TAKUN SAAKA 7

Advertisement

 *_Typing📲_*

_Chapter Seven_*

……….Lokaci da aka basu da ga gidan gwamnati na kamo wannan gagarumin ɓarawo da babu wanda yasan ainahin kamanninsa na zahiri yay matuƙar tada hankalin kowacce hukuma ta ƴan sanda dake a jihar. A ɓangaren jami’an ƴan sanda na farin kaya tuni sun duƙufa wajen bincike suma. Musamman da ya kasance jami’ansu ne suka sami nasarar samo wheelchair da sauran kayan da ɓarawon yay amfani da su a waccan ranar.

            Tabbas wannan ɓarawo yana da matuƙar wayo da dabaru kala-kala da ganosa ke bama duk wasu jami’ai wahala kai tsaye. A duk ɓarnar da zai aikata yana aikatata ne da maban-banta fuskoki da salo daban-daban kuma. A kusan shekara biyu kenan da fitowarsa a bayyane babu wanda zai iya cewa ga fuskarsa ta ainahi ko samun wani labari nasa koda ƙanƙani ne.

        Duk da dai wasu a cikin jami’ai da suka ƙware sosai wajen aiki da binciko mai laifi sun taka rawar gani sosai wajen kafa masa tarkuna na musamman amma yana tsallakesu saboda duk tsiyar da zai shuka ba gaba gaɗi yake aikata ta ba sai ya shirya da shiri na gaske.

          Bayan zama na musamman da sukayi jiya game da binciken da sukeyi akansa furucin matashiyar budurwa ya shigo cikin jerin abubuwan da suka zauna domin tattaunawa. Lokaci ne da bai kamata suyi sakaci da duk wata dama da zatazo musu ba komin ƙanƙantarta. Dan haka basu tsaya sanya ba wajen bibiyar matashiyar budurwa mai cikakken suna *_MUHIBBAT ALIYU HAMZA_* da jami’insu ya kawo musu labarin alwashinta akan abin farautarsu. Dan haka suka kasance biye da ita tun a safiyar yau, tun daga ƙofar gidansu har zuwa cikin makaranta, shigarta class da fitowarta zuwa Computers room. Dukkan binciken data gudanar har zuwa kiran da taima Yaya Abubakar duk akan idon wanda ke biye da ita ne batare data sani ba…

        

Advertisements

         Sosai tashin hankali ke tattare da Muhibbah ganin inda aka kawota. Duk da Yayanta jami’in tsaro ne na ƴan sanda mai muƙamin d.p.o bata taɓa zuwa police station ba. Amma a yau sai gata a cikin headquarters na ƴan sandan farin kaya tsumu-tsumu batare da tasan laifin data aikata ba.

         Wani lafiyayyen office aka kaita da yaji kayan more rayuwa tamkar ba’a hukumar ƴan sanda ba. Ta saci kallon dattijon mutumin dake zaune kansa duƙe yana aiki kan takardun dake a gabansa. Cikin girmamawa wanda ya shigo da ita office ɗin ya ƙame yana salute ɗinsa.

        Sai a lokacin ya ɗago fuskarsa ɗauke da murmushi ya dubesu ita da shi. Kansa ya jinjinama wanda ya kawota ɗin idanunsa a kanta. Gurin zama ya nuna mata da faɗin, “Ɗiyata bismilla zauna ko?”.

        Ajiyar zuciya ta saki dan har cikin ranta ta ɗanji sanyi. Gaishesa tayi da girmamawa zuciyarta na sake samun nutsuwa da shi. Ko ba’a faɗa mataba a yanayin shigarsa da shekarunsa ya isa tabbatar mata shi ɗin mai faɗa aji ne a hukumar.

           Ɗan kafeta yay da idanusa na kusan sakan ashirin ko ƙyaftawa bayayi. A take tsigar jikinta ta fara tashi tsoro na sake faɗaɗa a zuciyarta. _Hasbinallahu wa-ni’imar wakil_ ta shiga maimaitawa tare da sunayen ALLAH. 

          Murmushi ya sakar mata da yin ƙaramar gyaran murya yana ɗauke idanun nasa a kanta. Cikin taushin murya yace, *“Muhibbat Aliyu Hamza ko?”.*

        Hibbah ta jinjina masa kanta cikin dakiya da dauriyar hana bayyanar gazawarta tana faɗin, “Eh yallaɓai”.

       “Ɗalibar koyon kimiya da fasaha a babbar jami’a ta jihar nan?”.

     Nanma kanta ta jinjina masa da faɗin, “Eh yallaɓai”.

        “Uhm masha ALLAH. ALLAH yay riƙo da hannayenki ki zama abar alfahin ƙasarki baki ɗaya. Ina matuƙar son naga ƙananun yara musamman ma mata masu himma da ƙwazo akan abinda yay mana ƙaranci irinki”.

      A karon farko Hibbah ta saki murmushin jin daɗin yabon data samu da ga garesa tana faɗin, “Thanks you Uncle”.

        Murmushi ya sakar mata har haƙoransa na bayyana. “Kinsan miyasa aka kawoki nan?”.

Advertisements

        “A’a Uncle”. Ta faɗa cike da marairaicewarta da taso bashi dariya amma sai ya danne. Cikin ƙwarewar aiki ya ce, “Taimakonki muke nema akan masu power bike ɗin jiya da suka kusan tureku, harma sister ɗinku taji ciwo a ƙafarta”.

        Kallonsa Hibbah tayi cike da tsarguwa. Fahimtar hakan da yayi ya sashi saurin faɗin, “Muna son gano kosu ɗin ƴaƴan waye? a garin nan, mu kuma kamasu mu hukuntasu. Dan bai kamata ba ace dan kawai suna ƴaƴan masu arziƙi ba su dinga shatar tituna suna zabga gudu tamkar nasu su kaɗai. Zasu iya amfani da wannan damar suyita kashe al’umma saboda ƙarfin ikon iyayensu kuma talaka bazai iya kai ƙara a ƙwatar masa haƙƙinsa ba. Yanzu bayan ALLAH ya taƙaita muku wahala jiya da bamusan halin da kuke ciki ba zuwa yanzu ai ko. Kalla nan kiga”.

      Ya ƙare maganar yana ɗaukar remote ɗin da ke gabansa tare da janye idanunsa a kanta ya maidawa ga ƙatuwar tv dake mamake da kusan rabin bangon office ɗin. “Kinsan wannan mutumin?”.

         Fuskar dattijo mai cike da ƙasumba a cikin shigar manyan kaya ta bayyana. Kallon kusan minti ɗaya tai masa kafin ta girgiza kanta. “A’a yallaɓai ban sanshiba. Bamma taɓa ganinsa ba”.

        Wani ya kuma nunowa da faɗin, “Wannan fa?”.

         “Shima haka ban sanshi ba”. Hibbah ta faɗa idonta akan hoton matashin saurayi mai saida rake a Wheelbarrow.

        Cigaba yay da latso mata hotuna kala-kala na mabanbanta mutane tana cewa bata sansu ba. Sai wani guda biyu na kusan ƙarshe data taɓa gani an nuna a labarai kwanaki.

        “Yallaɓai wannan dai na taɓa ganinsa a tv, dan an taɓa nunasa kwanaki a labarai, kuma hoton yata yawo a social media akan cewar shi ɗin babban ɓarawo ne ɗan yahoo da ya yashe manyan kuɗaɗen wani attajiri. Yayana ma yace suma suna nemansa ruwa a jallo. Kuma nemansa kukeyi halan?”.    

        Sosai ma kuwa nemansa muke muma tare da waɗancan na farkon dana nuna miki. Amma rashin mai taimaka mana irinki yasa mun gagara hakan. Amma shiɗin wanene yayan naki?”

      Kanta tsaye batare da tunanin komai ba ta ce, “Uncle shima ɗan sanda ne”. 

         “Woow masha ALLAH. Lallai naji daɗin hakan sosai. Kuma zanso ganinsa shima harma nai masa ƙarin girma saboda samun ƙanwa irinki mai ƙwazon da ya kamata ƙasa gaba ɗaya tai alfahari dake”.

     Murmushi tayi cike da jin daɗin jin za’a ƙarama Yaya Abubakar ɗinta girma ta sanadinta. Shima ganin ta hau yanda yake buƙata saboda ƙuruciya sai ya ƙara faɗaɗa murmushinsa da faɗin, “Idan har kikai mana wanann taimakon da zan miki bayani akansa yanzun to lallai yayanki zai ƙara zama babban mutum, kema kuma zaki rama jin ciwon da aka saka ƙawarki tayi jiya. Da ga ƙarshe zaki samu ƙyauta mai tsokar gaske”.

         Batare da tunanin komaiba ta ce, “Insha ALLAH zan taimakeku Uncle, indai Yaya Abubakar zai ƙara samun girma”.

          Cike da jinjina wautarta fara’ar fuskarsa ta sake bayyana. “Yauwa ɗiya ta. Aikin da zaki mana shine gano mana inda masu power bike ɗin jiya suke.”

      “Lah Uncle ai nama g…..”

Sai kuma tai shiru tare da dafe bakinta saboda tunowa da gargaɗin Yaya Abubakar na ɗazun akan karta sake ta sanarma kowa.

      “Miya faru ki kai shiru ɗiyata?”.

        Da sauri ta girgiza masa kanta. “Babu komai Uncle, inason kai musu magana su fara bani wayata nayi magana da Yaya Abubakar”.

        Shiru yayi cike da nazarinta, a zuciyarsa. Yace (Yarinya mai wayo). A fili kam ganin ta kafesa da ido yay saurin sakin murmushi. “Okay okay babu damuwa zan musu magana su baki. Amma kafin hakan zaki cika mana alƙawarin mu. Idan ba hakaba kuma zamu cigaba da riƙeki anan, tare da sakawa a kamo mana Mamanki dasu yaya Abubakar ɗin naki mu faɗama duniya cewar sunada alaƙa da wancan hotunan mutanen da muke nema kin amince?”.

        A take dukkan fara’ar dake kan fuskar Hibbah ta ɓace ɓat. Shima tuni saɓanin murmushi ya maye gurbin tasa fuskar. Ya kuma tsatstsare ta da idanunsa cike da tsoratarwa. “Yanzun nan zan bada umarnin zuwa a ɗakko min Umminki. Tare da Yayanku Muhammad har wajen aikinsa. Sai Umar da Usman. Aliyu (Ammar) kuwa yanzu haka akwai jami’anmu dake zagaye da shi a makarantarku. Kalla nan”.

         Ya ƙare maganar da juya mata lap-top ɗinsa. Wani irin firgici da ruɗani ne suka bayyana a fuskar Muhibbat ganin hotunan Yayunta tare da hotunan ɗazun daya nuna mata na waɗanda ake nema. Kowanne da taƙaitaccen bayanin dangantashi da waɗan can masu laifin. A ƙarshe aka bayyana Ummi matsayin mahaifiyarsu tare da ita mai taimaka musu kasancewarta masaniya akan ilimin sarrafa Computer.

       Saurin ɗora hannunta tayi akan baki saboda kukan dake neman kufce mata. Ta shiga girgiza masa kanta a kiɗime. “Please yallaɓai kar kai haka dan ALLAH. Ni ƴan uwana ba ƴan ta’adda bane. Basu taɓa aikata laifin komai ba sai alkairi. Karka zaluncesu ta dalilina….”

          “Inhar baki so ganinsu a cikin wani hali sai kiyi mana abinda muka sakaki ki zama sanadin alkairinsu. Bawai ina lallaɓaki bane dan bazamu iya sarrafaki kimana dole ba. Inda naso tursasaki da tun a daren jiya zamu ɗakkoki har gida kiyi mana aikin akan dole.” yay maganar a matuƙar kausashe yana bugar desk ɗinsa.

     Ɗan zabura baya Hibbah tai jikinta na rawa. Yayinda shi kuma ya shiga ƙwala kiran sunan jami’in su Nura.

        Da sauri Nura ya shigo yana ƙamewa da faɗin, “Yes sir!”.

          “Maza a shirya jami’an da zasu fita operation yanzun nan.”

     “Okay sir”. Ya sake faɗa da girmamawa yana ficewa.

       Miƙewa yay shima yana nuna Hibbah da faɗin, “Oya miƙe”.

       “Yallaɓ…..”

Hannu yasa yay zipping bakinsa alamar karta sake cewa komai.

            Ɗakin da ke ajiye da na’urori masu ƙwaƙwalwa aka kai Hibbah. Inda suka sami mutane kusan goma sha uku a ciki. Kai tsaye wajen zama aka nuna mata alamar dama ita ake jira. Zama tai tana haɗiyar zuciya. Batason yin aikin saboda gargaɗin Yaya Abubakar. A gefe kuma batason a cutar mata da ahali akan abinda basu ji ba basu gani ba. A wani gefe na zuciyarta kuma nason yi kodan abinda mutanen suka nema yi musu jiya har ga Hafsat da ciwo.

           Waya irin ta jami’an tsaro aka ajiye a gabanta. Tare da kunna ƙaton tv irin na office ɗin data baro da shima ke a jikin bango. Hoton yayunta da rahotannin da aka shirya na karya dan tsoratar da ita suka bayyana.

    Ta sauke idanunta dake cike da ƙwalla a hankali bisa computer ɗin gabanta. 

       “Ki nutsu wajen yin aikin da zai ƙuɓutar da ƴan uwanki zama criminals zuwa taurari ta sanadinki, ko kiyi sakacin yin aikin da zai dusashe haskensu da ga taurari zuwa criminals ta sanadinki.”

    Mutumin ɗazu ya faɗa cikin tabbatarwa da murya mai kaushi.

     Kai kawai ta jinjina masa tana maijin wani ɗaci a zuciyarta da taurin zuciya. Sai da tayi addu’a a cikin zuciyarta kafin ta fara aikin cike da ƙwarewa. Kasancewar ɗazun dama ta binciko a inda suke sai yanzu batasha wahala ba duk da wannan Computer ɗin nada matuƙar tsaro fiye da tasu ta makaranta.

           Da wayar gabanta ta dinga amfani wajen yin magana da jami’an da suka fita operation ɗin tana sanar musu hanyoyin da zasu bi har zuwa location ɗin da agogon data jefama masu power bike jiya yake. Hakan shike nufin tabbacin samun su inhar agogon na tare da su basu farga sun yadda ba…….

★/★★/★★/★★/★★/★

                 Anguwar *_jahje street_*, anguwace mai ƙarancin rashin hayaniyar jama’a kasancewar ta ɗauke da manyan gidaje na masu hannu da shuni. Ko da rana ka shigo wannan anguwa zaka sameta tsit tamkar halittun da ke a cikinta basa numfashi. Akan samu ƙarancin gittawar ababen hawa da na mutane masu tafiya a ƙafa sai dai jefi-jefi. Shima hakan tafi kasancewa a ranakun hutun ƙarshen mako ko hutun ranakun ma’aikata da kan gitta.

          Sabo da rashin sakewarsu da juna yasa bazasu iya tantance kansu ba dan rayuwa ake ta babu ruwan wani da wani. Idan kaga magana ta shiga tsakaninsu sai idan ALLAH yasa ka fito maƙwafcinka ma ya fito ai gaisuwar hello hi shikenan kowa ya shige sabgar gabansa.

           A cikin gida mai lamba 110 matasan samari ne da shekarunsu zai iya kaiwa ashirin da biyar zuwa da shida, harma mai da bakwai za’a iya samu. Gaba ɗayansu bakwai zaune suke a ƙayataccen falon gidan mai matuƙar girma da ƙawa ga mai kallo. Su dukansu kowa harkar gabansa ya ke yi. Wasu na kallon ƙwallo, wasu na daga gefe suna sarrafa wayoyin hannunsu. 

       Ɗaya da ga cikinsu ya nutsu wajen sarrafa waya. Sai dai a hakan hira kan shiga a tsakaninsu musam akan kallon ƙwallon da mutum huɗu suka fi maida hankali a kansa.

        Wani mahaukacin horn daya nema harmutsa kwaƙwalensu da ga gate ya sakasu miƙewa a rikice gaba ɗayansu suna ambaton *_Master!!_*. Biyu da ga ciki suka shiga tattare ledojin dattin da sukai ciye-ciye tare da gwangwanen maltina da coc.. Ɗaya ya fita a guje domin zuwa ya buɗe masa ƙofar falon da ke rufe da security. 

          Buɗe ƙofar yayi dai-dai da isowarsa cikin takun ƙasaita da tabbatar da shiɗin fa ya isa. Sanye yake cikin baƙin wando jeans da baƙar t-shirt. Sai dai ya ɗora jacket baka itama a samanta batare da ya ja zip ɗinta ba. Sam ba’a ganin fuskarsa, sakamakon hular jacket ɗin dake har saman kansa, ga norse mask da baƙin google toshe da idanunsa. Ƙafarsa ma sanye take cikin baƙin takalmi.

     Cikin zafin nama da ALLAH yay masa yasa hannunsa da ke sanye cikin safar hannu ya matsar da wanda ya buɗe masa ƙofar ya shigo cikin falon.

      Hakan ya kara tabbatar musu da babu lafiya, dan kowa bai kalla a cikinsu ba ya nufi wata ƙofa a hargitse. 

     Kallon juna sukayi cike da tsoro, cike da ƙarfin hali ɗaya da ga cikinsu yace, “Brothers babu lafiya fa”.

       “Tabbas babu lafiya Khalid. Akwai abinda ya saka Master a wannan yanayi…..”

     Maganar tasa ta kakare a maƙoshi saboda fitowar wanda suke kira Master. Cikin wata irin murya mai amo da nutsuwa ya fara magana da faɗa. “Ina kayan da kuka fita aiki da su jiya?”.

      A tare sukai rige-rigen nufar ɗakunan barcinsu. Babu jimawa sai gasu suna dawowa ɗaya bayan ɗaya da kayan a hannu. Na’urar bincike da ke a hannunsa ya shiga kangawa jikin kayan. Akan jakkar Habib ta tabbatar da zarginsa. Ya fisgi bag ɗin da sauri yana zazzage dukkan abubuwan da ke a ciki, sannan ya ɗaura na’urar akan kayan. Saurin daukewa yay ya sake maidawa akan jakar. ƙaramin fuskar agogo mai kama da flower dake manne a jiki ta fara kawo jar danja tana ɗaukewa. Yay saurin fisge agogon da dudu-du girmansa bai wuce girman ficika ba. Numfashi ya fusga da ƙarfi, hakama sauran yaran nasa duk sai da sukai ajiyar zuciya. Dan abinda sukaga ya cire ɗin ya tabbatar musu wani ya kafa musu tarko ne ba tare da sun farga ba.

           Batare da yace dasu komai ba ya nufi na’urorin dake acan gefen falon an katangesu da glass na ƙawa daya zamewa falon baki ɗaya ado. Cikin wata na’ura ya saka agogon, bayan kamar sakan biyar ya cire ya fito ya nufi waje. Yana fita suka shiga kakkauda duk wani kaya suna maida shi a salon da zai basu kariya dan da alama yau ta ƙwaɓe.

       Baifi mintuna uku da fitarba sai gashi ya dawo. Hanyar ƙofar da ya nufa ya sakasu binsa da sauri suma dan sun kammala kauda dukkan abinda ya kamata su kauda ɗin. A kuma dai-dai lokacin sukejin ƙarar buɗe gate ɗin gidan alamar wanda suka sami nasarar bibiyar tasu sun iso. Sun kumafi ƙyautata zaton ƴan sanda ne abokan *_TAKUN SAAƘAr_* su………….✍

         

         *_Hum, wannan fa shine ana dara ga dare yayi🐒🚶🏻_*

*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI……_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_

_NISHADI_

_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*

*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300

2____400

3____500

4____700

5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*

   

Leave your vote

-1 Points
Upvote Downvote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like