TAKUN SAKA 35

Advertisement

 *_Typing📲_*

*_Zafafa biyar na ku

ɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

Advertisements

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

_________________________

*_Chapter Thirty Five_*

……….Yaran A.G sun gama bincike ko ina babu Master da Hibbah a gidan. Sai da ga ƙarshe A.G ya farga da bin jinin da Master ya dinga zubarwa har cikin kitchen. Yay tsam yana auna inda jinin ya tsaya ya kuma zuba da yawa. 

Advertisements

     “John!”.

Ya kira sunan ɗaya da ga cikin yaran nasa cikin da ka tsawa. A guje sukazo. Batare da yayi magana ba ya nuna musu p.o.p yana zaro waya aljihu. Cikin ƙanƙanin lokaci suma suka shige cikin p.o.p ɗin. Koda suka shiga suma ta cikin bututun sukabi suna sanar masa abinda suka fahimta. Sai da suka ɓilla har ta wancan gidan sannan suka sanar masa ta waya.

        Wasu yaran ya bari anan ya fito ta cikin layin, gida uku ne tsakanin gidan da inda su Master suka zauna.

       “Lallai guy ɗin nan ya cika matsiyaci shu’umi. Kaga shege kamar wani kurege ta ko’ina fasa hanyoyi yake.”

      Ɗaya da ga cikin yaran A.G ya faɗa rai a ɓace. Komai A.G bai iya cewa ba. Dan zuciyarsa tabbas tana gab da fashewa a cikin ƙirjinsa. Jin shigowar wasu ɓangarori na jami’an tsaro cikin layin ya sakashi fita. Cikin ƙanƙanin lokaci anguwar ma baki ɗaya ta gama hargitsewa. Bakaji da ganin komai sai jami’an tsaro da ƴan jaridu. Kowa burinsa yaji wani abu da ga bakin su A.G da suka fara zuwa wajen. Sai dai ina komai ya kasa fita da ga bakin A.G. da ga ƙarshe ma zare jikinsa yay ya baro anguwar saboda kiran da Alhajin Mande yay masa akan ya maza yazo inda suke tunda zancen guduwar master harta sake bazuwa cikin ƙanƙanin lokaci.

         Gaba ɗayansu sun hallara ne a gidan hutun Dr Sufi, duk da kuwa kiraye-kirayen wayoyi da suketa samu daban-daban akan neman tabbacin kuɗaɗen da akace Master ya wawasar musu. R.D na zaune yana rusar kuka kamar ƙaramin yaro shi da Alhaji Sallau. A.G na shigowa R.D ya miƙe ya nufesa cikin rawar jiki. 

      “A.G an kamashi?”.

A.G da shima kusan kan nasa so yake ya juye ya girgiza masa kai.

       Kuka R.D ya sake fashewa da shi saboda tsabar tashin hankalin da yake a ciki. “A.G ya nakasta min rayuwa ya yasheni matsiyacin nan. Naira dubu hamsin kawai ya barmin a accaunt tsinannen……”

         “Kowa ma abinda ya bar masa kenan R.D. yanzu ba lokacin zaman kuka bane ko jajantama juna. Lokacine na himmar cimma rayuwarsa dan baiyi nisa ba. A yanzu haka na baro cikin gidan da yake ne saboda kiran da kukaimin. Amma na bar yarana duk da kuwa ya gudu. Yarinyar nan ta wajen Halilu ne ta tona asiri. Amma abinda ya bani mamaki da ga ƙarshe bayan mun tarfasu a cikin gidan duk da abinda tai masa shine ya ringa bata kariya daga harbin dana saka ai musu, sai shi harbin yayta sama shi a dole jarumi”

       “Dan ALLAH da gaske kun harbeshi!!”. Engineer yay maganar tamkar wani zararre. Dan alamu ma sun fara nuna kamar notin kan nasa ya fara kwancewa shima fiye da nasu R.D ɗin”.

      A.G ya kaɗa masa kai cikin tabbatarwa. “Tabbas mun harbesa. Sai dai harbin duk ya samesa inda bazai mutu ba…….”

      Cikin katse A.G Alhajin Mande yace, “Idan matsiyacin yaron nan ya mutu yanzu to ai muma mun mutu A.G. dolene yaƙinmu ya kasance na dawowar dukiyarmu hannunmu harma da wadda muka sakashi ya tara. Kafin mu walakanta rayuwarsa da duk ma wanda ya shafesa. Tunda har ya bama yarinyar kariyar hakan na nufin yana sonta kenan, dan nidai nasan baida imanin da zai kareta batare da soyayya ba…….”

         “So! Kuma? Kai gaskiya bana tunanin haka”.

   Cewar Dr Sufi cikin kokwanto.

           Tsaki Alhaji Sallau yaja da faɗin. “Dr Sufi kana mamakin wacece mace. Duk wani shaiɗanci da kake ganin matsiyacin yaron nan ya iya bazai saka ya kasa shiga kaidin mace ba. Ai ni tun randa akace ya ruguza auren ƴaƴan halilu nakeji a raina akwai wata a ƙasa. Shiyyasa ban zauna ba sai da na gano inda ƴan uwan yarinyar suka koma yanzu haka. Jiya-jiya aka kawomin bayanan dama a meeting na weekend ɗin nan naso kawo zancen dan mu masa tarko da su koda yaso aikata cutarmu, to ashe shaiɗanin ya gama shirya mana tsaf.

      A zabure A.G yace, “Da gaske ka samo inda suke?”.

     “Tabbas kuwa bar kokwanto A.G”.

Alhaji Sallau ya faɗa yana zaro waya a jikinsa.

     Wata shegiyar dariya A.G ya sanya da faɗin, “Tabbas Master kazo hannu dan uban babanka. Dan da yarinyar zamuyi amfani kazo garemu. Yanda take son ahalinta muna damƙesu kaima bazata barka ka shaƙi numfashi lafiya ba”.

     Fahimtar gaskiyar zancen da manufarsa ya sakasu jin wani ɗan karen sanyi na ratsa zukatansu. A take suka gama aminta da zuciyarsu cewar Master yazo hannu ya gama kawai. Dan Alhaji Sallau na gama basu adireshin su Ummi A.G ya kira ya ransa ya basu Umarnin binsu Yaya Umar har wajen ayyukansu a kamo masa. Hakama su Ummi.

(Tabbas Master kayi gaskiya akwai matsala🙆🏻🤦🏻🚶🏻)

__________________________

            Ummi da surukanta gaba ɗaya na a sashenta suna hira kamar yanda suka saba zuwa mata a kowanne safiya su ɗan zauna bayan fitar mazajensu, matar Yaya Umar ta fara ganin abinda ke faruwa awayar hannunta. Cikin waro idanu waje take faɗin, “Tabɗi jan, shahararren ɓarawon nan yau ma ya sake guma uwar satar datafi ta kowanne lokaci a tarihi”.

      Kusan a tare suka haɗa baki wajen tambayar waye?.

     “Master mana. Gashi bbc ma har sun saki”.

     Ta basu amsa kanta tsaye. Gaban Ummi ne ya faɗi dan a saninta dai na yanzu Isma’il shine Master. Kafin ta samu damar cewa wani abu Zahidah tace, “To bara mu kunna television”. Batare da jiran amsaba ta dauka remote ta kunna. Cikin sa’a kuwa ana tsaka da nuna rahoton ne dan kowanne gidan tv da na redio shine latest labarinsu na yanzu-yanzun nan da gaba ɗaya ya hargitsa ƙasar dama duniya. Dan anyi itifaƙin bai taɓa mahaukacin sata makamancin na wannan karon ba ma. Ya yashe asusu goma sha ɗaya a lokaci guda. Asusai kuma masu matuƙar nauyi na kuma manyan mutane da ake matuƙar ganin mutuncinsu cikin dattijan ƙasa. Harda jami’an tsaron da ke farautar rayuwarsa.

       Hankalin Ummi bai gama tashi ba sai da taji sabon rahoton da ɗan jaridar ke faɗa cewar a yanzu haka labari yazo musu wata matashiyar budurwa da Master yay garkuwa da ita  ta samu nasarar tona masa a siri ta hanyar kiran wayar ƴan sanda ta sanar musu a inda ya ɓoyeta. Sun sami labari kuma a majiya mai ƙarfi a yanzu haka ƴan sanda sun zagaye gidan inda suke da tabbacin Master yana ciki shima. 

     Karkarwa jikin Ummi ya farayi, ta ɗauka waya da nufin kiran layin yaya Abubakar taji tabbacin zancen, sai ga ƴan sanda sun faɗo musu su huɗu. A razane duk suka miƙe da ɗaga da yin surrender, dan bindigu duk suka nuna musu. 

     “Duk ku fita!!”.

Ɗaya da ga cikin ƴan sandan ya faɗa cikin daka tsawa. ALLAH ya taimakesu dukansu akwai hijjabai a jikinsu har Ummin, dan basu iya zuwa su zauna mata babu hijjab ko mayafi. kamar yanda itama idan suka shigo bata taɓa zama cikinsu babu mayafi ko hijjab tare da ita. Haka suka fita cikin matsanancin tashin hankalin rashin sanin laifinsu. Da ga su sai wayoyin hannunsu. A cikin mota guda aka zuba su Ummi. suma ƴan sandan suka shiga tasu.

★★★★

      A ɓangaren su Yaya Muhammad ma suna wajen ayyukansu cikin tashin hankalin abinda suka gani a labaran daketa yawo a wayoyin hannu. Zukatansu sun gama basu Hibbah ce ta tonama Isma’il asiri. Duk da suma har yanzu basu san ainahin gaskiyar dalilinsa na aikata waɗan nan abubuwanba hakan bai musu daɗi ba. A daren shekaran jiya yake sanar musu akwai aikin da yake kanyi yanzu haka, yana kammalawa zai kawo Hibbahr ta gaida Ummi. Sai gashi koma ya hargitse tunda gashi suma ta shafesu.

      Dan batare da sun san nasu laifin ba suma dai sai ga ƴan sanda sunzo kamasu suma. Hatta da Yaya Abubakar da ke matsayin jami’in tsaro suna tsaka da kai kawo akan abinda ke faruwar kawai akazo akai arresting ɗinsa. Ƴan sandan dake station ɗinsu sun so ɗaga hankalinsu Yaya Abubakar ɗin ya kwantar musu da hankali yabi jami’an farin kayan da sukazo kamasan. Dan shima a ransa yanason zuwa kodan wani bincike.

★★★★★

         Kusan awa ɗaya kenan da barin su Habib gidan amma babu su babu labarinsu. Gaba ɗaya su Idris sun kasa zaune sun kasa tsaye. Sai kaiwa da kawowa suke a falon hankalinsu nakan wayoyinsu suna ganin abinda ke faruwa ta yanar gizo. Basu kunna tv bane saboda fahimtar gaba ɗaya Master baya buƙatar wata hayaniya. Dan tun korar Hibbah da yay a wajen ya maida idanunsa ya lumshe kai kace barci yakeyi. Koda Khalid ma ya tambayesa ko zaisha tea bai tanka ba dan yayi zurfi matuƙa a tunani.

       “What!!?”

Khalid dake rike da waya a hannu ya ambata yana mikewa tsaye a zabure cikin alamun gigita. Idris dake zaune gefensa yay saurin dubansa da faɗin. “Lafiya?”.

      “Inafa lafiya!, wai kaji mi matsiyacin A.G ɗin nan ke faɗama ƴan jarida kuwa akan alaƙar Master da aunty queen?!”. 

        Hannunsa ya janye a kansa da ke masa tsananin ciyo, tare da buɗe lumsassun idanun ya sauke akan  Khalid da yay maganar. Kafin Idris dake ƙoƙarin buɗe baki yay magana yayi ɗin ya katsesu.

       Cikin muryarsa da ke a shaƙe na mura da tsananin ɓacin rai ya ce, “Television”. 

       Kai Khalid ya jinjina masa da ajiye wayar hannunsa ya ɗauka remote ɗin tv ya kuna. Hakan kuwa yayi dai-dai da hasko A.G da ke bayani ga ƴan jarida, da alama yabar wajen su alhajin Mande ya koma office.

            “Tabbas har yanzu babu wanda yasan fuskarsa. Saboda yana amfani da facemasks iri daban-daban idan zai aikata laifinsa. Misali kamar yau an samu fuska biyu da yaje banki da ita, inda mutane da yawa suka tabbatar da sun gansa a matsayin alhajin ƙauye daya shigo bankin tankar baisan komai ba. Sai a yanzu ne kowa ya fahimci shine yay shigar ɓurtu tamkar yanda ya saba. Tabbas mun bibiyesa adalilin yarinyarsa kuma har mun sami nasarar harbinsa. Sai dai yanzu-yanzun nan muke samun labari a majiya mai ƙarfi dangane da ita yarinyar da tai kiran ta sanar da inda yake. matarsa ce, soyayya sukai kuma kafin aure. Hakan na nufin ahalinta sun san wanene shi suka ɗauketa suka bashi. Dan a yanzu haka zancen da nake muku harda ƙanin mahaifin ita yarinyar dake dauke da ɗawainiyarsu tun suna kanana saboda mahaifinsu ya rasu suka yashema asusu. Kenan hakan na nufin harda ita a cikin tawagar tasa…….”

        “Amma yallaɓai idan harda ita mi zaisa ta tona masa asiri?”.

    Wani yayma A.G tambayar cikin katsalandan na ƴan jarida.

        A.G yaja numfashi, “Muma wannan itace tambayar da muke nemawa amsa. Sai dai a ganina kawai sun shirya mana wasa da hankaline kawai sai suka rufta..” 

       “Kenan dama kuna bibiyar al’amuransa a koda yaushe?”.

     “Sosai ma kuwa. Dan bamu da burin daya wuce mu kamashi. Shiyyasa dare da rana muke tsaye tuƙuru akan dukkan motsinsa…”

       “Amma yaya akai duk da jajircewar nan taku harya samu nasarar yashe asusan bankunanku kuma a yau?”.

      A.G ya kafe ɗan jaridan da yay tambayar da ido har saurayin ya tsargu. Ganin sauran ƴan jaridar na juyawa suna kallon saurayin saboda kallon da yake masa ya sashi basarwa yana sakin murmushi. “Tambaya mai ƙyau. Sai dai zan bada amsartane anan gaba bawai yanzu ba…”

       “Tabbas zaka amsata kuwa! Koda su sun manta ni Isma’il Aliyu Hikima zan sakaka ka amsata!!”.

      Master ya faɗa cikin wani irin kaushin murya da ɗaci yana sake maida idanunsa ya rufe. A haka ya cigaba da sauraren A.G daya ke tabbatarma da duniya a yanzu haka sun sami nasarar tattaro ahalin Hibbah, dan sune kaɗai zasu iya faɗama duniya a inda master yake a yanzu.

       Cikin tashin hankali su Khalid ke duban Master daya maida idanunsa ya rufe. Sun san sarai yana jin A.G ɗin shima. “Innalillahi…. Boss akwai matsala kenan”.

     Bai motsaba, bai kuma tanka ba duk da yaji abinda Idris ɗin yace. sai dai faman taunar lip ɗinsa yake na kasa alamar zuciyarsa na masa zafi da ciwo. Dan tsabar yanda yake taunar lip ɗin har ya koma jaa sosai.

         Shigowar baba saude da ke faɗa musu Hibbah fa babu lafiya jikinta sai rawa yake ga kuma zazzaɓi ya sakashi buɗe idanu a hankali. Kallon baba Sauden kawai yakeyi yana cizar lip. Su Idris kam duk sun zabura kan baba saude suna tambayarta miya sameta? ba yanzu ta shigaba lafiya lau.

     “Gaskiya inaga firgici ne. Da alama bata taɓa gamo da makamancin wannan tashin hankalin ba. Tunda ta shiga fa sai surutai takeyi. Maida idanun yay ya lumshe, gaba ɗaya kansa ciwo yake masa tamkar zai buga.

       Jin yaƙi cewa komai yasa sukai tsuru-tsuru suna kallonsa. Musamman ma su Khalid. Ganin haka yada Baba Saude takowa ta ƙaraso inda yake. Cikin taushin murya tace, “Babana ko jikin ne?”.

     Idanunsa ya sake buɗewa, yanda suka sake kaɗawa sukai ja har kamar suna ƙyallin ruwa sai ka ɗauka kuka yake. Yay ɗan murmushi mai ciwo yana girgizama baba sauden kansa. 

       “Naji sauƙi baba, kice mata tazo nan”. Yay maganar acan ƙasan maƙoshi cikin rauni da ɗacin dake addabar zuciyarsa da maƙoshinsa.

        Baba saude da gaba ɗaya itama zuciyarta ta ƙara raunana. Ta kaɗa masa kai da juyawa ta koma. Babu jimawa kuwa sai gata ta fito riƙe da hannun Hibbah da kallo ɗaya zakai mata ta baka matuƙar tausayi. Duk ta susuce ta firgice. Cikin ƙanƙanin lokaci idanunta sun kumburo matuƙa, jijiyoyin kanta duk sun miƙe ruɗu-ruɗu. Duk da haushinta da su Khalid ke ji sai wani irin tausayinta ya kamasu. Suka shiga jera mata sannu cike da damuwa. Bata iya ta amsa musu ba, dan gaba ɗaya a yanda Hibbahn take ta fita hayyacinta ba lallaine ma tana fahimtarsu ba.

      Shi kansa master tunda baba Saude ta zaunar da ita gefensa ya buɗe idanu ya kalleta sai da tsigar jikinsa ya tashi. Yaja numfashi batare da ya ce komai ba ya maida dubansa ga baba Saude. “Baba kije abinki kawai”.

      “To babana, amma babu wani abinda kuke buƙata?”.

     Kansa ya jinjina mata kawai. Sai kuma ya maida dubansa ga su Khalid.  “Tea da bargo”. Ya faɗa a taƙaice dan baya son yawan maganar. 

     Cikin sauri Khalid ya nufi inda yake tunanin kitchen ne. Idris kuma ya nufi bedroom. Sai da duk suka shige ya maido dubansa gareta, batare da yace mata komai ba ya ɗaura hannunsa mara ciwon saman goshinta. Zafin da ya ratsa masa hannu ne ya sashi cije lip yana janyewa ya maida kan wuyanta. Ɗan zabura tai dan abin yazo mata a bazata duk da taji sanda ya taɓa goshin. Baice komai ba ya janye hannun. Hakan yayi dai-dai da fitowar Khalid ɗauke da babban bargo mai laushi. Zai warwaresa Master ɗin ya girgiza masa kai. Dai-dai nan shima Idris ya dawo ɗauke da shayin. Saman table ɗin ya ajiye yana jawosa gaban master ɗin duk da ya fahimci na Hibbah ne.

         Zamansa ya ɗan gyara yana riƙo hannunta, a ɗan zabure ta buɗe idanunta, kallon cikin idonsa da tai a mistake ya sakata saurin maida idanun ta rumtse hawaye masu zafi na silalo mata. Ɗan jawo hannunta da yay ne ya sata matsowa jikinsa dan gaba ɗaya a firgice take da shi da komai ma. Fahimtar hakan da yay ne ya sakashi kwantar da kanta a kafaɗarsa. Ta ja wata nannauyar ajiyar zuciya na tabbacin babu abinda tafi buƙata kamar ɗumin jikin uwa. Ganin haka yasa su Khalid barin wajen.

        “Bana son kuka”.

Ya faɗa acan ƙasan maƙoshin da yasa ita kaɗai ta jisa. Haɗiye kuka ta shigayi tana jan tagwayen ajiyar zuciya. Dan tunda ya ɗan jinginata da jikinsa tsinkewar da zuciyarta ke mata ya ɗan fara sassautawa. Hannu ya kai bisa fuskarta ya share mata hawayen yana faɗin, “Kinsan zuciyarki bazata iya ɗaukar duk wannan ba miyasa kika ƙirƙira?.”

      “Dan ALLAH kayi haƙuri”.

Ta faɗa tana fashewa da sabon kuka. Komai baice mata ba, sai kofi tea ɗin da ya ɗakko ya miƙa mata. Babu musu ta amsa ta hau sha, dan yau babu wata ƙofar samun damar masa gardama. Taso mata yake amma haka ta danne taita sha. Tana ajiye kofin tamkar jira sai ga amai. Ƙoƙarin barin jikimsa tai amma ya riƙeta. Tanata jujjuya masa kai alamar ya barta shi kuma bai fahimta ba. Sai kawai ta saki aman ya wanke musu jiki baki ɗaya.

         Da sauri su Khalid suka miƙe zuwa garesu. Hakan kuma yayi dai-dai da fitowar baba saude itama a firgice.

        “Dan ALLAH kayi haƙuri”. Tai maganar wani aman na yunƙuro mata, duk ta sake firgicewa, ta cire hijjab ɗin jikinta ta fara goge masa aman daya ɓatasa. Komai baice mata ba, sai riƙeta da yay ganin kamarma jiri na neman ɗibarta ta faɗi. Sai da ya tabbatar ta gama ya maida kanta kan kafaɗarsa ya kwantar. 

     Duban su Idris da ke ta faman jera mata sannu yayi, kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa. Mikewa yay riƙe da ita suka nufi bedroom duk da bayajin daɗi da ƙarfin nasa jikin shima. Har cikin bathroom ya rakata, bayan ya zaunar da ita ya haɗa mata ruwan ɗumi. Batare da yace mata komai ba ya fito ya barta.

      Da kallo tabisa wasu hawaye masu zafi na sake silalo mata. A ranta tana mamaki da tambayar kanta shi ɗin wanene shi?. Rashin mai bata amsa ya sakata fara zame kayan jikinta ta fara wankan batare da tunanin zai iya sake dawowa ba. A kiɗime ta waro idanu da saurin saka hannu ta kare jikinta tare da kaiwa tsugunne ganin ya turo ƙofar ya shigo kansa tsaye, shima da ga shi sai guntun towel.

       Ɗauke idanunsa yay da ga kallon da yay mata shima, kayan da ya cire na jikinsa data ɓata da amai ya ajiye yana ɗan jan numfashi a sarƙe………….✍

*_Kuyi manage da wannan, da hanau gara mannau😬🚶🏻_*

     

TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI……_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_

_NISHADI_

_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*

*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300

2____400

3____500

4____700

5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*

 

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like