SULTAAN 4

Advertisement

 👑 *S U L T A A N*

Mss Flower🌸

*FITATTU HUƊU🔥*

Advertisements

_RESEMBLANCE OR SIMILARITIES OF STORY/LIFESTYLE SHOULD BE CONSIDERED AS TOTAL COINCIDENCE_

*FIRST CLASS WRITERS ASSO…*

           *04*

Advertisements

*ZEENA POV* 

Ƴan mata uku ne ke tafiya da yammacin, biyu kansu ɗauke da tulu yayin da ta tsakiyarsu babu abin da ta ɗauka, wani irin mugun kyau gareta mai fizgar hankali, her skin is so white as snow, yayin da fatar jikinta was shiny as silk, ta na da matsakaicin tsayi, dogon gashinta da ke tsefe ya sauka har bisa mazaunanta sai kitso jela biyu da ta zubo shi ta gaba wanda ya sha ado na farin dutse, duk da sanyin yammacin ba ta saka wata tufa ta ƙwarai ba, wani irin jan saƙi ne a jikinta felle biyu, ɗaya ta rufe Fulaninta yayin da ta ɗaura ɗayan a ƙugunta, ta sha jigida fara mai adon jan dutse, haka ta saka sarƙa da ƴan kunnaye ja da fari, ilahirin jikinta sai ya kaɗa a duk takun da ta yi, sun yi tafiya me nisa kafin ta dakata cikin shagwaɓa ta dubi ƴan matan ta ce “na yarda zobe na a bakin ruwa” 

Cikin jin haushi babbar cikinsu ta ce “sai ki bari sai gobe ki ɗauka in rabonki ne” 

“Ni ba zan yarda ba, idon kafin goben wani ya ɗauke shi fa, kin san yanda nake son zoben nan Nenne don Allah mu koma in ɗauko abuna” ta ce cikin turo baki kyawawan fararen idanunta masu ɗauke da kwalli suka kawo ruwa. 

“Wallahi Zeena in kin ga na koma can a yau, sai in ba suna na Nenne ba, wannan uwar tafiya ki ce wani mu koma saboda wani zobe, kin ga tafiyata” ta yi gaba ɗayar ma wadda da gani ta girmewa Zeena ɗin ta ce “Ni ma dai, sai ka ce marasa hankali ko kafin mu koma ai bakwai ta yi”

Hawaye ne suka shiga zuba a idonta, cike da shagwaɓa ta shiga buga ƙafarta tana cewa “tunda ba kwa sona ni na tafi ɗauko abuna ni kaɗai” 

“Sai kuma ki yi” in ji Nenne da ko waigowa ba ta yi ba. 

Juyawa Zeena ta yi tare da sakin wani murmushin jindaɗi, ta zaro zoben daga haɓar abin da ta ɗaure ƙugunta sannan ta kama hanyar wani wajen daban. Ta yi tafiya mai nisa kafin ta ƙarasa wata bukka, batareda ƙwanƙwasawa ba ta tura ƙofar tana cewa “Nuri!” 

Wani matashin saurayi da ke zaune bisa tabarmar kaba ya yi sauri ya miƙe bakinsa fal fara’a ya ce “na ɗauka ba za ki zo ba, har na fidda rai” 

Wani kyakyawan murmushi ta yi, da ya bayyana dimples ɗinta sannan ta ce “ai tunda na ce maka zan zo, zan zo” ta ƙare tana kaɗa idanunta tare da faɗawa jikinsa tana dariya, rungumeta ya yi yana shaƙar wani cool scent da ke fita daga jikinta, shafa soft skin ɗinta yake yayin da ta yi lufff a cikin jikinsa alamun tana jin daɗin yanayin

“Zeena ki aminta mu yi,za su bari mu yi aure in kin samu ciki” ya fizgo maganar yana shinshina wuyanta

“Uhm! Wai Nuri ba na ce ka daina wannan maganar ba, ba ka yarda da Ni ba ne kome?, Na yi maka alƙawarin zamu yi aure fa, Ni duniya ban da wani mijin da ya wuceka, amma na yi wa Ammata alƙawarin ba zan taɓa aikata wannan ba, ka tayani riƙe alƙawari ba karyawa ba” ta ce cikin shagwaɓa.

Yarinyar wani birkita mai lissafi take, ta haɗu ta kowani lungu, ba abin da yake mugun ɗaga masa hankali kamar huge boobs ɗinta da ke a tsaye duk ɗan motsin da za ta yi sai sun kaɗa, ba don son gaskiya yake mata ba baya son duk abin da zai ɓata ranta babu abin da zai hana masa yin komai da ita. Hannunta ta ɗora saman na shi da yake massaging soft plump boobs ɗinta ta ce cikin shagwaɓa “Nuri ka siyo min wurin da ka ce, gobe nake son canza kitso fa” 

Ya lumshe ido tsananin daɗin muryarta ya ce “tunaninki ya mantar da Ni” 

Dukansa ta yi tana turo baki kamar wacce za ta yi kuka sannan ta ce “Ni babu ruwana da kai tunda ba ka sona” ta miƙe zumbur ta juya bayanta tana kukan shagwaɓa. 

Fuck! Yarinyar wani birkita masa hankali take, ƙuri ya yi wa curvy waist ɗinta zuwa huge bombom ɗinta masu wani irin girma suna sama da ƙasa dalilin buga ƙafarta da take yayinda jigidar da ke kan naked pure white skin ɗinta ta shiga ƙara mai jan hankali, lumshe idonsa ya yi ya ƙarasa inda take yana ɗora hannu kan bombom ɗinta tare da ɗan matsawa sannan ya ɗora kansa kan kafaɗarta ya ce “to bari kukan mana, na kawo miki abin da ya fishi ai”

Dariya ta saki da ta bayyana wushiryarta sannan ta ce “ina yake Nuri?”, Lakace mata hanci ya yi ya jawo wata leda mai ɗan girma ya ɗaga hannunsa sama yana cewa “in kina da tsayi ki amsa”cikin dariya

Ɗage ta fara yi tana ƙoƙarin amsa amma ta kasa hakan ya sa ta fara kukan shagwaɓa, tare da turo baki, janyota ya yi tare da haɗe bakinsu waje guda, ya shiga ba ta wani kisses, ƙafarsu gaza ɗaukarsu ta yi dole suka zube kan tabarmar kabar, soft lips ɗinta yake shanyewa kamar an aikosa, sun jima a wannan yanayin kafin ya janye bakinsa dukkansu suka shiga maida numfashi, kuncinta ya dafa tare da tallabo haɓarta idanunsa na ɗigar hawaye ya ce “yaushe ne za ki zama halaliyata,mallakina haƙurina na daf da ƙarewa” 

Zuba masa kyawawan idanunta ta yi masu kama da an ɗiga ruwan zaiba, farare tass wanda suka zo da kwallinsu, cikin tsantsar sonsa ta ce “wannan rana za ta zo Nuri, zuciyata da dukkan gangar jikina zai zamo naka ba da jimawa ba” 

Ya lumshe idanunsa tare da haɗe goshinsu waje guda ya ja dogon numfashi sannan ya yi mata sumba a goshi ya ce “tashi mu je, dare ya fara yi, kar a miki faɗa”

Hannunsu sarƙe da na juna suna hira cikin nishaɗi har suka kawo wani gida ginin jar ƙasa wanda haka gine-ginen gidajen wannan ƙabila yake, matsota ya yi a jikinsa yana kallon ƙwayar idonta ya ce “bana son rabuwa da ke” 

Dariya ta saki wadda ta ƙara bayyana tsantsar kyawunta duk da duhun dare ne ita ɗin wani irin haske gareta, farar fatarta sai ka ce wata ɗan daren goma sha huɗu, ta kaɗa idanunta ta ce “gobe idan Abbu baya nan in su Nenne zasu ɗebo ruwa za ka ganni, in yana nan kuma sai jibi” 

Ya ɗan matsa bombom ɗinta ya ce “in dai zo gobe ko da dare ne sai mu haɗu bayan bishiyarmu ta alƙawari, ba na jin zan rayu in ban ganki a gobe ba” 

Ta yi wal da idanunta ta ce “to shi ke nan” ta manna mai sumba a baki ta wuce da gudunta. 

Cikin sanɗa ta fara ƙoƙarin shiga gidan. Tana wulla idanu zuciyarta cike da addu’ar ka da ta yi gamo da iyayenta har ta shige ɗaki, turus ta yi ganin dukka gidan a tsakar gida suna shan gwanda, zaro idanu ta shiga yi cikin rashin gaskiya. 

Abbunta cikin fushi ya miƙe yana cewa “ke wanne irin kunnen ƙashi gareki, ba kya jin magana ko, duk nasiha da faɗan da nake miki a banza ko” 

Hawaye suka shigo zubo mata, cikin shagwaɓar da ta zame mata jiki ta fara cewa “Abbu zobena ne fa ya faɗi na koma ɗaukowa kuma sai da na ce su rakani suka ƙi” 

“Uban zoben, daga wajen wannan ɗan iskan yaron kike, ke sai kin kaimu ga hallaka hankalinki zai kwanta ko?” Ya ce a fusace yana ƙoƙarin kai mata duka, da gudu ta ɓoye bayan Ammanta ta ce “Amma don Allah ki ba wa Abbu haƙuri, ba zan ƙara ba” sai yarfe hannu take 

Amma ta sakar mata mugun ranƙwashi ta ce “shegen tuban muzuru, kin sani sarai prophecy ya ce soyayyarki da mutumin da ba mai muƙami ba na nufin halakarsa da halakar dukkan ƙabilar nan, me ya sa ba za ki rufa mana asiri ba ne Zeena” 

“Amma wallahi ina son Nuri, ƙila bokan ma ƙarya yake, don kawai na yi kyau sai a ce dole sai wani shugaba zan zauna da shi, in na so wani da ba shugaba ba kowa nawa zai mutu, Ni ban yarda ba Allah” ta ce cikin buga ƙafarta

Amma takaici ya sa ta wanketa da mari sannan ta ce “don uwaki tun kafin a haifeki boka ya shaida mana da zuwanki da yanayinki, duk kalaminsa babu ƙarya don zahiri ga shi muna gani, ya tabbatar mana ke haske ce idan kika haɗu da duhu, duhu zai mamayemu gabaɗaya, mu je na duba ki sam ban yarda cikakkiyar budurwa kike ba, da alama yaron can ya lalataki shi ya sa har kike mana furucin ke kina son shi duk da kuwa mu da muka haifeki zamu faɗa halaka” 

Kuka take yanzu sosai hannunta dafe da kuncinta don marin da ta akai mata bai saketa ba, idanunta raurau ta ce “Amma wallahi ban taɓa yin komai ba” 

“Ƙarya kike munafuka, wuce ciki mu gani, idan na tabbatar da zargina kuwa ke da fita har gaban abada” Amma ta ce tana hankaɗata ƙeyarta zuwa cikin ɗaki…

*🔥FITATTU HUƊU🔥*

      

*👑SULTAAN* # Nml grp ~N~ 300 vip ~N~ 500 via 1401611541 Access bank, shaidar biyanki ta wannan numbern 08167888934

*Mss Flower🌸*

TSINTACCIYA

Nimcyluv

Baƙar fata

Autar manya

DATTIJON ARZIƘI

Real ladingo

Gaba ɗaya 800

Via 6850917335 Na’ima Shu’aibu Sulaiman Fidelity Bank, masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 za ku tuntuɓa. To show evidence of payment 08142105218

*Mss Flower🌸 08167888934* For more information😇

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like