TAKUN SAAKA 14

Advertisement

 

*_Typing📲_

*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

Advertisements

*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM_*

Advertisements

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

_________________________

*_MACE SAI DA GYARA_*💃🏻💃🏻

 *Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*

_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawa nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki._

*_Muna da haɗin_*

_Turaren wutane_ 

_Humrh_ 

_Kulacham_

_Turaren wanka_

_Turaren Kaya_

_Gyaran jiki_ 

_Na amare_ 

_Da masu jego_

_Da sabulai masu gyara fata_

*_Da magungun nan mata_*

_Irin su kaza_ 

_Tantabara_

_Tsumi_

_Gumba_

_Zuma_

*_Duka akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan 👇🏼_*

Wushishi road KADUNA

08067807620

09057713999

_________________________

*_Chapter Fourteen_*

………….A gidan Ummi komai ya canja. Gaba ɗaya ya ranta sun bar walwala. Sun daina fara’a. Sun daina zaman hira, abinci ma kaɗan suke tsakura. Idan tai magana suce sun ƙoshi. Ta ko ina ta gaza gane kansu.

      Da farko tayi biris da su, duk da kuwa ta fahimcesu tsaf. Sai dai ganin abin nasu bana ƙare bane sai itama lamarin ya fara damunta. Dan ita kanta sun jefata a cikin kaɗaici. Hatta da Hibbah ƴar karamarsu itama ta ɗauke mata wuta. Saboda wannan abun daya faru ma ta tattara ta koma makaranta duk da Yaya Abubakar ya hanata zuwa da.

    Duk da ta ɗan fuskanci ƙalubale a wajen mutane a ranar data koma saboda tafiya da itan da ƴan sanda sukazo sukayi ranar haka ta daurema zuciyarta ta cigaba da zuwa. Bakuma ta sanarma kowa ba. Dan a ganinta da zaman gidan su tana cigaba da ganin Abba da baƙinsa gara kallon da ƴan makarantar zasu mata.

        Tunfa Ummi na ɗaukar lamarin nasu wasa sai ƙara girmama ya keyi. Dan kwanakin nan biyu ma basa dawowa gidan sai sun dai-daici tayi barci sannan. Hankalinta sosai ya kuma tashi. Ga damuwar yaranta, ga damuwar auren da aketa ƙulle-ƙullen nana musu na son zuciya. Wanda tsaf ta gama fahimta da gane ina hakan ya dosa. Sarai ta gane manufar Abbah akan son ƙulla auren ƴaƴanta da nashi, manufar kuma duk ɗaya ce tsakaninsa da hajiya mama. 

      Gaba ɗaya ta rasa ina zata saka kanta taji sanyi, babu uwa babu uba, babu abokin shawara a cikin ƴan uwa, babu wanda zata kaima ƙara ya duba matsalarta ya share kukanta. Gudun abinda zaije ya dawo kuma ke sakata kwaɓar ƴaƴanta akowane lokaci. Bata son abinda zai rabata da su. Bata son a cutar mata da su. Dan sune hope ɗinta, sune murmushin fuskarta. Sune masu share hawayenta da tun tana ƴar ƙanƙanuwarta suke kwaranya a bisa kumatunta. Tasan nuna ƙarfinsu ya kawo kuma zai iya zama sanadin da komai Abba zai iya aikatawa a garesu domin samun cikar burinsa, kuma kamar yanda yasha faɗa koda ya salwantar da rayukansu babu mai yarda shine ya aikata. Wasu hawaye ne masu zafi suka silalo mata saman fuska. 

       Wata banzar dariya Abba da ke shigowa cikin sashen ya shiga tuntsurawa yana tafa hannaye. Cike da izgili ya dubeta sheƙeƙe yana faɗin, “Kuka kuka kuka! Ai kuwa yanzu kika fara kuka Asiya. Yo ina jarumtar taki ne yau? Shin har kin fara zuwa ƙasa ne tunkan ma a ɗaura auran manufarsa kuma ta tabbata?. Tunda har kikace ni ban isaba Asiya, to wlhy kema bazaki taɓa isa ba. Yau ina wanda kike gadar da shi? Ya tafi tamkarma ba’ayisa ba. Abinda kika hanashi yay mana ta hanyar zagon ƙasa ya dawo hannunmu a lokacin da ko ido baki isa ɗagawa akai ba. To suma ƴaƴa mazan da kike ɗagawar kin haifa masa zasu mamaye komai tafin hannunmu zasu cigaba da zama ballagaza kawai. Zaki iya tashi kuma mu shige ciki dan ina bukatar haƙƙina. Inba hakaba kuma zan ƙwata anan cikin falon babu ruwana….”

      Hanyar bedroom ɗinta ya nufa yana gama faɗa alamar ta biyosa. Ummi da ke jin wani ƙullutun abu yazo ya tokare maƙoshinta ta shiga karanto duk addu’ar da tazo mata a saman harshe saboda jin numfashinta na fita a gwagwgwame. A hankali sanyi ya rinƙa shiga cikin ƙashinta, yayin da jikinta ya fara wani irin rawa, har haƙwaranta na haɗuwa waje guda. Hannu takai domin lalubo wayarta da ke saman centre table. Sai dai hakan ya gagara sakamakon gushewar gani da ta risketa a lokaci ƙanƙani. Hannunta ya goce da ga lalube wayar, sai gata ƙasa wanwar da ga saman kujera…..

         A dai-dai wannan lokacin Hibbah ta shigo tana masifar bibiyarta da kullum Shuraim keyi babu fashi balle nuna gajiyawa duk da yarfatashin da take yi a kulum. Data fita da ga gida zuwa makaranta yana biye da ita. Hakama idan ta dawo sai ya rakota har gida ta hanyar bibiyarta. Zuwa yanzun tun lamarin nasa na bata mamaki har ya koma takaici da al-ajab. Har tabbayar kanta take shin baida aikinyi ne ko mi?. Wannan takaicin nasane ya sata yau ana saukesu a napep taje tai masa knocking glass. Yana saukewa ta balbalesa da masifa batare data yarda sun haɗa ido ba dan karma yay mata kwarjini. Sai dai abin ALLAH wadai da takaici, harta gama masifar tata ma bai nuna yaji haushi ba. Sai ma murmushin da ya nema rikita mata lissafi ya sakar mata yana wani narkewa a cikin kujera.

          Wani uban kara ta ƙwalla tana isa inda Ummi ke kwance wanwar tana wani irin tari dake fita da ƙyar. Kiran sunanta ta shigayi tana girgizata hankali tashe. Sai dai ina Ummi ta fita hayyacinta. Dabarar rarumar wayar Ummin ce tazo mata a rai. Batare data nutsu wajen ganin wanda ta kira ba kawai tai dailing numbern farko, dan tasan su ne dai kawai suke yawan kiran no din Ummin tasu a koda yaushe.

       “Yaya dan ALLAH kazo gida, Ummi…Umminmu. Na shiga ukuna. Ummi dan ALLAH ki tashi. Wlhy kika mutu nima mutuwa zanyi. Dan ALLAH Ummi na roƙeki karki mutu. wlhy bazamu sake yin fushi da ke ba. Mun tuba Ummi, mun daina. Mun yarda zamu auresu Ummi…….”

    Sambatu taketa faman yi tama manta da waya a kunnenta. Kukanta ya fiddo Abba da ga ɗakin Ummi ɗin wando a hannu. dan harya cire kaya ya baje a gado yana jiran jakarsa ta shigo ya murza a wulaƙance. Ido huɗu sukai da Hibbah da ke sake ƙwala kuka tana kiran Ummi da girgizata. Ai sai ta sake fasa wata ƙarar ganin a yanda ya fito, saboda bai saka wandon dai-dai ba an samu mishkila wajen bayyanar jikinsa.

       Sakin Ummi tai ta fita a guje da ga sashen baki ɗaya jikinta na rawa. Tana da yayu maza manya. Amma tunda take da su ko zama da singlet da boxers basu taɓa yi a gabanta ba balle a yanayin da Abban ya fito wanda bata taɓa ganin wani mahaluki a yanayin ba.

           Jikinsa ta faɗa dai-dai maigadi ya buɗe masa gate ya shigo, dan Hibbah wayarsa ta kira saboda shine na ƙarahe da ya kira Ummi yaji yaya jikinta? Dan ya kwana biyu baizo gidan ba. Duk yanda yaso ganin ya janyeta a jikin nasa hakan ya gagara, sai sake ruƙunƙumesa takeyi jikinta na rawa, yayinda taketa faman son ɓoye fuskarta a ƙirjinsa duk da tsahon nata gaba ɗaya iya ƙirjin nasa ta tsaya.

           Cikin zafi-zafi ya shiga tureta yana girgizata. “K Muhibbat nutsu, muje inga Ummin gani nazo”.

      Jin muryar da bata yayunta ba ya sata saurin ja da baya tabar jikinsa. Isma’il da ya samu ta rabu da jikin nasa da sassarfa yay gaba abinsa zuwa sashensu har yana haɗawa da ɗan gudu-gudu. kusan cin karo sukai da Abbah da ya koma ya ɗakko kayansa saboda ihun da Hibbah tayi ya farga da halin da yake a ciki. Duk da ya kuma ga Ummi a yashe a ƙasa sai kawai firgici biyu ya kamashi. Na farko kar wani yazo ya gansa a yanda yake sakamakon ihun Hibbah a zata wani abu yaso mata har Ummi ta shiga halin da take ciki a yanzu. Dan haka ya fito dan ya gudu salin alin, idan Hibbah ta sako sunansa a ciki kuwa yasan ta yanda zai kare kansa ai.

         Haka kawai zuciyar Isma’il ta raya masa irin abinda Abban ke gudu. Dan haka yasa ƙafa ya taɗesa sai gashi a ƙasa tim. Takan kafafun Abba yabi da shaggun takalman ƙafarsa, ji kake ƙasss ƙashi na bada sautin karyewa ko tsagewa. Wata iriyar wahalalliyar ƙara Abba ya saki tare da ɗaukewar numfashi na wucin gadi. Ko waiwayensa Isma’il baiyiba ya ida afkawa cikin falon inda ya hango Ummi a ƙasa itama babu alamar rai tattare da ita. 

        “Ummi!… Ummi! Ummi!!” ya shiga ƙwala mata kira da kama hannunta yana girgizawa. Sai dai babu alamar motsi tare da ita sam. Mikewa yay da sauri ya ciro wayarsa yay kiran Yaya Umar da yasan shine mafi kusanci da gida. Sai dai bai ɗaga ba. Tunawa ana sallar la’asar yanzu haka ya sakashi cije lip ɗinsa na ƙasa ya cusa wayar a aljihu. Batare da tunanin komai ba ya ciccibi Ummi gaba ɗayanta yay waje. Sai lokacin Hibbah ta nufo falon sabida hango abinda Isma’il ɗin yay ma Abba.

      “Muje asibiti” yace mata kawai yana nufar hanyar gate. Babu musu ta bisa tana kuka da riƙe hannun Ummi ɗin da ya ɗakko. Sai lokacin kuma Hajiya mama ke fitowa da ga sashensu itama. Ta bisu da wani irin kallo mai ma’anoni da yawa saboda ganin baƙon fuska ɗauke da Ummi ɗin. Dan duk zuwan da Isma’il ɗin keyi gidan ba taɓa haɗuwa sukai ba. Wahalallen ihun da Abba ya saki ne ya fargar da ita halin da yake a ciki, babu shiri ta runtuma a guje kansa tana ƙwala kiran sunansa…….

★★★★_____★_____★★★

       Tun kan su ƙarasa asibitin Isma’il yay ƙoƙarin kiran doctor Bilal. Cikin sa’a kuwa ya ɗaga dan mutuminsa ne. Bayani yay masa cewar gasu a hanya tare da mara lafiya su zam cikin shiri. Dr bilal yace babu damuwa sai sunzo. 

       Cikin mintuna kalilan kuwa suka iso asibitin saboda uban gudu da yake zugawa a hanya. Kamar yanda yay fata sun sami su Dr Bilal na dakon isowarsu. Babu ɓata lokaci aka shiga da Ummi ciki.

     Kuka sosai Hibbah keyi da son binsu, badan yaso ba ya riƙo hannunta yana ƙoƙarin dakatar da ita. Sai dai taƙi ta nutsu, dole yay mata yanda yasan zata nutsun, ya jawota jikinsa ya rungume. Da ƙarfi ya rumtse idanunsa zuciyarsa na wani irin bahagon gudu. 

            Itako Hibbah tuni ta ƙara lafewa tana wani irin kuka mai ban tausayi, dan gaba ɗaya ma ta mance a jikin wa take. Sai da ƴar nutsuwa ta fara zo mata ne sakamakon kiran wayarsa da akayi tai azamar janye jikinta. Komai baiceba shima. Sai ƙoƙarin ciro wayarsa da yay a aljihun wandonsa. Ita kuma ta koma kan kujera ta zauna tana cigaba da kukanta da add’ur ALLAH ya bama Umminsu lafiya.

      Yaya Umar da yaga miss call ɗinsa bayan fitowarsu massallaci ne ya kirasa. Dan haka yay masa bayanin da bazai ruɗar da shi ba. Koda ya yanke kiran sai ya shiga kiran sauran suma.

★★

      Cikin mintuna kalilan yaran Ummi suka gama hallara a asibitin. Gaba ɗaya hankalinsu a tashe yake. Sai dai sunata ƙoƙarin lallashin Hibbah da ke kuka sosai har yanzu. Harda su amai. Ga zazzaɓi mai zafi ya gama lulluɓeta matuƙa.

     Fitowar Dr bilal ya sasu maida hankalinau garesa. Cikin son kawar da damuwarsu yace, “Ku kwantar da hankalinku babu wata matsala mai yawa insha ALLAH. Dan yayi ƙoƙarin kawota asibiti akan lokaci. Sai dai ku kiyaye dan ALLAH kar yazam muna tufƙa ana warwarewa.”

        A take nutsuwa ta saukar musu. suka shiga jerama Isma’il godiya tamkar zasu ɗaukesa su goya. Shi dai ransa a dagule yake da takaicin Abbansu, dan shi baisan ba mahaifinsu bane.

          Sun cigaba da dakon jiran farkawar Ummi da aka sakama ƙarin ruwa a asibitin har wajen sha biyu na dare da aka basu sallama saboda Alhmdllhi komai normal, amma sai Dr Bilal yace su barta anan ta ƙara hutawa har sai gobe idan ALLAH ya kaimu da yamma. Duk sun gamsu da bayanin nasa. Dan haka sukai masa godiya da fitowa dan su tafi gida Hibbah da zata kwana da ita tare da Nurse tayo musu rakkiya.

         Har sannan Isma’il na tare da su. Karan farko a tarihi da Hibbah ta dubesa cike da girmamawa da idanunta kumburarru. “Yaya Isma’il mun gode sosai. ALLAH ya bada ladan zuminci. Yanda ka jikan Ummin mu, kaima ALLAH ya baka ƴaƴa da zasu jiƙanka. Ya ƙarama Abbanka lafiya da tsahon rai mai amfani, ya jiƙan Umma”.

      Ba karamin ratsa zuciyarsa addu’ar tata tayi ba. Ya kafeta da ido har sai da Yaya Umar ya zunguresa sannan ya sauke ajiyar numfashi da sakin murmushi. “Nagode sosai auta. ALLAH ya karama Ummi lafiya ya albarkaci rayuwarki. ALLAH ya baki miji na gari”.

       Cikin jin daɗi yayunta suka amsa masa da amin. Itama tattausan murmushi da bata taɓa masaba a yanzu ta saki tana juya baya alamar taji kunya da addu’arsa ta ƙarshe. Su Yaya Usman suka ƙyalƙyale da dariya Ammar na tsokanarta. Bata kulashi ba dan yau batajin yin faɗa Ummi bata da lafiya.

      Tun a asibitin suka rabu da Isma’il. Shi yay gida suma suka wuce gida. Inda tunkan su shiga sukaji labari a bakin maigadi cewar Abba ma na asibiti. Ya fadi ne a bakin ƙofa da alama yaji ciwo a kafafunsa. Hakama goshinsa da bakinsa sun fashe yanata zubar da jini ma.

       Kasancewar da ga Hibbah har Isma’il basuyi musu bayani ba sai basu kawo komai a ransu ba suka ɗauka tsautsyine kawai. Addau’ar samun lafiya sukai masa suka shige. Dan ba’ai musu tarbiyyar son ganin lalacewar wani ba koda ace maƙiyinsu ne.

*________________________________*

           A ɓangaren Abba kam da ƙyar aka iya ɗagasa da ga inda Isma’il ya taɗesa. Bakinsa duk ya fashe da goshinsa daya daushi kwalliyar tsitstsigen baranda. Hakama kafafunsa da alamar yayi karaya ko targaɗe. Dan ko takasu baya iyayi ma. Hasalima a sume aka ɗaukesa da ga gidan zuwa asibiti saboda jinin da yayta kwararwa kafin Junaid yazo da mota su fita da shi zuwa asibiti.

      Su hajiya mama babu wanda yasan ainahin abinda ya faru da Abban suma. sai dai kansu ya ɗaure matuƙa ganin da ga shi sai boxer kayan da ya fito da su a hannu sabida ihun Hibbah yashe a gefe. Sunma rasa yaya zasu fasalta al’amarin musamman da likita ya tabbatar musu kafarsa ɗaya ta samu karaya da hannunsa. Ɗayar kuma tsagewar ƙashi ce ga ciwon goshinsa dana bakinsa da yay wanu zundun-dun uwa an saki shantu. 

         Hajiya mama ta hana ai masa gyaran karayar wai sunada mai gyaran gargajiya zaizo da ga kauye. Sai a jirasa yana hanyar tahowa. Tun yamma ake jiran mai gyara har dare ya tsala bai iso ba. Haushin abinda Hajiya mama tai musu su kuma likitocin sunce bazasu taɓa ƙafar ba har sai wanda tace ɗin yazo ya gyara masan. Duk roƙon da Momy taita musu sunce bazasuyiba wlhy.

*_WASHE GARI_*

     Da safe acikin su Yaya Abubakar babu wanda yabi takan zancen duba wani Abba. Da dai su Ammar suka kammala yin breakfast suka gyara gida sai suka runguɗa asibiti wajen mahaifiyarsu. Sun isketa zaune Hibbah na shafa mata mai saboda wanka da tayo. 

          Ta dubesu cike da tausayi da begen ƙishirwar murmushinsu. Duk wanda ya gaidata sai ta kamo hannunsa ta shafa kansa tana ƙoƙarin haɗiye hawayenta. 

       “Ku daina fushi da Umminku kunji”. 

Ta faɗa cikin damuwa da ƙunar da takeji a cikin zuciyarta. Komai basu iya cewa ba sai dai dukansu sunyi ƙasa da kawuna ransu fal tausayinta. Musamman Yaya Muhammad da yasan wani yanki na labarinta batare da itama ta sani ba, shima Abbansu ne ya sanar masa kafin ya rasu. Ya kuma tabbatar masa ya faɗa masane saboda wataran yasan kunnensa zaiji gorin da za’aima mahaifiyarsa kar zuciyarsa ta ɗauki wani abun daban. Shine ya fara jan numfashi da ƙyar da dubanta yana ƙoƙari haɗiye hawayen da suka ciko masa ido.

        “Ummi baki mana laifin komai ba. Amma dan ALLAH a wanan gaɓar munason jin wani abu game da ke. badan bamu yarda dake bane. Sai don son sanin minene dalilin da yasa duk basa ƙaunarki?. Mi kikayi musu haka da zafi? Miyasa kika yarda kika auresa bayan shiɗin kanin Abbanmu ne? Mai fuska biyu ga mutane”.

          Murmushi ta saki mai kuna da kai hannu ta shafo kan Yaya Muhammad. “Muhammadu Aminullahi zan faɗa muku insha ALLAH. Da zaran munje gida yau zakuji komai”.

       A take fuskokinsu suka nuna jin daɗin zancenta. Dan danan suka ɓalle mata hira kamar yanda suka saba a baya. Itako sai murmushi take zuciyarya na kara sanyaya da ɗunbin sonsu da kaunarsu.

       Dr bilal ne ya shigo, bayan sun gaisa yace suje waje zasu ɗan ƙara duba Ummin suga ya ya komai na tafiya normal. Sun masa godiya tare da fitowa su duka. Duk anan ƙofar ɗakin suke zaune Hibbah nacin abincin da sukazo da shi. Kamar ance ta ɗaga kai sai idanunta karaf akan Zahidah da Hafsat, Muhammad Shuraim biye da su.

      Babu shiri ta miƙe zaram tana rarraba idanuwa. Tunkan su ƙaraso tace, “Lallai ma! Miya kawoka nan?”.

       Furucin natane yaja hankalin yayun nata gaba ɗaya. A tare suka sauke idanunsu bisa kan Muhammad Shuraim da ke sanye cikin ado da kamshi na shadda da keta maiƙo, ga hular zanna da ya murza wadda ta kara masa cikar kamala da kwar jini.

      A fusace Hibba ta sake buɗe baki zatai magana Yaya Umar ya harareta. Dole tai shiru tana wani mar-mar da idanu akaikaice tana ballama Shuraim harara.

          Shiko murmushi ya saki yana matuƙar jin mamakin tsaurin ido irin na Hibbah. Ya cigaba da takowa a hankali zuwa gaban su Yaya Muhammad da duk hankalinsu a kansa yake suna kallonsa cike da nazari. Duk da zasu iya yin sa’anni da Yaya Umar cikin girmamawa ya shiga gaishesu su duka. Gashi yaki yarda ya haɗa idanu da su shi a dole yana gaban surukai.

       Hakan ba karamin dariya da burgesu yay ba. Ammar sai wani ƙara buɗe ƙwanji ake su a dole yayu. Yaya Muhammad ya ce, “To sai dai bamu gane baƙon namu ba?”.

       Murmushi Shuraim yay cike da ladabi yana ɗan shafar ƙeya yace, “Yayanmu bazaka sanni ba. Dama ina jiran lokaci ne nazo gareku. Sai dai jin Momy babu lafiya yasa nazo dubata kafin hakan. Sunana Muhammad Shuraim Aliyu. Mai fata da addu’ar samun nutsatstsiyar yarinya mai tarbiyya kamar Muhibbat….”

      Wata malalaciyar harara Hibba ta zuba masa tamkar zata fashe dan takaici da haushinsa. Yayinda Ammar dake guntse dariya a kaikaice yace, “Dama dai a tarbiyyar ka tsaya dana yadda. Amma ba Nutsuw…..”

           Gwiwar hannu Yaya Umar dake gefensa yasa ya bugesa. Yay azamar rumtse ido da ɗaura hannunsa a wajen yana faɗin, “Wayyo Ya Umar zaka kashe ni”.

          Yaya Abubakar kam murmushi ya sakarma Shuraim shi da Yaya Muhammad. Haka kawai su dai Shuraim ɗin ya birgesu matuƙa. Dan haka Yaya Abubakar yace, “Masha ALLAH mun gode matuƙa. Bara doctor ta fito sai mu shiga ka dubata”.

       Sosai daɗi ya kama Shuraim, ya shiga jera musu godiya da addu’ar samun lafiya ga Ummi. Su ma su Zahidah suka shiga gaishesu da tambayar jikin Ummi ɗin. Hibbah kam taƙi kulasu suma wai haushinsu takeji sun faɗama Shuraim sirrinta.

      Suma basu kulata ba dan sun gane manufarta sarai. Haka ta ringa antaya musu harara suna ramawa har Doctor ya fito suka shiga su duka. 

      Tunda suka shigo Ummi take kallon Shuraim da ya durƙusa har ƙasa ya gaisheta da tambayar jikinta. Fahimtar ƙarin bayani take buƙata yasa Ammar fara rattafo zance. Sosai murmushin fuskar Ummi ya sake faɗaɗa. Dan har cikin ranta taji ƙaunar Shuraim da samun nutsuwa da shi. Tana kuma fata da addu’ar ya zame musu mafita akan haɗa Junaid aure da Hibbah da ake ƙoƙarin ƙullawa.

         Basu wani jima sosai ba yace zai wuce, bayan ya ajiyema Ummi ledan dubiya. Godiya suka sake masa Ammar ya tafi rakasa. Yana ƙoƙarin ficewa Isma’il ke ƙoƙarin shigowa. Baya ya koma ya bashi hanya. Batare da tunanin komai ba Ammar ya gabatar da Shuraim ga Isma’il ɗin. Shima Shuraim Ammar ya gabatar masa da Isma’il matsayin ɗan uwansu. Hakan ya basu damar yima juna kallon ido ciikin ido. Da alama kallon da Isma’il yayma Shuraim ɗin na tsantsar kishi ne da shima kansa baisan yayi ba. Haka shima Shuraim kallon alamar tambaya da tsoron sakkiyar da babu ruwa yayma Isma’il ɗin kai tsaye. Cike da basarwa kuma sai suka saki hannun juna kowa na ƙoƙarin haɗiye abinda ke ransa da cikin idanunsa, kafin su kalli Hibbah a tare Shuraim ya ida ficewa, Isma’il ya karasa shigowa…………✍

*_Tofa mazaje ya take ne?😂😂💃🏻, kodai Hibbahr mu ta mutunci ta haɗa karo ne😹😹😝. To muje zuwa muga wane mai rabon zai ɗauka a ciki, dan har yanzu itaɗin allura ce a cikin ruwa mai rabo ka ɗauka. zamuga yaya TAKUN SAƘAAR zai kasance a filin dagar dan ga Junaidu ma bin Halilu a gehe yana jiran waman dakala bati siddan. Ga kuma oga master da tabbas sai ya binciko hibban tunda ya ɗau alwashin hakan🐒😉😂._*

_Please kuyi manage da ga nan har Monday na ƙara samun sauƙi😭🙏🏻_

*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI……_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_

_NISHADI_

_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*

*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300

2____400

3____500

4____700

5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_* 

            

    

Leave your vote

-2 Points
Upvote Downvote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like