Advertisement
*_Chapter Thirty Seven_*
……….Gaba ɗaya komai ya sake ɗaukar zafi a ɓangaren jami’an tsaro. Dan kuwa dai zuwa yanzu an tabbatar da ahalin su A.G suna hannun Master, sai dai kuma su su A.G sun tabbatar ma da duniya su Ummi basa tare da su. Kawai dai sun faɗa zasu kamasu domin master ya bayyana kansa. Kuma koda sukaje sai basu samesu a gidan ba kwata-kwata.
Wannan magana ta fara canja salon zantikan bakunan mutane harma da wasu a manyan masu fashin baƙi da ke faɗa aji na ƙasar. Da yawa suna faɗin anya kuwa babu wani abu a ƙasa da ke tsakanin su A.G da Master. Dan kuwa dai kalamansu suna kamanceceniya da wanda sukai amai suka lashe abinsu.
Master dai da duk keji da ganin komai bai sake ko tari ba. Tunda ya baje a falo dai ya duƙufa akan aikin da suma su Habib basu san na miye ba. Dan tundama suka shigo suka gaidashi duk sai suka koma ɗayan sashen inda yake kamar matsayin nasu har baba saude. Nan kuma ya zama nashine shi da iyalinshi su madam Hibbah mai zamani😜.
Har kusan sha ɗaya na safe baiga Hibbah ta fito ba, shi kuma tunda ya fito a ɗakin bai komaba saboda busy da yayi. Sanin dalilin rashin fitowar tata ya sashi aika Habib kiranta lokacin da ya kawo masu breakfast. Tana zaune bakin gado bayan tayi wanka ta shirya harda gyara ɗakin akai knocking ƙofar. Cikin sanyin murya ta amsa tana miƙewa. Habib da ke tsaye da ga waje ya faɗa mata saƙon Master.
Tamkar tana gabansa ta kwaɓe fuska zatai kuka. Sai dai sanin babu damar tsallake kiran yasata warware ƙaramin mayafin jallabiyar kanta ta naɗashi.
“Good morning”.
Habib ya faɗa fuskarsa sam babu walwala. Ɗago kanta tai ta dubesa a karo na farko. Sai dai kafinma tace wani abu shi yayi gaba abinsa. Idanu taɗan rumtse tana haɗiye abinda ya zo maƙoshinta ya tsaya mai ɗaci. Sai kuma jikinta ya sake yin sanyi dan sam bataso taga mutum yana fushi da ita. Ko sadda tana gaban Ummi inhar tai laifi akai mata faɗa takan yi kuka ta manta, amma inhar taga Ummi cikin ɓacin rai da yayyenta saita kasa zaune ta kasa tsaye. Shiyyasa a yanzu ma duk ta firgice da fushin Master duk da tasan itace mai gaskiya.
Advertisements
Koda ta iso falon tsaye ta iske Habib na tambayarsa a haɗa masa abinci. Batare da ya ɗago akan takardun da yake dubawa a hannunsa ba ya girgiza masa kai da faɗin, “Barshi ta zuba”.
Kai Habib ya jinjina masa. “Okay, bayan hakan babu abinda kake buƙata kuma?”.
Yanzun ma bai ɗago ba ya bama Habib ɗin amsa. “Da ga yanzu itace zata ringa komai anan sashin”.
Daɗi ya ratsa zuciyar Habib. Ya ɗan juyar da kansa gefe yana murmushinsa da ya kasa ɓoyuwa. Ya haɗiye hawayen da ke neman kufce masa tare da duban Hibbah da ke tsaye tana saurarensu, dan kalaman Master ɗin ruɗar da ita sukayi. Ita dake fatan ya barta ta koma ga ahalinta ake kuma ƙirƙirarma aiki. Kallon karki sake cutarmin da ɗan uwa Habib ɗin yay mata, cikin nuna alamar rauninsa da bata dukkan amana. Batare da ya furta komai ba ya juya ya fice a falon tana binsa da kallo harya fice……
“Amana ya baki, duk da bayada tabbacin zaki riƙe masa. Dan a farko sun baki dukkan yarda babu shakku ko ɗar game da ke, amma sai kika sauya musu tunani….”
Master yay maganar har zuwa yanzu idanunsa da hankalinsa naga lap-top ɗin da takardun hannunsa. Idanunta dake kallon ƙofar har yanzu ta lumshe a hankali hawaye masu ɗumi suka ziraro mata. Takai tsugunne gabansa, “Nima iyayena sun yarda da kaine suka baka aure na da tabbacin bazakaci amanarsu ba amma sai kaci Yaya Master. Ka tausaya musu dan ALLAH dan Ummi na da ƴan uwana sunada rauni a kaina tamkar yanda ƴan uwankama kai ne rauninsu. Nima sune dukanin hope ɗin rayuwata. Bani da kuɗin dazan baka sama da wanda su Abba suka baka akan musu aiki. Sai dai inada kalaman roƙo da ban haƙuri a gareka kaji tausayin maraicinmu. Dan ALLAH a wannan gaɓar ka barni na koma ga ahalina su auramin wanda zuciyarsu tafi so da nake da tabbacin bazaici amanarsu ba……”
Tunda ta fara magana bai ɗagoba bai kuma daina uzurin gabansa ba sai yanzu. Idanunsa da har yanzu suke da kalar ja ya ɗago ya zuba mata. Duk son danne ɗacin dake kan harshensa da yayi ya gaza sai da ya bayyana acikin muryarsa. “Wanene shi?”.
A yanda yay maganar ne ya saka Hibbah ɗagowa ta kallesa cikin mamaki. Amma ganin ita ɗin yake kallo shima sai tai azamar maida kanta ƙasa cikin suɓutar baki da fashewa da kuka tace, *_“Yaya Isma’eel!”_*.
Numfashi Master ya fesar a hankali da lumshe ido….
Hibbah da bata san yanayi ba ta cigaba da faɗin, “Yaya Isma’il ya kasance abin alfaharinmu a tun farkon haɗuwa. Sannan shi abin so ne ga ahalina, sun so inama ace shine ya zama zaɓina tun farko, sai dai kash yazo a makare. A makaren da ka rigada kaima rayuwata kutse da yazo bisa alƙalamin ƙaddara ta, sai dai inaji zuwa yanzu a zuciyata tamkar bai makara ba. Gani gabanka gwiwa biyu ina roƙonka domin daraja da rahamar wanda ya haliccemu dan mu bauta masa, ka sawaƙemin aurenka dake kaina ka kuma maidani garesu. Sannan kayi haƙuri akan kuskuren da nai jiya gareka, nima bani da wani zaɓin da ya wuce hakan ne. Ahalina na cikin tarkon masifar ƙanin mahaifinmu, kai kuma ka kawoni nan ka ajiye kana musu aiki bayan suma burinsu ka kammala musu aikinne su ɓadda rayuwarka. Bazan tambayeka miyasa kake biye musu ba, sai dai zan sanar da kai kaima ba komai bane a garesu, lokaci suka ajiye domin ka. A zahiri dai kanada ibada da kiyaye dokokin ALLAH, amma a baɗini kana saɓa masa da babban laifi da ƙazantarsa da muninsa yasa ko’a kan harshe yake da ɗacin faɗa. Miyasa ka zaɓi saɓa masa bayan ni’imar lafiya da yay maka, ya baka ilimin addini, ya baka damar tarbiyantar da marayu, ya baka dukiyar da kake ci kake sha kake tufafi da shimfiɗa abubuwan jin daɗin rayuwa. Yayo ka a musulmi da baya barin lokutan salla biyar su wucesa sai da kuskure. Kaji tsoron ALLAH ka barsu tun kafin kai ALLAH ya barka……”
Duk yanda yaso cigaba da abinda yakeyi hakan ya gagara, dan kalamanta ba zuciyarsa kawai suka daka ba jinin jikinsa da ɓargonsa suke daddatsawa da tsinkawa a lokaci guda. Batare da ya shirya ba bakinsa ya suɓuce wajen faɗin, “Miyasa kike tunanin Isma’il ya fini nagarta?”.
Duk da bawai cikin lallashi ko taushi yay maganar ba sai Hibbah ta samu kanta da sakin murmushi tana ɗan dubansa. “Saboda bai taɓa cutar da mu ba. Kullum burinsa ya bama Ummi da mu kariya a wajen azzalumi Halilu. Bai taɓa tunanin rabani da Ummi na da su Yaya Muhammad ba. Kana ganin kuwa akwai sama da wannan nagartar wajen ƙayatar da yarinyar dake neman mijin aure?”.
Advertisements
Shu’umin murmushi shima ya saki da maida kansa ga aikin gabansa batare da yace mata komai ba. Sai da yaja kusan mintuna uku harma ta fidda ran samun amsa sannan ya bata amsar batare da ya kalletan ba yanzun. “Duk manta da waccan nagartar ta Isma’il ɗin da tunanin mi nake aikatawar ki riƙe Muhammad Shuraim (MASTER) dan a yanzu shine ƙaddararki. Na baki damar farko da zaki iya komawa ga ahalinki amma bakici jarabawar ba saboda gaggawa da ci da zuci irin wanda ke kai rayuwar da yawan mutanenmu ƙasa. Ba ko mai ne akema TAKUN SAƘA ba. Kamar yanda bada kowa ake kafa tubalin ginin TAKUN SAƘA ba. Dakinyi juriyar bina a yanda na ɗoraki da yanzu ba wannan matsayin muke ba. Amma zan miki alfarma a karo na biyu, zakije ga ahalinki, sai dai da sharaɗin tsarabar JINI NA”.
Hibbah da sam bata fahimci ma’anar furcin ƙarshe ba tai saurin jinjina masa kanta, “Na yarda da sharaɗinka, ko wanene jinin naka ka haɗani da shi muje wlhy baza’a taɓa cutar da shi ba koda da harara”.
Kallonta yay cike da salon izza yana sakin wani shaiɗanin murmushi da ɗage gira sama. “Kin tabbata?!”.
“ALLAH shine zai zama ahaidarmu”.
Hibbah ta faɗa cikin sauri da kaguwa.
“Da ga yanzu zuwa ko yaushe zaki iya ganin kanki gaban ahalinki da Isma’il ɗinki, amma ni minene makomar igiyoyin aure na dake kanki?”.
“Zan tayaka addu’ar ALLAH ya baka wadda ta fini”.
Maimakon amsa sai ya nuna mata kayan breakfast ɗin da Habib ya ajiye. Da sauri tace masa “Banajin yunwa”.
“Nike ji ai”.
Ya bata amsa kansa tsaye. Hankalinsa nakan aikinsa. Batare da musu ba Hibbah ta haɗa masa komai gabansa tana satar kallon takardun dake barbaje a ƙasan carpet da bata san na minene ba.
Shi dai duk da yana lure da kallon kurillar da takema takardun bai nuna ya gani ba. Sai ma turesu da yay gefe yaja abincin data haɗa masan ya hau ci hankalinsa kwance, kai kace baida wata damuwa. Sai da yasha kusan rabin cup na tea ɗin sannan ya miƙa mata. Kai ta girgiza masa batare da ta kallesa ba. Shima batare da yace komai ba ya kamo hannunta cikin nasa. Yanda yay ɗin ya tilastata ɗago idanu ta kallesa. Kofin ya ɗaura mata yana ɗan wani cizar lip da ƙanƙance idanunsa.
Haka kawai kallon da salon nasa ya saka tsigar jikin Hibbah tashi. Babu shiri tai azamar amsar kofin shayin tana maida kanta ƙasa ta duƙar. Shima ɗauke kansa yay ya maida ga aikin da ke gabansa. Lokaci-lokaci yana amsa wayar da ita kanta batasan da su wanene ba dan maganar ma a cuɗe suke yinta.
“Ciwonka ya daina zafi?”.
Ta faɗa cikin suɓutar baki daboda idonta daya sauka akan ƙafarsa dake harɗe ɗaya kan ɗaya tamkar wani jinin sarauta.
Duk da ya jita bai tanka ba. Hakan yasata ɗago ido ta ɗan dubesa. Ganin gaba ɗaya hankalinsa nakan system ɗin tai tunanin baiji ba, sai ta sake maimaitawa.
“Kin damu da ni har haka?”.
Ya faɗa batare da ya kalleta ba. Fuska ta ɓata, tare da kumbura baki ta cigaba da shan shayinta. “Daga tambaya”.
Kallonta ya ɗanyi ya ɗauke kansa. Yanda tai maganar kamar zatai kuka ne yaso bashi dariya. Amma sai ya gimtse abarsa yamaki cewa komai. Itama bata sake cewar ba harta kammala ta ajiye kofin zata miƙe. “A ina baba Saude take zanje wajenta”.
“Aiki zakimin nima anan”. Ya fa ɗa yana nuna mata gefensa. A marairaice ta ce, “Zanfa gaisheta ne”.
Maimakon ya bata amsa sai ya ɗakko lap-top da ke gefensa kalar pitch ya miƙa mata fuskarsa sam babu alamar wasa. Maganarsa ta dazun da yace mata rashin haƙurinta ya hanata zuwa wajen su Ummi ne ya sata zama a inda ya nuna matan. Koda ta kunna sai taci karo da hoton yayunta a screen ɗin harda yaya Isma’il. Babu shiri ta saki tattausan murmushi tana dubansa. “Nagode sosai ALLAH ya shiryeka kabar ƙwamushe kuɗaɗen mutane”.
Harara ya zabga mata yana sake tsuƙe fuska. A zuciyarsa kuwa kokawa yake da dariyar dake taho masa yana mamakin shegen kauɗinta. Wato tsoron jiya harya barta ta dawo normal. “Idan kikai wasa yau babu accaunt ɗin dazai kwana da ko naira acikin yayunki har Isma’il ɗin naki ma”.
“Wayyo, dan ALLAH kayi haƙuri wlhy wasa nake maka fa. Ai kaima kaga yanzu ka zama ɗan uwanmu ko”.
Hararar ta ya sakeyi ya ɗauke kansa. Itama sai bata sake magana ba ta ɗauke kanta tana murmushi. Dan idan yay harara ita dariya yake bata. Sai da ta kammala dai-daita komai sannan ta dubesa. “Mizanyi to?”.
Batare da yayi magana ba ya jawo takardun gefensa ya miƙa mata, sai kuma ya ɗan matso har jikinsu na haɗuwa. matsawa ta ɗanyi kaɗan, komai baiceba ya fara nuna mata abinda zatayi.
“Ni dai dan ALLAH karka sakani satar kuɗ…”
Bata ƙarasa ba yasa yatsa ya ɗalli laɓɓanta. “Idan wannan baki bai daina damuna ba sai na cinyesa ALLAH”.
Hannu tasa ta dafe bakin hawaye na ciko idanunta dan taji zafi. Shiko ya ɗauke kansa da cigaba da nuna mata ɗin kamar bai ganta ba. Sam ta manta da gargaɗinsa, yana gama faɗa cikin marairaicewa ta sake faɗin, “ALLAH bana son cutar kow…..”
Tai saurin sake dafe bakin batare data ƙarasaba ganin yanda ya juyo. Kanta ta shiga girgiza masa idanunta na cika da ƙwalla. Lap-top ɗin da ke akan cinyarsa ya ajiye tare da juyowa gaba ɗaya. Babu shiri ta miƙe zumbur tana ajiye tata gefe tare da takardun zata gudu yasa ƙafa ya harɗota. Gaba ɗayanta ta faɗa saman cinyarsa. Ya cije baki saboda ciwonsa. Cikin daburcewa ta shiga son tashi a jikin nasa tana faɗin. “Dan ALLAH kayi haƙuri ALLAH bazan sake ba”.
Bakin da ke maganar ya zubama lumsassun idanunsa da ke cike da mura. Sai yatsun hannunsa da ya tallafo ƙugunta har zuwa saman cikinta da yake ɗan motsawa. Zata sake yunƙurawa ta tashi ya sake nutsa hannunsa a saman cikinta dole ta koma ta sake zama tamkar zatai kuka. Kunyar duniya ta baibayeta tamkar zata halaka ta. Narkakken kallon da yake mata ya sata kai hannu zata rufe idonta dan rumtsewar ma ji take kamar bazai hanata ganin idanun nasa dake da matuƙar kaifi a gareta ba. Tana gab da kaisa saman fuskar tata ya riƙe. Da ƙarfi ta matse idanun da sake shagwaɓe fuska. “Nace fa kayi haƙuri”.
Hannunta daya riƙo ya murza cikin nasa da wani salon da yasa jininta tsinkewa a lokaci guda. ya sake kusanto da fuskarsa gab da tata yana sake marairaice idanunsa “Ni idan akai min laifi sai na rama ai”.
Ya faɗa cikin wata irin murya data saka Hibbah buɗe idanu ta kallesa babu shiri. Ganin fuskarsa gab da tata tai saurin sake maida idanun ta rumtse tana motsa baki alamar maganace a ciki babu damar faɗa. Fuskar tasa ya sake kusantawa da tata yana busa mata numfashinsa. Ji take tamkar ta fasa kuka dan yanayine da bata taɓa fuskanta ba a rayuwarta na kusanci da namiji irin haka. Tana ƙoƙarin buɗe idonta da son roƙonsa taji saukar laɓɓansa saman nata a bazata. Wata irin zaburar data bashi damar sake nutsata cikin ƙirjinsa ya rungume tayi. Tsabar rikicewar datai bama tasan ta saƙalo hanunta a wuyansa ba tana mintsini. Wata zazzafar ajiyar zuciya yaja yana sake narkewa bugun zuciyarsa na ƙara ƙarfi dan shima wannan shine karon farko a rayuwarsa daya tsinci kansa a irin wannan yanayin mai wahalar fassara da mantawa, daga shi har ita jikinsu rawa yakeyi, duk yanda yaso ganin yay control ɗin kansa ya barta ya kasa, sai ma sake ƙaimi yakeyi da canja salon tafiyar tasu zuwa wani abu daban.
Firgici ya saka Hibbah fara jujjuya kanta hawaye na zirara, duk mintsinin da take masa baisa yajita ba balle ta samu kubutar da take fata da ga garesa, sai ma yazam tamkar ƙara masa ƙaimi take da mintsinin.
Samun damar ɗaura hannunta da tai saman ciwonsa ta ɗan danna ya sashi janye jikinsa yana jan wani bahagon numfashi. Ba ƙaramin shiga tai cikin matsanancin firgici ba ganin yanda gaba ɗaya kamanninsa suka sauya mata lokaci ƙanƙani. Tai ƙoƙarin fisge jikinta da son tashi ya sake riƙota. “Na roƙeka dan ALLAH ka bari banaso, ka tausaya min karka ci amanata. Inason na cikama mahaifiyata burinta na tun farko akan auren Yaya Isma’i……”
Ruf ya sake rufe mata bakin batare data ƙarasa ba. A Kokawar son ƙwatar kanta da take cikin rawar jiki da firgici ne ta samu damar ɗayo mask ɗin face nashi, cikin zafin nama ya kai hannu domin hanata da ƙoƙarin jan kansa baya aka samu matsala ta zareta baki ɗaya, real face ɗinsa ta Isma’il ta bayyana kanta gareta…………✍
_______________________
Hi team no makeup
Ina kanawa mutanena🗣️
Shin Ina masoyan mg’s ina ma’abota ado da kwalliya kusaurara kuji dame nazomuku 💃
Nasan dayawa kunsiya kayanmu Kuma kunshaida yadda suke gyaranjiki cikin lokaci kalilan Koda iyasabulun kikayi anfani dashi sekinyaba balle kankat wato beauty kit dinmu toh inamaitabbatar muku cewa ynx kayanmu ankaramasu kayayyaki Wanda zasu Kara gyara fata fiye da tsammanin Mai tunani within 2weeks zakicanza kiga duk inda kikayi se anbiki d👀 domin ynd fatanki zaikoma Shar kamar madara bawanda zemiki kallo daya yadauke idanunshi😃😍
Hajiyata shin menene matsalanki, pimples ne?
Spot? sunburn,acne, stretch marks, knuckle, wrinkles, Black head,ko kinshafa Maine yabatamiki jiki
Inamai shaidamiki cewa ynx ne lokacin dayakamata kiyake dukkan wadannan kema kidinga fita sakayau abunki baruwanki da kunshe fuska ko kice sekinyi makeup hjy fita zar abunki kinuna ainihin natural beauty dinki😍domin kayanmu gbdynsu organic ne babuna bleaching zssu sa ki haskaka fatarki tayi ta kyalli kamar madubi ze fiddomiki d ainihin natural beauty dinki ne😘kunaji barin fadamuku wani Abu billah wannan prdcts damuke dashi ynx Koda kudinki seda rabanki domin duk sunzarce nabaya ankaramasu abubuwa dayawa masu matukar anfani agyaran fata🤗Ina Wanda basasan shafa Mai koda sabulun kawai kike anfani dashi inamai tabbatar Miki zkg ynd jikinki zekoma luwai luwai😘
Soap:3k
Beauty kit:12k
Chat:08062991549
07066210195
Call :07046881166
08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg’s skincare
amare inakara shaidamuku duk wacce tayi anfani d kayanmu Bata bukatar gyaranjiki sedai ra’ayi🥰
Masoya kunanan kauna yanda nakwashe aljihu domin nafarantamuku kuyi achieving goal dinku pls Nima kunanan kauna kufarantamin😪🤠aljihuna yafarfado hilis karnakoma kauyenmu🥲
Yar shawarmannan duk nasaba😤 hilis kugarzayo arabani da kaya🤝
Nd guest what🤩
Duk Wanda yy siya 10k zuwa sama zesamu Karin gift😃
Pamper your skin🧖♀️
Shine like a bride👰🏻
Glow🧚🏻♀️.
_________________________
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI……_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*
*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
GIPHY App Key not set. Please check settings