Advertisement
*_Chapter Forty Two_*
………..Har cikin ransa sai da yaji shock dan bai zaton hakan ba da ga gareta cikin sauƙi. Sai dai idan yayi dubi da tarbiyanta da yanda ta tashi za’a iya mata koda wayone da yaudara ta amince. Idanunsa ya lumshe tare da riƙe hannuwan nata yana murmushi, ya rungumeta da ƙyau shima yana jerama UBANGIJI godiya, dan jinsa yake tamkar ya sauke wasu kaya masu nauyi dake bisa kansa.
Muhibbat da gaba ɗaya ta kasa tsaida kukanta ta sake yunƙurin barin jikin nasa.
“I’m sorry Hibbaty”.
Ya faɗa cikin kunnenta yana sake matseta da busa mata iskar numfashinsa cikin kunnen dake tada mata tsigar jiki..
“Ni ka sakeni, wajen Ummina zanje, karka sake shiga sabgata kuma. Karka sake zuwa mana gida.”
Cikin gimtse dariyarsa ya ɗagota da riƙe fuskarta cikin tafukan hannunsa. “Buɗe idanun mana ki kalli cikin nawa ki faɗa. Kefa kikace da Isma’il zaki zauna, taya kike tunanin kunnen Isma’il yaji wannan zance yay sakacin barinki kiyi nesa da shi kuma?”.
Advertisements
Sake matse idanun tayi hawaye na zirarowa. Batare data iya buɗesu ba tace, “To na fasa. Yanzu bazan zauna da kai ba”.
“Shi kuma babyna kimin yaya da shi? Dan bazaije ko ina ba a gidansu zai tashi”.
Babu shiri ta buɗe idanun sai dai bata kallesa ba. Cikin motsawar sakarcin nata tace, “Ni yaushe naga wani babyn ka balle na rakitama kaina har yaje gidanmu”.
Hannunsa ya ɗaura a saman cikinta yana ƙasa da shi a hankali, cikin muryar raɗa ya ce, “Gashi anan insha ALLAH, zaki gansane kema soon”.
Hanunsa ta ture da faɗin, “ALLAH ya kiyaye”.
“Na yanzu kam ya faru sai dai ya kiyaye na gaba kuma”. Ya bata amsa yana kwantar da ita shima ya kwanta a gefenta. Duk yanda taso tashi kuma ya hana dole ta haƙura. Sai dai ta masa shiru bata sake tankawa ba. Shima gajiya da suruntunne ya sashi rufe idanunsa da fatan samun barci.
Koda suka tashi wajen sha ɗaya duk yanda Hibbah taso zillewa hanata yayi tare sukai wanka. Ta gama ƴan koke-kokenta na shagwaɓa ta bari. Breakfast ma tare sukayi, tanason taje gaida baba Saude ya hanata. Dole ta haƙura tanata faman sinne kai dan sam bata buƙatar su haɗa ido. Sai dai dukan motsinsa saita bisa da kallo, har yanzu zuciyarta na kaikawo akan kasancewarsa Isma’il kuma Master. Sarai yana lure da ita amma sai ya basar yanata aikinsa tana gefensa. Lokaci-lokaci yakan sakata tai masa wani aikin.
A yau dai komai yinsa take babu musu ko tsiwa, dan idan ka ganta bazaka taɓa ɗauka Hibbahn Ummi da su Yaya Ammar bace. Haka suka kasance har yamma salla ce kawai ke tashinsu. Abinci ma da aka kawo na rana catai ta ƙoshi. Shima kuma baici ba dan bayajin daɗin bakinsa tamkar ita. Har dare bai fita ko inaba yanata aiki, sai bayan sallar isha’i ne Habib ya shigo musu da ledar kayan kwaɗayin da suka fita yawo suka siyo. Koda ya shigo falon Hibbah na kwance a doguwar kujeran da Master ke aiki kanta a saman cinyarsa. Dan ta kwanta tai filo da hanun kujerar ya taso daga inda yake zaune ya ɗagota yasa kan nata saman cinyarsa. Duk yanda taso tashi kuma bai bata fuska ba dole ta haƙura ta kwanta ƙamshin turarensa na mamaye kwanyarta a hankali. Aikinsa yake ita kuma tana kwance idanu a rufe ta lula duniyar tunani.
Koda Habib ɗin ya shigo bayan ya amsa masa sallamar da bashi iznin shiga kallo ɗaya yay musu ya ɗauke kansa zuciyarsa na masa wani fari fat. Kayan ya ajiye yana masa sannu da aiki.
Amsawa yay yana ɗago idanu ya kalli ledar, sai kuma ya maida dubansa ga Habib ɗin.
Da sauri Habib yace, “Na aunty Queen ne, sai da safe”.
Advertisements
Kafin ma master yace wani abu tuni ya fice. Kansa ya ɗan girgiza da maida dubansa ga Hibbah da duk take jinsu amma tayi luf. Ganin bata motsaba komai baice ba ya cigaba da aikinsa. Sai zuwa can da yaga barci na meman dibarta ne ya ajiye aikin yana buɗe ledan. Gasashshen namane mai romo da ice-cream. Sai Haɗaɗɗun chocolates masu daɗi. Roban ice-cream ɗin ya ɗauka ya buɗe. Dan shima ma’abocin sonshi ne. Batare da yayi magana ba ya ɗiba yakai baki.
Hibbah dake sauraren taji yace ta tashi ta hadiye yawu da ƙyar. Jin alamar ya ƙara kaiwa baki yasata buɗe idanunta da miƙewa zaune. Hannu tasa ta warce roban tana ɗan hararsa ƙasa-ƙasa da ƙunkuni.
“Ai nidai banji ance nakaba amma ka hau kai da sha”.
Gira ɗaya ya ɗauke yana sauke mata wani shu’umin kallo. “Naga kamar baki da ra’ayine shiyyasa nace bara na maida jinina da kika tsotse jiya da wanda kikasa bindiga ta zubarmin”.
Baki taɗan murguɗa gefe da kai cokalin ice-cream ɗin zata sha ya kai hannu zai riƙe ta tura da sauri.
“Humm rowa ko?”.
Kumburarrun idanunta ta ɗan juya masa “Kai da baka da rowar ka taɓa siyamin ne?”.
Master daya shagala a kallonta har tana saka tsigar jikinsa tashi ya ɗan waro idanu kaɗan. “Aunty Queen kiji tsoron ALLAH ban sayo miki kazan first night ba randa aka kawoki?”.
“Kadai satoni! Kuma ni babu wata kaza daka sayamin”.
Dariya ta bashi, amma sai ya gimtse yay murmushi kawai. “Ai ke amaryace ta musamman, shiyyasa kaiki gidan mijinki ma ya zama na musamman.”.
Yay maganar da ɗan kwantowa jikin kafaɗarta yana wani sassanyan murmushi idanunsa akanta. Matsawa taso yi ya tura hanunsa ta bayanta ya riƙo ƙugunta. Cikin marairaicewa yace, “Ki sammin ko kaɗan mana, inba hakaba kuma a daren nan na ɗiba rabona a can”.
Sam Hibbah bata fahimci a ina zai ɗiba rabon nasa ba. Dan haka ta sake juya kanta gefe tana kaiwa baki da faɗin, “Gara kaje ka ɗiba rabon naka a can amma ba nan ba”.
Wata ƴar dariyar ƙeta yay da ɗaura hanunsa saman ƙirjinta, “Ina godiya sarauniyar gidanmu”.
Da sauri ta ture hannunsa har tana neman sakin robar ice-cream ɗin ya riƙo da sauri. Kafin tayi wani yunkuri ya miƙe zaune sosai da fige ɗan spoon ɗin ya juya mata baya. Shaf ta manta da wanda take tare, ta ɗane bayansa cikin shagwaɓa tace, “Ummi kin gansa ko”.
Ice-cream ɗin ya dinga ɗiba yana kaiwa baki da kakkauce mata. Itako ta maƙalƙalesa ta baya da daura kanta a saman wuyansa tana son amsa amma ta kasa. Master da ke sha da sauri-sauri ya fara ƴar dariya mara sauti da batai zaton ya iya ba. Ganin yasha kusan rabi yasata barin bayansa ta sakko da sauri a kujerar taje gabansa zata warce ya kauce ta faɗa jikinsa. Zaune tai ɗare-ɗare bisa cinyarsa. “Ni wlhy ka bani abuna, ai dai baice naka bane, nawa yace”.
Master dake murmushi ya sake kaiwa bakinsa da ajiye robar ta gefen kanta batare data sani ba. Ta buɗe baki zata sake magana ya haɗe bakin nata da nasa ya fara juye mata ice-cream ɗin daya gama narkewa a cikin bakinsa. Bata da wata mafita saita shanyewa. Dan ganin tana son ture masa fuska ya sashin toshe mata hanci dole ta haɗiye. Koda ya saki hancin bai saki bakinba ya zarce da kissing ɗin ta. A salon da yake sumbatar natane ya sata nutsuwar dole tana amsar sakonsa. Sai da taji hannunsa cikin rigarta ne tai ƙoƙarin turesa jikinta na fara rawa.
Matsar da bakin yay yakai saitin kunnenta yana sake rungumota da ƙyau. “Kemafa yarinyar nan na kula fitinanniya za’ai. Dan sosai jikinki ke amsar kowanne saƙo”.
Hibbah jitai tamkar ta tsala ihu. Tai azamar wuntsilowa a jikinsa, yana son kamota ta zille da gudu tabar wajen.
Binta da kallo yayi yana sakin murmushi da lumshe idanu.
★★★
Hibbah bata sake jin ɗuriyar Master ba har tai shirin barci ta kwanta, zuciyarta cike da tunani da kwaɗayin ganin ahalinta. Wani gefe kuma na imagine yanda su Ummi zasuji cewar Isma’il shine master ashe, dan ita kam har yanzu zuciyarta ta kasa gaskata hakan, neman wanda zasu tattauna maganar kawai take a ranta. Dan tambayoyine fal bakinsa amma kunyarsa da nauyin daya aza mata yasa ta kasa masa ko guda ɗaya.
Tun tana a tsorace da tunanin zai shigo har barci yay awon gaba da ita bai shigo ɗin ba. Sai kusan ƙarfe ɗaya har tamayi nisa a barci sannan ya shigo a matuƙar gajiye da tsananin bukatar barci. Yaji daɗin ganin tayi barcin, hakan na nufin ta ɗan samu ƴar nutsuwa a zuciya da jikinta daya murza a jiya. Shirin barcin yay shima da dukkan abinda yake na al’adar rayuwarsa sannan ya kwanta a gefenta.
*_Washe gari_* tamkar jiya tare sukai sallar asuba. Hibbah dake ta faman sinne-sinnen kai ma ta gaishesa da tambayar jiinsa. Amsa mata yay da tambayarta nata jikin itama, tace ita dai lafiyarta ƙalau. Murmushi yayi kawai bai sake cewa komai ba harya kammala azkar ɗin dayay zamanyi sannan ya mike ya bita gadon. Harta fara lumshe idanu taji saukar hannunsa a jikinta. Babu shiri ta buɗe tana kai hannu zata ture nashi. Hanawa yay ta hanyar riƙe hanun nata da busa mata numfashinsa cikin kunne.
Zatai magana yay saurin tareta da faɗin, “Shiiii bake kikace lafiyanki ƙalau ba”.
“Da wasafa nake ALLAH akwai ciwo”. Ta faɗa da sauri tana buɗe idanunta sai gasu a cikin nasa. Duk kuma yanda taso janyewa ya sarƙesu ta gagara. Wasu mayatattun halittun fitina take gani suna yawo a cikin idanun nasa. A take nata suka fara tara ƙwallar da shi kuma suka sake ɗaga masa hankali.
“A ina ciwon yake?”.
Yay maganar da wata kasalalliyar muryar dake tabbatar da ɗunbin begenta dake cizonsa. Sake rikicewa Hibbah tai zata fara ja da baya yay mata runfa da jikinsa yana jan sassanyan numfashi da busa mata akan fuska. Sosai ta rikice, dan irin abinda tagani cikin idanunsa a shekaran jiya da rana yanzunma shine tattare da shi. A hankali ya ɗaura hanunsa saman nata yana sake matso da fuskarsa gab da tatan. Kai ta shiga jujjuya masa laɓɓanta na motsawa alamar son roƙonsa.
Yasan bazai iya ɗaga mata ƙafa ba, hakan yasashi lumshe idanun nasa dai-dai yana kai laɓɓansa saman tausasan nata, dan dama dauriya kawai yakeyi harya iya ɗaga mata ƙafa da daddare. Rawar jikinta da kukan da take masa yau har yaso yafi na shekaranjiya dan wahalar data sha kawai take ƙiyastowa. Shiko da idanunsa suka rufe bida ita kawai yake ta salo-salon da baisan yama iyaba sai yanzun.
Kuka take sosai tana lafe a jikinsa, nata jikin na ɗan rawa dan yauma ɗin dai wahalar tasha, duk da dai ta shekaranjiyan tafi ta yau sai dai ta yau ɗin ma babu sauƙi dan famine. Shiko babu abinda yake iya furtawa sai shafa bayanta zuwa gashin kanta.
“ALLAH yay miki albarka”.
Ya faɗa a fusge yana sake turata cikin jikinsa har saida ta ɗan saka masa kuka ya sassauta mata. Sai da yaji kukan nata ya ƙi tsayawane ya mike cike da dauriya ya kaita toilet. Yau ɗin ma dai da taimakonsa ta gyara jikinta tana faman masa raki da roƙon ya kaita wajen Ummi ita dai karya kasheta.
Sosai yaji tausayinta dan shima yasan dai yayi gaggawar koma mata duk da wahalar data sha kwana biyu da suka wuce. “Indai wajen Ummi ne zan kaiki, amma sai kin barmin kuka. Kin yarda?”.
Da sauri ta jinjina masa kai alamar eh ta yarda. Ya sumbaci kumatunta da faɗin, “Good girl! ko ke fa. Kefa yanzun kin girma harkan yara yawane Hibbaty”.
Da wannan daɗin bakin ya taimaka mata suka fito, koda suka sake komawa suka kwanta lafe masa tai a jiki tana jan ajiyar zuciya har barcin wahala yay awan gaba da ita cikin ƙanƙanin lokaci. Sumbata ya kaima goshinta, a ransa wani nutsuwa da kaunarta na ratsashi. Dan a yau yafi jin matuƙar nutsuwa fiye da shekaranjiya da komai yayisa ba cikin hayyacinsa ba.
Barci sosai sukayi batare da wani ya takura musu ba. Dan su Habib ma tun safe suka bar gidan. Baba Saude kuwa da ba sanin mike faruwa tayi ba ita duk ɗaukarta ma Hibbah bata gidanne. Dan tun randa sukazo bata sake ganinta ba master ya kasa ya tsare.
Kusan a tare suka farka. Sai dai jin motsinsa yasa Hibbah ƙin buɗe nata idon. Idanunsa ya zubama fuskarta yana ƙare mata kallo, yanda yaga idonta naɗan motsawa yasan ta tashi. Baiyi magana ba, sai yatsansa daya ɗora saman rumfar idon yana wasa da shi. Dole ta buɗe idanun da ture hannunsa tana kumbura fuska. Murmushi yayi da saƙalo hanunsa ta bayanta ya matso da fuskokinsu dab da juna yana kai mata sumbata.
“Nifa kwana biyu naga harma kin nutsu autan Ummi”.
Yay maganar cikin raɗa tamkar mai tsoron ajisu.
A ranta tace, (ba dolena ba. kana min wannan muguntar nacika magana kace na maka rashin kunya ka fake da hakan ka maidani machine). A fili kam saita marairaice masa fuska tana mar-mar da idanu. “Dan ALLAH yaushe zaka kaini wajen Ummin?”.
Yasan dama shine matsalarta. Maimakon ya bata amsa sai ya lumshe idanunsa yay shiru tamkar bai jita ba. Idanunta ta buɗe tana kallon fuskarsa har batasan ta shagala ba. Sosai yaji idanu na yawo masa a jiki, amma ya dake harda sauya saukar numfashinsa tamkar mai barci. Tunaninta barcin gaskiyarne ya ɗaukesan. A hankali takai hannu bisa girar idonsa ta ɗan gyara, sai kuma ta murza goshinsa kaɗan duk dan son ta tabbatar ba facemask ya saka ba. Sake kumawa tai kan laɓɓansa nan ma dai taji, ta cigaba da shafa kumatunsa da siririn gashi na saje ke kwance har zuwa kunnensa ta ɗan murza nan ma zuwa bayan kunnen da ƙeyarsa. Yanda take masa gaba ɗaya tsigar jikinsa miƙewa take, ganinfa da gaske neman firgita masa jiki takeyi sai da ya shammaceta ya buɗe idanunsa da suka fara sauya kala. Aiko karaf suka faɗa cikin nata. Saurin janye hannunta tai a fiskarsa amma ya riƙe ya dannesa da nasa. Gaba ɗaya ta daburce, baya ta juya masa murmushi na kufce mata dan taji kunya harga ALLAH.
Shima murmushin ya saki da kwantowa bayanta yana son leƙa fuskarta. “Ki kalli mijinki nakine auta, yanda kike auta a gidanku insha ALLAH kece ta fari kece auta a zuciyar Shuraim ɗinki. Karkiji komai, kiyi komai ba komai baby luv”.
Fuskar ta cusa a cikin filon, duk yanda yaso ya janye taƙi. Dole ya haƙura ya miƙe yana dariya da take mamaki. Tanaji ya shiga toilet ta sauke nannauyan ajiyar zuciya. Jin motsin ruwa ya sata tabbatar da wanka yake dan haka ta miƙe ta fara gyara gadon, fatanta ta fice kafin ya fito. Tana cikin gyaran takardun daya ajiye idanunta ya sauka akan wadda ke sama da tsautsayi yasa file ɗin ya ɗan goce suka zubo. Tsugunnawa tai tana tattarosu sai taga tamkar sunan Abbansu a jiki. Duk yanda taso hana kanta dubawa ta kasa, ɗaya bayan ɗaya ta dinga dubasu sai taga duk takardun kaddarorinsu ne da ta taɓa jin su Yaya Muhammad na maganar suna hannun Halilu. Mamaki ya kamata ta cigaba da dubawa har zuwa na ƙarshe da ke rubuce da dogon bayani. Ƙofar bayin ta ɗan kalla jin har yanzu akwai motsin ruwa yasata zaman dirshan ta fara karantawa a nutse……….✍
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI……_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*
*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
GIPHY App Key not set. Please check settings