*_za’a fara posting in sha Allah 1st January da yardar Allah_*
*HANZARTA KI BIYA NAKI KAFIN RANAKUN SU QARE*
*XAKI BIYA TA WANNAN ACCOUNT NUMBER DIN*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
SAIKU TURA SHAIDAR BIYA
08184017082
GA MASU TURA KATIN WAYA KO KUMA VTU,SAIKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYANKU
09134848107
GIPHY App Key not set. Please check settings