Advertisement
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
Advertisements
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
_________________________
Advertisements
*_Chapter Twenty one_*
…………A matuƙar hargitse Abba ya samu gidan, da ƙyar ya iya kutsa kai ya isa ga su Hajiya mama da Garba kema bayanin yanda akayi. Saboda labarin yanda ɗaurin auren ya kasance na faruwa Hajiya mama ta nufi sashen Ummi a hargitse zata fara zubar da tujara Garban ya dakatar da su.
“Sam ba laifin Asiya bane. Dan a wannan gaɓar tafi kowa cancantar aima jaje, a kuma tausaya mata.”
A fusace Hajiya mama ta juyi garesa kasancewar ɗa ne a gareta. dan kuwa ɗan ƙanwarta ne. “Garba har yaushe kasan makircin Asiya? da shaiɗancinta da zakayi ƙoƙarin kareta akan abinda yake zahiri. Ni dama nasan shurun da tai da yarda da wannan auren bana arziƙi baneba. To wlhy yau ɗin nan……”
“Inna ku saurareni”. Garba ya katse hajiya mama. A dai-dai lokacin kuma Abba ya iso da ƙyar garesu, dan illahirin ƙafarsa rawa ma take tamkar karayar tasa na neman dawowa sabuwa ne.
Garba ya cigaba da faɗin, “Sam ba laifin Asiya bane. Dan ba kowa ne ya canja ɗaurin auren nan ba sai shi yaron da ya auri ita Muhhibatu.
Cikin matuƙar mamaki hajiya mama ta ce,“Shi Shuraim ɗinne ya canja ɗaurin auren? To a dalilin mi zaiyi hakan?”.
“Wlhy Inna nima ban saniba. Sai dai gaskiya kunyi ganganci haɗa auren yarinyar nan da yaron. Dan hatsabibin mutumne fiye da hasashen mai hankali. Na tabbatar da hakan da idanun. Shine ya hanani kiran Yaya Halilu. Ya tsaramin abinda naje na sanarma Sheikh Aliy. Ya tsoratani da inhar banyi yanda yake so ba zai kasheni. Ya nunamin mutanensa da ke a kowace kusurwa na cikin massallacin, wanda alama kawai zai musu numfashin duk wanda ke cikin massallacin ya dakata da aiki. Na tsorata matuƙa, dan nasan zai iya aikata abinda yafi haka. Mutumin daya iya zuwa muku da fuskar mutanen kirki ya yaudareku sai kasheni zai gagaresa. Hakanne ya sani bin umarninsa naje na faɗama malam yanda yace. Wlhy ban sake kiɗima ba sai da na tsugunna gaban malam ina faɗa masa wani yaro dake gefen malam ɗin ya ɗoramin bindika akan ciki batare da kowa a cikinku ya lura ba. Tayaya kuke tunanin zan iya ƙin bin umarninsa.”
Yaya Abubakar da zukatansu ke neman faso ƙirazansu su fito a rikice yace, “Uncle Garba kace shine Shuraim?”.
“Abubakar wlhy shine Shuraim, na tabbatar da shi kuka ɗaurama ita wannan yarinyar Muhibbatu aure”.
Ai gaba ɗaya wajen ya sake ruɗewa. Ummi tai baya zata faɗi sai da Hajiya Mardiyya ta tarota. Abba kam wata mummunar hajijiyar ruɗani ce ke neman zubar da shi shima. Yayinda wani tsoro-tsoro firgici-firgici ya sashi fara waige-waige tamkar Shuraim ɗin na tare da su a wajen.. Abinda bai ganeba anan, miyasa Shuraim zai dakatar da ɗaurin auren ƴaƴansa da su Usman? Tunda gashi ya cika umarnin aikin auren ita Muhhibat?. Wayarsa ya shiga lalube yana ƙoƙarin fita a wajen.
A.G ya kira, wanda sai da tana gab da tsinkewa ya ɗaga cikin ɓacin rai. “Malam miye kuma na kiran….?”
Katseshi Abba yay da faɗin, “Ko kasan Master ne ya rusa ɗaurin auren ƴaƴana bayan shi an ɗaura nasa da yarinyar nan”.
Cikin taɓe baki A.G yace, “To kai mi kake tunani? Kasan dai shi baya abu da ka, zata iya yuwuwa akwai dalilinsa nayin hakan, dan kawai ya bada ƙafa kamar yanda ya saba”.
“Ina ba haka banee!!”.
Abbah da ke a birkice ya faɗa cikin matsananciyar tsawa.
“Ya kake min ihu haka ne? Alhaji Halilu?”.
“Ya bazan maka Ihu ba bayan kai ne ka tsara komai…..”
“Muka dai tsara, tunda komai da yardarka akayi, a kuma gabanka bawai a boye ba.”
Abba ya buɗe baki zaiyi magana A.G ya katsesa da faɗin,
“Kaga ina zuwa gashi ana kirana da ga office. Zan kiraka”. Bai jira cewar Abba ba ya yanke kiran dan ogansa ne ke kiran nasa, da alama tsiyar da Master ya tafka harta fito kenan. Wani irin ƙarajin baƙin ciki Abba ya saki shi kaɗai a ɗakinsa, ji yake tamkar ya rotsa wayar tasa da ƙasa kawai ya huta. Jikinsa kansa ta ko’ina rawa yake da tsatstsafo da zufa, kansa ya kulle ya kasa fahimtar komai game da abinda Master ya aikata.
Hargitsewar gidan yasa babu wanda ya farga da rashin Hibbah. Dan ita kanta Ummi ƴaƴanta nacan zagaye da ita kowa nason ganin hankalinta ya dawo jikinta. Yayinda acan tsakar gida Hajiya mama ke doka rantsuwa tana direwa akan sam bata yarda ba wanann shirin Ummi ne da ƴaƴanta. Tabbas sune suka saka Shuraim ɗin yayi haka. Da yawan mutane maganar Hajiya maman tayi tasiri a garesu, musamman da ya kasance alaƙar Hibbah da Shuraim ɗin kawai kowa ke kallo a zahiri da kuma ɗaura auren su Yaya Muhammad da wasu matan daban alhalin su su Hajiya mama basu san da zancen ba sai yanzu da aka ɗaura.
Gidan ya ruɗe sai cece kuce ke tashi ta ko ina. Kowa na faɗin albarkacin bakinsa da hasashen zuciyarsa.
Cikin ƙarfin hali Ummi da tun fara tujarar Hajiya Mama yaranta suka kamata suka shige ciki da ita ganin yanda duk suka tattara kansu gareta ta haɗiye tashin hankalinta da ruɗani tana mai duban su Yaya Usman ɗin da su kansu bawai suna cikin cikakken hankalinsu bane akan al’amarin. Kan Yaya Abubakar da ke kusa da ita ta dafa tana murmushi. “Har yanzu zuciyata ta kasa daina yimasa ƙyaƙyƙyawan zato. Dukkanin cikamakin kamala da mutunci a bayyane suke garesa, shiyyasa nai saurin aminta da aura masa Tanee. Amma ta yaya fari zai koma baƙi a wanan ranar?, bayan har yanzu idanuna da zuciyata sun ƙi kallon komai da baƙin”.
Cikin taraddadi da jan gwauron numfashi Yaya Abubakar yace, “Dama nasan hatsabibin nan bazai ƙyale Hibbah ba. Dan ta masa tabo irin wanda bazai gogu a cikin tarihinsa ba. Hakan yasani yarda da amincewar aima ta aure ko zata kuɓuta daga garesa. Ashe mun riga mun daɗe da kasancewa cikin lissafinsa, ko tantama banayi akan lallai shu’umin nan Master ne yazo mana da fuskar Shuraim. Sai dai ina mamaki matuƙa ta yanda ya kuɓutar da mu daga auren waɗan nan yaran. Mi hakan ke nufi ne?”.
Ammar ya ɗago kansa da ga ɗorawar da yay bisa cinyar Ummi a firgice yana faɗin, “Yayamu Master fa kace? Gawurtaccen ɓarawon da kuke nema ruwa a jallo ko wa? Danni ban gane ba”.
Numfashi yaya Abubakar ya fusga da ƙarfi yana jinjinama Ammar kai alamar tabbatarwa. Tare da bin fuskokin sauran ƴan uwansa da suma ruɗanin ne ƙarara ya bayyana akan fuskokinsu har suka gaza motsawa.
Cikin ɗan rawar jiki Ummi tace, “Abubakar mi kake faɗane haka? Kana nufin yaron kwanaki da ƴan sanda suka sakata tai aiki akansa?”.
Yaya Abubakar da shi kaɗai yasan lissafin da zuciyarsa keyi ya ɗan firzar da numfashi yana ciza lip ɗinsa na ƙasa da duban Ummin tasu cike da kulawa. “Ummi ki kwantar da hankalinki. Babu abinda zai samu Muhibbat da izinin ALLAH…..”
Da sauri Ammar ya amshe zancen da faɗin, “Ummi mugodema ALLAH ma da kafin a kaita gidansa ne komai ya fito. Yanzu kunga ko a kotu ne a raba auren kawai sai a bama Yaya Isma’il dama sunfi dacewa”.
Sosai maganar Ammar ɗin tai tasiri a garesu har Yaya Muhammad ya shafa kansa yana ɗan murmushi.
Yaya Abubakar kam ɗago kai yayi ya kallesa tamkar wanda zancen yayma allura. cikin nazarin furucin na ammar, ya ɗan kaɗa kai yana jujjuyawa, dan baya son faɗar abinda a yanzu zuciyarsa ke hasko masa kai tsaye saboda Ummi. Miƙewa yay yana faɗin, “Komai ma da baƙwa tunani zai iya yi. Sai dai inaji a jikina Muhibbat ce tarkonsa a wannan karon”.
“Yaya Abubakar kana nufin zai cigaba da bibiyar auta?”. Cewar Usman a tsorace yayinda duk suka bisa da kallo har Ummi.
Numfashi Yaya Abubakar ya fesar yana gyaɗa kai dai-dai yana ƙoƙarin kaiwa ƙofar fita. “Bazaka gane lissafinba Umar. Ku dai da ga yanzu dukkanin idanunku su kasance akan Muhibbat ne. Dan duk yanda kuke tunanin wanann shu’umin mutumin yafi ga haka. tabbas bazai taɓa bayyana kansaba bayan bai gama tsara yanda komai zai tafi masa ba.”
Da kallo kawai suka bisa harya fice yana ƙoƙarin kai waya bisa kunnensa. Da alama kira yayi. Kafin Ammar ya miƙe yana faɗin “bara na nemota itama.”
Kai kawai suka iya jinjina masa, dan jikin kowa ya gama sanyi a cikinsu.
★★★★
A ɓangaren su Musbahu kam koda suka iso L.E street. Habib ne ya shiga sanarma ogan nasu isowar tasu, duk da kuwa sarai yasan yaji.
Zaune ya sameshi ƙafa ɗaya kan ɗaya a katafaren falon nasu da yaji kayan more rayuwa yana sarrafa system da ke saman cinyarsa. Duk da yaji shigowar Habib ɗin bai ɗago da ga abinda yake ba, sai dai ya amsa masa sallamar akan laɓɓa.
Habib da ya ɗan kallesa ya risinar da kansa ƙasa da girmamawa yace, “Barka da hutawa Master”.
Uffan baice ba, bai kuma ɗago ya kalli Habib ɗin ba har tsahon wasu sakanni, sai dai ya jinjina kansa alamar amsawa.
Habib da ya fahimci ƴan mulkinne a kusa yau sai kawai ya cigaba da magana. “Aiki ya kammala, itama gata tare da mu”.
Dakatawa yay da ga sarrafa lap-top ɗin, a hankali ya ɗago idanunsa cike da ƙasaitarsa ya saukesu kan Habib ɗin da ya nutsu waje guda saboda tsabar girmamawar da suke bashi.
Kallo daya yay masa ya janye idanunsa ya maida akan system ɗin da faɗin, “Su Salis?”. Yay maganar a taƙaice cikin sigar tambaya”.
“Dukanmu tare muka shigo”. Habib ya bashi amsa.
Lap-top ɗin ya ajiye ya miƙe, batare da ya sake cema Habib ɗin komai ba ya nufi hanyar fita cikin takun da ke nuna cikakkiyar lafiyarsa da nutsuwar da ALLAH ya azurtashi da ita.
Shima Habib bayansa yabi da saurai suka fita a kusan tare. Kallo ɗaya yay ma su Salis da ke ƙoƙarin fitowa a mota ya ɗauke kansa da cigaba da tafiya cikin izza da ƙasaitarsa tamkar wani jinin mulki.
Dai-dai yana isowa inda suke suka haɗa baki wajen faɗin, “Barka da gida Master”.
Hannu kawai ya ɗaga musu yana nufar motar da Habib ya fita da ita. Da sauri Habib ya buɗe masa motar ta sashin da Hibbah ta ke yana matsawa gefe tamkar yanda sauran suka nutsu.
Duk da yasan a sume take hakan bai hanashi sake ɗaure fuska ba kafin ya sauke nutsatstsun idanunsa masu kaifin gani a kanta. Sai kuma ya ɗan kaudasu tare da ƙarasa takawa gaban motar da ƙyau yana yamutse fuska. Dai-dai lokacin da yake ranƙwafawa su Habib suka kalli juna, yana ɗagowa ɗauke da Hibbah suka waro idanu waje da saurin maida kawunansu ƙasa.
Ko kallo basu ishesa ba, sai ma sake tamke fuskar boginsa da yayi ya shiga taku cike da izzarsa da kasaita zuwa cikin gidan ɗauke da Hibbah da batasan wainar da ake toyawa ba.
Idris ya haɗe yatsunsa waje guda alamar love yana wani cije baki. Sauranma idanu suka shiga kashewa da yin alamar nice👌🏼 cike da shaƙiyanci.
Tsaf yaga duk iya shegen nasu ta glasess ɗin windows. Ya ɗan ciji lip ɗinsa na ƙasa da tura ƙofar falon da ƙafa. Hakan ya saka su Khalid saurin mara masa baya gudun yin laifi.
Koda ya shigo falon up stairs ya nufa, anan ma falo ne babba masha ALLAH, wanda babu abinda baijiba na kayan more rayuwa. Sai tashin ƙamshi yake ga sanyin ac mai saka nutsuwa. Kai tsaye ya nufi ɗaya da ga cikin bedroom ɗin da ke a up stairs ɗin. ya shimfiɗeta saman gadon ɗakin yana wani sake ɗaure fuska da yamutseta irin shifa ya gajin nan. Ya ɗan zubamata harara yana janye jikinsa. Wayarsace ta fara tsuwwa alamar shigowar kira.
Sharewa yay tamkar bazai amsa ba. Sai da ta na gab da tsinkewa ya zarota a aljihun wandon baƙin jeans ɗin jikinsa yana jan siririn tsaki da jingina jikin mirror ɗin ɗakin yana kaiwa kunnensa batare da ya ce uffan ba, sai dai shirun nasa na nuna alamun sauraren mai magana ya ke da ga can. Tsawon minti biyu da wasu sakanni ya ce, “Uhmm” da ɗan gyaɗa kai.
Dai-dai nan akai Knocking ƙofar a hankali, kasancewar sun san idan yana a irin wanann yanayin duk wata hayaniya baya buƙatarta.
Cikin ƙosawa da motse-motsen kuwa ya bada izinin shigowa yana janye wayar a kunnensa………..✍
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI……_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*
*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
GIPHY App Key not set. Please check settings