HALIN GIRMA 8

Advertisement

 *HALIN GIRMA*

            8

*Zafafa biyar na kudi ne, idan kina so ki karanta ki tuntubi 08184017082 or 09134848107* 

***

Sake kiranta yayi a karo na biyu, ta daga tana goge ruwan da yake hannun ta, tana ciki tana wankewa Gaji toilet shi yasa bataji kiran farko ba, sai da ta fito wanda yayi daidai da sake kiran.

Advertisements

“Assalamu alaikum.” Tayi sallama cikin muryar da ta saka Moh sallama duk bacin ran Khalil da ya kwasa yanzu.

“Wa alaikisalam, kina lafiya?”

“Lafiya lou wallahi, ya aiki?”

“Alhamdulillah, ina waje nazo ganin Abba.”

“Owk tam gani nan.”

Tace sannan ta ajiye wayar, ta fito tana tunanin yadda zata sanar wa Abban, a harabar gidan ta hangi motar sa, alamun ya dawo kenan, karasawa tayi wajen su tun kan ta isa Moh yake sake admiring kyawun ta, koman ta very simple hatta da tafiyar ta kamar ba zata taka k’asa ba, a matukar nutse take komai hakan yake sake dulmiyashi a kogin soyayyar ta.

Advertisements

   Taba shi Musaddik yayi, ya dan yi firgigit sannan ya saki murmushi

“Allah zaka bada maza, kamar ba soja ba?” Yayi whispering maganar yadda Moh din ne kawai zaiji, banza yayi masa ya rigata karasowa wajen suka hadu a hanya. Kamshin turaren sa me dadi ya rigashi karasawa

“Sannu da zuwa.” Tace tana shakar kamshin da ta kasa tantance shi

“Yawwa Dear, kina lafiya?”

“Alhamdulillah, lafiya lou.”

“Masha ALLAH, gani nazo neman izini wajen Abban mu, ina fatan ban makara ba.”

Girgiza masa kai tayi

” Masha ALLAH, yanzu ya za’a yi, shige mana gaba zakiyi muje ko?”

Da sauri ta kalle shi, idanun ta suka haska cikin nasa sai a lokacin taga ya rage kasumbar fuskar sa sosai kamar ya aske, fuskar sa ta fito sosai idanun sa da suka fi kama da a lumshe suke sun fito sosai, saurin dauke kanta tayi tana jin wani irin faduwar gaba

” Tunda ba zaka yi introducing dina ba, bari nayi da kaina.” Musaddik da ya karaso wajen ya harare shi yana murmushi

” Sannu malama Fatima, sunana Musaddik kuma ni ogan sa ne a komai, ina fatan zaki karbi aboki na hannu bibbiyu dan da gaske yake ba da wasa ba.”

” Sannu da zuwa,  Ina wuni?” Ta gaishe shi tana sauke kanta kasa har yanzu bata daina jin faduwar gaban ba

” Lafiya lou, ya komai da komai?”

” Alhamdulillah.” Tace

” Bari na duba Marwan sai yazo ya yi wa Abban magana.”

” Owk.” 

Ta juya zuwa part din su tana addu’ar kar su hadu da khalil, a falo ta tarar da su dukka Zeenat na danna wayarta, Maama na zaune Marwan yayi filo da kafarta yana kallon Disney World, shigowar ta ya saka suka maido hankalin su kanta

” Sannu da gida Mama.” 

Kin amsawa tayi, ta gimtse fuskar ta ta muskuta tana cigaba da kallon TV.

” Mama dama Muhammad ne yazo wajen Abban.”

Da sauri Zeenat ta mike, ta hau kyalkyala dariya kamar wata sabuwar tababbiya, kawai sai Maman ma ta hau tayata, suka sakata a gaba da dariya abinda ya bata mata rai har taji kuka na neman xuwar mata

” Su Malam ne anzo za’a Abba kenan, ya kyauta miki ai ya taimaka da yazo, dan Khalil yafi karfin ki, shi din dai shine daidai da me bakin hali irin naki, me kike so nayi yanzu.”

Daidaita muryar ta tayi, tace

“Dama so nake Marwan yayi musu iso wajen …” Da sauri ta katse numfashin ta

“Tashi maza maza Marwan, je kace wa Abban gidan su Aliyu yana da baki, yi masa kar ya gaji da jira yace ya fasa.” 

Sai ta sake tuntsurewa da dariya Zeenat na tayata. Hawayen da take ta rikewa ne suka shiga sakkowa a fuskar ta, 

“Kadan kenan kika gani in dai junan mutum bakin ciki toh wallahi shine a ciki.” Zeenat tace tana jan tsaki. Juyawa tayi zata fita Maman ta tsaida ta

“Zo ki wuce ki wanke kanukan da aka bata.”

Bata ce komai ba, tayi hanyar kitchen din zuciyar ta na kunci sosai. Wanke wanken take tana kuka sosai, irin wand a ta jima batayi ba, tana da masifar dauriya akan duk abinda za’a yi mata, amma kuma a wannan bangaren ta rasa me yasa ta kasa jurewa, wulakanci bashi da dadi kuma yanaa da ciwo musamman a tasaka gaba ana dariyar shakiyan ci da wulakanci.

   Adadin lokacin da ta saba dauka tana wanke wanken sai data ninka shi saboda damuwar da take ciki. Ta baya ta fice ta koma bangaren Gaji tana jin kamar ta tattara komai ta bar musu gidan. Sau daya a cikin ranaku masu yawa yau ta tuna mahaifiyar ta, shiyasa bahaushe yace wanda ya rasa uwa yayi kuka.

***Da kallo Abba ya bisu har suka zauna suna masu nuna jin nauyi da kunyar sa. Bayan sun gaisa yace

“Gashi kuma ban shaida ku ba.”

“Dama Fatima ce ta sanar mishi da Abban yace yazo ya nemi izini a wajenka, toh shine dama dalilin zuwan namu.” Musaddik yayi maganar yana addu’ar Allah yasa be kwafsa ba.

“Toh toh…” Abban yace yana tunanin yadda al’amarin yake, musamman maganar Khalil da ya riga ya karbe ta 

“Ita Ummin ce tace kuzo ko?” Yayi tambayar yana kallon su

” Ummi?” Suka Hada baki

” Auw Fatima toh, sunan Uwata ne ni ummi nake kiran ta.”

“Masha ALLAH, Eh Itace ta turo mu.”

“Toh shikenan, ina zuwa.”

Tashi yayi ya shiga ciki, ya kira wayan Abban su Fatiman dan yasan be kai ga dawowa gidan ba 

“Yaya barka da warhaka.”

“Barka dai, ya aiki?” 

“Alhamdulillah mun gode Allah.”

“Allah ya bada sa’a, kana ji, dama akan maganar Ummi ne, yaron nan Ibrahim yazo da maganar sa jiya har ma na bashi izinin daidaitawa da ita ganin shi din na gida ne, yau kuma kwatsam sai ga wani yazo shi kuma wai Ummin ce ta turo shi.”

” Ibrahim Kuma?

“Eh shifa.”

“Amma da kaina na tuntubi Hajara da maganar sa, amma ta nuna min sam ba da gaske yake ba, hakan ya saka na ce Ummin ta sanar wa wannan din yazo ya ganka.”

“Ibrahim kam yazo jiya ya same ni, ga wannan kuma shima.”

“Allah ya kyauta.”

“Zamu duba muyi bincike, idan yaso sai a bashi dama shima, wanda suka daidaita shikenan, bamu san me Allah ya boye ba, kar muyi gagagwa.”

“Shikenan Yaya, duk yadda akayi yayi.”

“Madallah.”

Fitowa yayi ya tarar dasu a zaune, ya zauna yana fuskantar su

“Kace sunan ka?”

“Muhammad.”

“Toh Muhammad daga ina?”

“Adamawa-Yola, amma mahaifiya ta yar Kano ce, nima kuma kaso me yawa na rayuwa ta nayi shi ne a Kanon.”

“Toh toh Masha ALLAH, Anyi karatu Muhammad?”

“Eh Abba, nayi karatu.”

” Aiki fa?”

” Soja ne ni.”

” Ah Masha ALLAH, soja ga wuta ga yaki, soja marmari daga nesa. Hakan yayi kyau a cigaba da samar mana da tsaro a k’asar mu, Allah ya yaye mana abubuwan da suke damun mu suka hanamu zaman lafiya a k’asar, Allah kuma ya cigaba da dafa muku.”

” Amin.” Suka amsa cikin jin dadin yadda Abban ya sake dasu

” Shikenan Muhammad, ka bani number wayar ka da address din ka, zan neme ka in sha Allah.”

Hannu Musaddik yasa a aljihun sa zai ciro wallet dinsa ya dauko complimentary card din Moh din yayi sauri fara karantowa Abba number, yace kuma zai masa text message na address din in sha Allah. Godiya sukayi masa suka fito yana jin tsoro na shigar sa, tsoron kar Abban yayi rejecting dinsa, tsoron yadda zai yi komai ya tafi yadda yake so.

  Kiranta ya sake yi ta fito bayan ta wanke fuskar ta sosai dan kar ya gane, duk da haka sai da ya gane kuwa,ya kafe ta da ido yana jin babu dadi.

“Me ya samu idon ki?” Ya tambaye ta dan ba zai iya hakuri ba,

“Ba komai.”

“Ban yarda ba, kalli idon ki, Dan Allah ki fad’a min me ya faru?”

“Abu ne ya fad’a mina idon dazu, amma ya fita ma.”

“Ban yarda ba, ki fad’a min waya bata miki rai? Waye ya saka ki zubar da hawayenki masu tsada?”

Ji tayi kukan na sake taso mata, dan dama idan kana cikin halin kuka aka matsa maka da tambaya ko ana so ka maida zance sai kaji sabon kuka ya taho maka,

“Ba komai da gaske ba komai.”

“Dan Allah ki fad’a min menene?”

“Mamana na tuna.” Ta fad’a masa saboda kawai ya kyale ta da tambayar

“Kiyi hakuri, akwai abubuwa da yawa da nake son sani, I ll call you idan na koma, ki daina kuka kinji? Komai zai wuce in sha Allah.”

“In Sha Allah.” Tace tana daidaita kanta.

“Kinyi alkawari kin daina kukan ko?”

“Nayi.”

“Nagode, zan kiraki.”

“Shkenan ka gaida gida.”. Juyawa tayi ta koma ciki shi kuma ya fita ya tarar da Musaddik ya cika yayi fam kamar zai fashe.

“Muje ko?”

“Allah iyakata wajen bishiyar chan, ka kirasu suzo su dauke mu wahalar tayi yawa ai.”

“Naji muji toh.” 

Ya ciro wayar sa ya kirasu cikin kankanin lokaci suka karaso, har suka isa babu wata magana tsakani Musaddik ya sauka su kuma suka wuce.

  A gaggauce ya gama komai ya shirya cikin kayan sa masu kauri, ya zauna yana jawo wayar sa, kafin ya kirata ya samu kiran DG, yayi saurin dagawa yana karawa a kunne. Gaisuwa sukayi ya bukaci ganin sa a Abuja idan an shiga working days, da toh ya amsa masa sukayi sallama ya juya akalar kiran zuwa number Ammin sa. 

“Ammi na barka da dare.”

Yace sanda ta daga wayar

“Barka dai yarona, kana lafiya?”

“Lafiya lou Ammi, ya gida da kowa da kowa.”

“Kowa lafiya, ya aikin naka?”

“Alhamdulillah Ammi, babu dadi gashi ina missing dinki sosai.”

“Ban yarda da wannan zancen naka ba, idan da gaske ne ai kasan in da nake.”

” Ina na zuwa ai, ranar ma wani aikin ne ya taso urgent shiyasa na tafi.”

” Ku kenan aiki, Allah ya taimaka ya bada sa’a.”

” Amin Ammi, naje naga Takawa ai, har munyi magana ma akan maganar da Bubu yayi min.”

” Eh naji kuwa suna waya jiya, sai dai bamu zauna munyi maganar ba, me yace maka?”

” Akan yarinyar ne dama Ammi, mahaifin ta yace nazo na ga wanshi ya bani izinin zuwa wajenta.”

” Ina jinka.”

” Toh nayi magana da Takawa akan idan har zuwa gidan su ya taso ba sai kowa yaje daga royal family ba, a samu wasu cikin mutanen Takawa din da ya aminta dasu suje neman auren.”

” A wanne dalilin kenan? Ina ka taba jin anyi irin wannan shirmen Muhammad? Idan ma anyi hakan an fad’a maka ba zasuyi bincike akanka ba kafin su baka izinin ganin yarsu ba? Ai dole ne iyaye na kwarai su yi bincike sosai su san wa zasu bawa yarsu.”

” Nafi son duk wannan yazo daga baya Ammi, dama dole su sani amma ba yanzu ba, marikiyar yarinyar ce matsala, idan har taji da wuri zata iya bata abun dan ta jima tana bata wa.”

” Idan hakan ne matsala, toh ka bar komai a waje na, karka manta wanne gida kake magana Muhammad, wargi ma ance waje yake samu, bata isa tayi komai ba idan har taji kai din waye, gaba da gabanta fa, ka daina tunanin komai kayi addu’a, har naji inason yarinyar da dukkan zuciya ta, Allah ya sa ta zama abokiyar arzikin ka.”

” Amin Ammi, in sha Allah ma ba zata sani ba har sai ranar, zanyi duk yadda zanyi bata sani din ba, yadda abin zai dake ta, kuma nayi alkawarin hukunta ta daidai da abinda tayi.”

” Ya sunan diyar tawa?”

“Fatima sunan ta, Iman.”

” Masha ALLAH, Allah ya tabbatar mana da alkhairi.”

” Amin.”

” Inyeee, lallai babu kunya Babana? Hadda saurin amsawa ko?”

Dariya ya saka sosai,yayi saurin kashe wayar jin Ammin zata yi masa dan biki.

   

Rik’e wayar ya cigaba da yi a hannu yana juyata,maimakon ya kirata sai wata dabara ta fado masa, take yaji wani dadi ya kamashi ganin ya samu hanyar da zai hana Maman sanin komai har sai lokaci ya kure mata. 

   Kwanciya yayi ya ja blanket har saman kansa, sannan ya kirata yana jin ringing din na tafiya daidai bugun zuciyar sa.

***Da safe ya so ya makara bayan ya koma bacci da asubah, kiran Musaddik ya tuna masa abinda suka shirya, a gaggauce ya tashi ya shirya, ya kimtsa kansa cikin shigar Khakin sa, ya fito a sojan sa, kayan sun yi masifar karbar sa, yanayi da tsarin zubin halittar sa sunyi daidai da kayan, shi kansa yana jin sa ontop a duk lokacin da ya samu kansa cikin irin shigar kayan. 

   A hannu ya rik’e wular ya fito suna ganin shi suka taso da sauri, duk suka k’ame su biyun kafin daya ya bud’e masa motar daya kuma ya zagaya mazaunin driver ya tada motar suka fice daga gidan.

   A chan permanent site din sukayi zasu hadu da Musaddik, yana isa yaga motar sa a waje, be shiga ba ya kirashi a waya ya fito ya same shi. Tare suka fito da Ja’afar, Musaddik ya zura kansa cikin motar yana kallon sa.

“Ya riga yazo, yana reception yana jiran MD ya hada shi da oga at the top”

“Ga kuma Oga kwata-kwata anan ba.” Ya kalli Ja’afar suka kwashe da dariya

” Me ka shirya masa Oga?

” Ni na isa Captain? Ai ban isa ba Wallahi. Duk abinda ka shirya min dai, ni ai bani da say.”

” Ya akayi be gane ka Musaddik bane wai?”

” Ba zai gane ba ai, I’m not in charge of staff din wajen, wannan aikin admin human resources ne, plus kaga chan sabon branch ne nan kuma main site.”

” Haka ne kuma, yanzu zan jira anan.”

” Yes Sir!” Ya Sara masa suka kwashe da dariya

Khalil na zaune cikin zulumi yana fatan haduwar da zasuyi da shugaban wajen ya zama alkhairi, yana so ya dawo da aikinsa as soon as possible yadda zaifi jin dadin kwace Iman da karfin ikon sa, da yan kudaden sa a aljihu. Fitowar MD ya saka shi tashi da sauri

” Yawwa Ibrahim, yazo yana parking lot, sai kaje ka same shi, best of luck.”

” Nagode sir, Allah ya kara girma.”

” Amin.” 

Saurin fita yayi, ya tarar da motoci biyu a wajen, duk da bakin glass, tunanin wacce a ciki ya bi numbers din motar da kallo. _Royalty_ aka rubuta a jikin plate din babbar da tafi kyau da sheki, wajen ya nufa kirjin sa na dukan tara tara, kafin ya karasa yaga murfin bayan motar ya bud’e, anyi masa fitala. Kofar ya nufa ya zura jikin sa bakin sa dauke da sallama, sai da ya zauna ya daidaita a ciki, kofar ta rufe ruf ya shaki kamshin motar me dadin gaske, ya juyo sukayi ido hudu da wanda ko a mafarki be taba hasashe ko tunanin gani ba.

“Hello Ibrahim.”

Moh yace yana sakar masa wani irin murmushi me dauke da ma’anoni masu yawan gaske 

“Me… Me ban gane ba?” Ya hau k’inkina ya ma kasa daidaita maganar sa.

“Sunana Muhammad Ahmad Santuraki, Also known as Captain Moh, shugaban wajen nan gaba daya, nice to meet you.”

” Nooo! Impossible! This most be a joke, Kai din? Kai din? Kai… Kai Kai din?”

” Calm down and take a deep breath, karka hargitsa kanka dan akwai sauran surprises, na farko karka taba wulakanta mutum baka san shi din waye ba.”

” Innalillah wa inna ilaihi rajiun.”

Ya shiga maimaitawa ba kakkautawa, gaban motar ya kalla yaga sojoji ne su biyu majiya karfin gaske, kowannen su fuskar sa murtuke take babu alamun dariya, jiran umarni kawai suke kamar mayunwatan zakuna, hadiye wani mugun yawo yayi yana jin sanda Muhammad din ya bada umarnin tada motar ,be iya bud’e baki ya hanashi ba, yana jin sanda motar ta soma tafiya a hankali har ta daidaita akan babban titi, kafin me tuka motar ya kara taka motar da gudun gaske

“Shikenan na gama yawo.” Ya furta a zuciyar sa be san maganar ta fito fili ba.

Murmushi Muhammad yayi ya taune gefen lips dinsa yana ayyana kalar rashin m din da zai masa.

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like

HALIN GIRMA 18

Advertisement  Halin Girma     18 Hafsat Rano *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* Advertisements…