Advertisement
Halin Girma
9
*Zafafa biyar na kudi ne, idan kina so ki karanta ki tuntubi 08184017082 or 09134848107*
I’m on Instagram as @zafafabiyar5. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1ft46u5twk6r3&utm_content=nj79azb
Advertisements
***
Yana jin sanda motar ta tsaya, ya juyo da sauri ya kalle shi, hankalin sa na kan wayar sa yana dannawa, fuskar sa a hade tsaf babu alamun wasa ko kadan, tsoro ne ya sake shigar Khalil din sosai, yaji kamar yayi ta kurma ihu yana neman taimako, amma kuma ya san babu wanda zai taimaka masa musamman idan aka zo aka ga wanda yake tare dasu.
Ji yayi an murda handle din bangaren sa, yayi saurin matsowa sai gashi a tsakiyar motar, daf da Moh, wani banzan kallo ya watsa masa da ya sakashi saurin komawa inda yake zaune.
“Come ou!” Wani murdadden soja yace matsa bayan kofar ta gama budewa, idanu ya soma rabawa tsakanin Moh da sojan fuskar sa ta nuna matukar tashin hankalin da ya shiga
“I said come out!” Ya daka masa tsawa da ta saka shi saurin fitowa
“Dan Allah Oga kayi hakuri, wallahi sharrin shaidan ne da rashin hankali, duk abinda na farfada ba wai har zuciya ta bane wallahi.”
Ya hau magiya yana kallon Moh da yayi kamar baya wajen, damtsen hannun sa sojan ya kama ya shiga jan sa har zuwa wata kofa in da ya hangi sojoji sun fi su ashirin suna tsalle tsalle a wajen.
Advertisements
“Oga dan Allah ka bawa oganku hakuri Dan Allah!”
“Kasan waye oga kuwa?”
Da sauri ya girgiza kansa
“Ban sani ba wallahi, rashin sani ya jawo nayi masa abinda nayi amsa amma dan Allah na tuba yayi hakuri.”
Dariya sojan ya saka sosai
” Baka da hankali amma, ka zo har nan wajen kayi tunanin zamu kyale ka, ka tafi free? Nah sai mun dan sassamaka yadda gobe ba zaka kara ba. “
” Dan Allah nace fa? Ka tayani bawa ogan hakuri. “
” Naka wasa ne. “
Yayi gaba yana rik’e dashi, yanayin rikon da yayi masa da yanayin jikin Khalil din zai baka dariya sosai, dama bashi da wani jiki sosai gashi kuma a hannun manyan maza, wani daki ya kaishi sannan ya sake shi yana masa dariyar mugunta
“Zaka kwashi kashin ka hannu yau, wallahi Oga zai iya sawa a batar da kai a k’asar nan, kasan waye kuwa? Tab.”
Jawo masa kofar yayi ya rufe ta har da key yana kwasar dariya.
Chan karshen dakin yaje ya tsugunna yana jin dana sanin barin zancen da yayi, dama a maida baya da ya goge duk abun da yace ma Muhammad din cikin rashin sani. Ji yayi cikin sa na kara alamar ya lalace, ya tabbatar bala’in tsoro da firgicin da ya shiga ne ya saka cikin nasa lalacewa. Mikewa yayi da sauri ya hau zagaye a dakin yana maimaita
“Innalillah wa inna ilaihi rajiun.”
Ji yayi ana murda key din dakin, ya tsaya yana kallon kofar cikin tsoro. Captain Moh ne ya shigo sojoji biyu na biye dashi a bayan sa, daya rik’e da kujera yazo ya ajiye masa ya zauna yana wa Khalil murmush
“Alhaji Khalil barka da warhaka.”
“Dan Allah dan Allah kayi hakuri, wallahi sharrin shaidan ne da yarinta wallahi amma ba zan sake ba.”
“Haba Khalil, so soon haka? Ka sani ko sojan gona ne ni, kasan fa talaka da samun wuri.”
“Wallahi ni dai ba zan sake ba, kayi min rai, mahaifiyta da ni ta dogara, dan Allah.”
“Calm down magana zamuyi, ka nutsu ka saurare ni, warning ne me hade da dokoki, ina fatan zaka bud’e kunnuwan ka kaji ni sosai.”
“Ina ji wallahi.”
“Babu kai babu abinda ya zama mallaki na, Ina nufin Fatima, ko a hanya ka hadu karka taba nuna ka santa balle har magana ta hada ku, a da nayi niyyar barka ka gwada sa’ar ka akanta, amma kuma a yanzu na gama yanke wa, baka kai na nemi abu tare da kai ba, dan haka ko son ta zai kashe ka sai dai ka hakura… “
” Na biyu, a yau ba sai gobe ba zaka wuce in da ka fito, ba tare da ka bud’e bakin ka kace wa kowa komai ba, ina nufin, bakin ka ya zama kanin kafar ka, kar naji zancen a wajen kowa ciki har da ita yayarta ka da bata tsoron Allah. “
” Last but not the list ka koma bakin aikin ka, ka rik’e mutuncin ka sannan bakai ba wulakanta kowa. “
” Duk abinda ka fad’a wallahi zanyi, nayi alkawari, ni dai kar ka raba ni da mahaifiyata wallahi bata da kowa sai ni. “
” I’m done with you, gashi nan take him back, ku tabbatar ya bar Kano kafin karfe shida na yamma. “
Juyawa yayi cikin wani irin taku ya fice daga wajen, yana fita sukayi kansa
” Ai wallahi ba zaka shigo nan a banza ka fita bamu ci ladan ka ba. “
Wani soja yace yana kai masa rankwashi.
” Tashi kayi frog jump. ” Dayan ya daka masa tsawa yana zaro belt dinsa. Da sauri ya hau yi yana hada zufa su kuma suna tuntsura dariya, sai da suka gajiyar dashi sosai sannan suka fito dashi suka sashi a mota suka maidashi har kofar gidan suka ajiye sannan suka tafi.
***Abba na zaune yaji text message ya shigo wayar sa, tunanin sa ma ko alert ne ya bud’e sai yaga sako daga bakuwar number da be sani ba, bud’e message din yayi ya soma karantawa
_” Dr. barka da warhaka, ya aiki? Allah ya taimaka. Dama wata magana nake son yi akan fatima, ina rokon alfarmar daka saka ido sosai akan abinda yake faruwa a cikin gidan, in sha Allah zaka gano wani abu da ya dade yana faruwa ba tare da sanin ka ba. Sai anjima a huta lafiya. “_
maimaita karanta sakon ya dinga yi yana kokarin daidaita tunanin sa waje guda, waye ko wace wannan? Me sakon yake nufi? Me ya faru da Fatima din? Duk wadannan tambayoyin ne suka shiga yi masa yawo aka, be san me yasa ba, kawai sai yaji hankalin sa ya kasa kwanciya da abinda ya karanta. Tashi yayi ya fito zuwa falon gidan, ya k’wala kiran Iman din. Zeenat ce ta fito
” Ina Ummi? “
” Ina ga tana wajen Gaji. “
” Je ki kira min ita. “
Fita tayi shi kuma ya cigaba da tsaiwa awajen har suka shigo a tare.
” Ki same ni a daki na. ” Yace yana juyawa tabi bayanshi, dariyar mugunta Zeenat tayi a tunanin ta wani laifin Iman din tayi dan sosai yanayin Abban ya nuna bacin rai.
A gefen gadon sa ya zauna, ta samu chan gefe daga kasa ta rakube tana tunanin dalilin kiran.
” Kina jina Uwata? Kina da wata matsala wacce ban sani ba? “
Girgiza kanta tayi
” A ah Abba babu. “
” Kalle ni nan, ni ne mahaifin ki, baki da wanda yafi ni bayan mahaifiyar ki, ki fad’a min gaskiya idan akwai wani abu da yake damunki.”
Zuciyar ta ce tayi rauni, taji kuka na taho mata, ta k’asa rike shi kawai ta fashe da kuka. Dafe kansa Abban yayi, ya shiga tunanin me yake faruwa? Wanne irin abu ne haka da har shi ya kasa ganewa?
“Fatima…” Ya kira ainihin sunan ta a karo na farko a rayuwar ta
“Na’am.” Ta amsa cikin muryar kuka
“Kowanne bawa da irin yadda rayuwa take zuwar masa, kiyi hakuri zanyi bincike, sannan akwai shiri da nake yi na kaiki wajen mahaifiyar ki da zarar maganar bikin ku ta tabbata, nayi mata alkawarin kai mata ke da zarar lokacin auren ki yayi, mahaifiyar ki na son ki fiye da yadda take son kanta, ki rik’e wannan.”
” Tashi kije kinji, ki daina kukan haka.”
Tashi tayi bayan tace
” Nagode Abba.” Ta fice ya bita da kallo yana jin kamar be kyauta mata ba.
Dakin su ta wuce ta tarar da Zeenat na waya har da shewa, juyawa tayi zuwa store ta zauna a gefen katifar ta, tayi kuka sosai har sai da taji babu abinda yayi saura a zuciyar ta. Tsawon lokaci ta sauka a ciki har sai da taji maganar Mama tana fad’a a waya anan ta gane ta dawo dan dazu bata gidan. Tashi tayi ta fice ta kofar baya bayan ta gyara fuskar ta a sink din kitchen.
***Zama Mama tayi tana sababi akan tafiyar Khalil din babu sanarwa, sai dai a k’asan zuciyar ta taji dadin hakan domin a kalla hankalin sa zai dauke daga kan Iman din har a gama magana da shi dayan da yazo. Abba ne ya shigo ya sameta tana zaune , ya zauna a gefenta sai tasha jinin jikin ta musamman da ta gama sanin halin sa tsaf.
“Me yasa kika ce min Ibrahim ba da gaske yake akan maganar Ummi ba, sannan shi kuma yaje ya samu Yaya da maganar.”
Yadda ta zabura yaso bawa Abban mamaki.
“Khalil din ne yaje wajen Yaya? Yaushe akayi haka? Me yayan yace masa?”
“Duk ba wannan na tambaye ki ba, baki bani amsa ta ba.”
“Toh toh ai gani nayi shi Khalil ba yanzu zai yi aure ba, su kuma yaran nan yanzu ne muke so mu aurar dasu, bana so Zeenat ta tafi da bar Iman tunda kaga tare suke komai, shiyasa nace gwara wanda ya shirya.”
“Haka ne kuma.” Yace yana mata wani irin kallo da ya sakata tunani sosai
“Toh hakan yayi ai, Ina fatan dai zeenatu ta sallami yaron nan Bashir ko? Dan ina nan akan bakana ba zan bashi ba.”
“Dan Allah Dr ka bar wannan maganar, tunda tana son shi kayi hakuri kawai ayi tunda an wuce zamanin da za’a yi wa yara auren dole.”
Girgiza mata kai yayi yana dakatar da ita
“Wannan maganar taki shirme ce, musulunci mu ya bawa damar zaba wa yayanmu mazaje na gari, dan haka ban yarda da Bashir ba, idan akwai wani ta kawo shi.”
Ya tashi ya fice ransa na baci da yadda maganar Bashir din taki karewa, sam Hajara bata shirya gane abunda yake hango musu ba, eh hango musu tunda duk in da aka je aka jawo ita uwa sai tafi cutuwa da abinda zai samu yarta.
***Text message biyu ya tura a lokaci daya, address din sa da Abba yace ya tura masa ta message sai kuma message din da yayi wa Abban Iman din, wanda yake ganin shine kadai hanyar da zai bi wajen hana Maman sanin duk wani abu akan Iman din, ya tabbata daga lokacin Abban zai saka ido sosai, ba kuma za’a dau lokaci ba zai gano komai, shi kuma sai yayi amfani da wannan damar ya nemi alfarmar barin komai ya zama sirri a tsakanin su iyaye maza, domin dama su iyaye maza baa sansu da ratatin zance ba, ba kasafai ma suke zama suyi ta magana anyhow ba, ya tabbata idan har hakan ta yiwu toh zai samu abinda yake so, zai kuma tabbatar da Fatiman sa ta samu gatan da bata taba tunani ko hasashen samun sa ba.
***Tunani Abba ya fad’a ganin address din da Muhammad ya turo masa a matsayin in da yake,Emir Palace Kano, Emir Palace Adamawa-Yola, me hakan ke nufi? Kiran Abban su Fatiman yayi yazo ya same shi a part din sa, ya nuna masa message din sannan ya kira sauran yan uwan su Abba Musa suka hau tattaunawa akan abinda ya kamata su yi. Dama chan Abba Musan yana siyasa sosai, sai sukayi shawara akan shi ne zai wuce gaba wajen binciken waye Muhammad din a cikin kwana uku kachal. Haka kuwa akayi, washegari ya same su da maganar da ta yi matukar basu mamaki. A yadda suka sani idan wani daga cikin irin wannan yaga yarinya yana so, kawai aikawa ake iyayenta suzo ayi magana a fadar sarkin, a matsayin shi sarki dama uban kowa ne, sai suga ga banbanci inda Muhammad din yazo kai tsaye ba tare da ya nuna shi din waye ba, ba kuma tare da ya nuna karfin iko na mulki ba, hanyar da ta dace da kowa yake bi wajen neman aure shima ita yabi.
A cikin su babu wanda be yi amanna da maganar ba, musamman binciken da Abba Musan yayi da irin yabon da Muhammad din ya samu daga wajen mutane da dama musamman mazauna masarautar.
Shiru Abba yayi bayan kowa ya gama tofa albarkacin bakin sa, aka bashi dama a matsayin sa na mahaifin Iman din,
“Bakwa ganin idan iyayen yaron nan suka san in da yazo neman aure zasu kyale shi, duba da mu din ba wasu bane akan irin girma da nasabar gidan da ya fito.”
“Idan har a yadda bincike na ya nuna min ne, iyayen sa basu da matsala masu son talakawan su ne, dan haka muyi addua kawai in sha Allah alkhairi ne.”
“Shikenan, Allah ya tabbatar mana da alkhairi,.”
“Yanzu kayi magana, Amin ya Allah.”
” Ina neman alfarma daya, da mu bar maganar nan a tsakanin mu zuwa muga abinda Allah yayi.”
” Hakan yayi, Allah ya shige mana gaba.”
Suka hada baki a tare, sai kuma suka shiga wata hirar tunda daman su dan dade basu yi irin wannan zaman ba, anan duk suka ci abinci a tare sannan kowa ya tafi zuwa sabgar sa. Aka bar Yaya a zuwan zai kira Muhammad din da daddare ya sanar dashi ya bashi izinin yazo yaga Fatiman su daidaita, da daddaren bayan ya gama komai ya turawa Muhammad din text message akan ya cigaba da zuwa. Muhammad na zaune shi da Musaddik suna kallon video da ya saka akayi wa Khalil suna kwasar dariya text din ya shigo, tashi yayi ya daka tsalle kafin yace
“Yess!!!
” Ya akayi?”
” Karfe nawa yanzu?”
Yace yana kallon agogon falon
” Opss Ashe dare ya fara, ba dan ba dan ba da yanzu zanje na ganta, amma ba komai kafin na wuce Abuja zan tsaya na fara ganin ta.”
” Me faru wai.”
” Karanta!” Ya mik’a masa wayar
” Ah congratulations angon fatiti, Allah ya tabbatar mana da alkhairi.”
Rik’e k’ugu yayi yana hararar sa
” Allah ka sake bata mana suna sai na saka frog jump, kaji ma na ratse.”
” Kut! Allah fa ka raina ni Moh, komai sai kace zaka sani frog jump an fad’a ma nima kamar wadanchan dogs din naka ne na bakin gate.”
” Ka dai kula, kana magana ne da Captain Muhammad Ahmad Santuraki, Captain Moh!”
” Whatever, ni dai muhammadu na sani, ba wani bragging da zaka min.”
” Zaka gane ne idan na dauke ka na je na jefa wa mayunwatan zakunan nan na barack, ba zaka sake kiran sunana gatsal ba.”
” An gaya ma kowa irin khalil ne? Lusari!”
Dariya suka saka Muhammad ya shiga gwada yadda Khalil din yake, suka sake tuntsurewa da dariya suka tafa
” Ashe farar kura ce a wajen, sai uban cika baki dan iskan yaro, gobe ma ya sake, naso ka dan saka su sun sassama masa jiki wallahi,.”
” A hakan ma nasan sai sunci zalinsa ai.”
” Wicked soul!” Yace yana dariya
” Naji, bari naje na kira Baby na, naji voice dinta me dadi kafin gobe naje na ganta, dan yanzu ina da license, na matsu na ganmu tare, muna yawo a garin nan cikin mota my hands in to her’s, ga cool music na tashi Malam, wow love in the air.”
” Toh Mr Romeo, Allah ya kaimu dai zamuyi kallo, yadda kake son ta Allah yasa tana maka ko rabin sa ne.”
” I don’t care, as long as munyi aure, zan koya mata yadda zata so ni.”
” We shall see.”
***Ruwan zafi ne a katon bawo, Khalil na zaune a gaban ruwan hajiyar su na danna masa bayansa, gaba daya jikin sa ciwo yake kafarsa kamar zata cire yake ji, babu irin tambayar da batayi masa akan me ya same shi ba amma yaki fad’a mata, haka Mama ta bugu tana fad’an tafiyar Khalil din hajiyar ta fad’a mata a yadda ya dawo, kuma yaki cewa komai. Yana jin su har suka gama ya tashi ya koma dakin sa ya kwanta yana tariyo abinda ya faru cikin tausayin kansa. Shi ya jawo yana takama da shegen bakin sa ya je ya kaishi ya baro, dama an fad’a mutum ya kiyayi harshen sa, akwai hadisi guda da akayi magana akan harshe da kiyayar sa, yaga izina a kansa, gashi bashi da damar fadawa wani abinda ya faru domin yasan shi za’a yi wa dariya, ko da muhammadu a iya soja ya tsaya matsayin da yake kai ya isa ya taka shi son ransa ba kuma wanda ya isa yace dan me? Balle ganowar da yayi waye Muhammad din, anan ya gane bakin rijiya ba wajen wasan yaro bane, shi din ma ganganci ne da kuruciya. Eh toh kuruciya mana tunda dai yasan a girme Muhammad din zai girma shi dole ya fishi hankali da komai. Abu daya ne zai hana shi walwala, yadda zai yi da tarin soyayyar ta, gashi yayi masa kashedin ko a hanya babu shi babu ita, ya kuma tabbatar idan har ya kuskura yayi wani abu, za’a iya neman shi ma baki daya a rasa, dan masu kudin nan yasan ba wani abu bane a wajen su su batar da mutum bat, har abada a daina jin labarin sa.
Tagumi ya rafka yana jin kamar yayi ta kurma ihu ko yaji sassaucin radadin da zuciyar sa ke masa. Allah sarki Khalil 😂
GIPHY App Key not set. Please check settings