Advertisement
*_Chapter Forty Three_*
………..Bayanine tiryan-tiryan daya shafi takardun da harƙallarsu, harda kuɗaɗen daya kwashe na Halilun da yanda akai ya amshesu, da masu mallakin dukiyar da alaƙar dake tsakaninsa da su A.G. A yanzu kam Hibbah ta sake tabbatar da Master baya tare da su A.G ɗin, duk da ya mata bayanin komai ta yanda ya shiga jikin nasu da tunanin shaiɗaninsu ne shi. Wasu irin irin hawaye suka gangaro mata saman fuska zuciyarta na tunano mata randa Isma’ill ya karyama Abba ƙafa akan abinda yay ma Ummi…..
Zare takardar da akai ta bayanta da ɗisowar ruwan wankan jikinsa ne ya sata juyowa da sauri. Master daya tamke fuskarsa matuƙa kamar bashine ya gama tarairayarta yanzun ba, ya ɗan harareta yana ɗaukar sauran takardun ya maida cikin file ɗin. Ya ajiye ya juyo kawai yaji ta faɗa masa jiki a bazata ta rungumesa da sakin wani marayan kuka. Babu shiri ya dafe towel ɗin daya ɗauro a ƙugunsa dake neman faɗuwa. Dama ba wani rigan arziƙi bane a jikin nata, hakan sai ya bashi damar jinta bisa fatarsa dake ta faman raɓar ruwa yanda ya kamata. Ya lumshe idanunsa yana riƙota da ƙyau shima da sakin nannauyar ajiyar zuciya.
Baice komai ba sai yatsun ɗayan hanunsa daya tura cikin gashinta, ɗaya kuma yana shafa bayanta a hankali, zuciyarsa sai wani irin zallo take da tsalle-tsalle kamar zata fito waje. Ganin kukan nata bana ƙare bane yajata suka zauna a bakin gadon tana jikinsa. Fuskarta ya ɗago dasa babban yatsansa yana share mata hawayen.
“Miya faru kuma?”.
“Ka yafe min”.
Wani ƙasaitaccen murmushi ya saki yana ɗan ɗage gira sama, idanunsa na yawo akan fuskarta. “Ni baki min laifin komai ba”. Yay maganar yana ɗan sumbatar laɓɓanta.
Kanta ta girgiza masa hawayen na sake rige-rigen sakkowa. “Nasan na maka laifi, na fahimceka a bai-bai, amma wlhy karkaga laifina nima inada hujjata. Nagode, ALLAH ya saka maka da alkairi, ya cigaba da baka kariya a dukkan motsinka da al’amuranka. Abinda naji wajen su Abba da shegen jami’in nan yasa nake maka kallon bai-bai. Kuma koba niba duk wanda yaji tunda baisan gaskiya ba zaiyi komai kamar nine”.
Advertisements
“Na sani Muhibbat, shiyyasa naita miki uziri. Duk da kin hasalamin zuciya a ranar, dan kaɗan ya rage ki buɗemin dukanin aikina da zai iya sa harsu Ummi su rasa ransu ma. A hakanma kaɗan ya rage ki jefa rayuwarsu a haɗari, ALLAH ya taƙaita. Ina ƙaunar Ummi Muhhibat, hakama su yaya Muhammad. Bayan yaran nan da kike ganina da su a yanzu ahalinki sune ahali na biyu da nake kallo mafi kusanci dani a duniya. Tun bayan rasa mahaifiyata Ummi ce ta fara dafa kaina taimin addu’a cike da soyayya. Taya kike tunanin bazanyi yaƙi a kan zuri’arta ba. Taya bazanso haɗa jini da ita ba.” ya ɗaura hannunsa saman cikinta “Ina fata da addu’ar ALLAH yasa wannan cikin nayi ajiyar jinina da zai miki rakkiya zuwa wajen Ummina”.
“Nidai ba yanzu ba”.
Ta faɗa tana tura baki da kwantar da kanta a kafaɗarsa.
“Haba baby luv kiji tausayina mana, Su uncle Habib mafa shi suke jiran gani”.
“Waɗan nan na daina kulasu a gidan nan ai, dan suma haushina sukeji”.
Ƴar dariya yayi mara sauti da kamo hannunta ya ɗaura bisa fuskarsa. “Kefa kikai musu laifi, kika sa aka harbar musu Yayansu. Ba dole suyi fushi da ke ba. Amma nasan da sunga kin ɗan fara amai sun samu ɗa zasu daina ai”.
Baki ta tura tana ƙara cusa kanta a wuyansa. “Ni dai nace ba yanzu ba”.
“To ai ya riga ya shiga insha ALLAH, dan ban buga ƙwallona da wasaba tun a farkon fari”.
Tashi tai zata bar jikinsa da faɗin, “Nidai babu ruwana wlhy inada kunya”.
“Nima ai inada ita. Bakiga tun shekaran jiya kunyarki nake ji ba”. Yay maganar yana binta da kallo.
Juyowa tai ta kallesa da ɗan waro idanu tana riƙe haɓa “Kai ɗinne kake wani jin kunyata?”.
A yanda tai maganar da waro idanun da bage bakin ya bashi dariya, amma sai ya gimtse baiyiba, yay ɗan murmushi kawai da ɗage gira ɗaya. “Baki yarda kin kalleni ba yazaki gani. Idan kina son tabbatarwa zoki gani”.
Advertisements
Kafinma ya rufe baki ɓurum ta faɗa toilet da sauri. Murmushin fuskarsa ne ya sake faɗaɗa. Ya miƙe domin shiryawa yana godema ALLAH da wannan farin ciki daya bashi a lokacin da bai zata ba. Harya kammala shirinsa tsaf cikin ƙananun kayan nasa na fama Hibbah bata fito ba. Yasan inhar tanajin motsinsa a ɗakin kota gama bazata fito ba. Dan haka ya tattara wayoyinsa da lap-top yayo falo.
Tun a ƙofar fitowa yaja ya tsaya saboda cin karo da baƙon dake zaune a falon ƙafa ɗaya kan ɗaya yana kallo. Abdull da ya ɗan ɗago ya kallesa ya ɗauke kansa yana wani shaƙiyin murmushi. Hararsa Master yayi da cigaba da takowa cikin falon. Ya zube kayan hannunsa saman centre table ɗin da fisge remote ɗin hanun Abdull ɗin ya rage ƙarar tvn.
“Banza ɗan nanaye ko ina ake sai an nuna hali”.
Murmushi Abdull ɗin ya sake saki har da ƴar dariya. “Ni da kai a tantance ɗan nanaye ai ayanzun. Mutumina kafa samu lafiya da alama. Na wani tada hankalina a banza harda baro canada babu shiri”.
“To ubanwa yace kazo mai kan gwanda kawai.”
“Zakako cika baki yanzun tunda harbi yayi sauƙi, tsabar zalama ma ga ciwo sai da ka tafi kwaɗayi filin ball”.
Murmushi master yayi dan Abdull ba ƙaramin tasa rayuwarsa yake gaba ba. Shima mutum ne mara son hayaniya da yawan magana, dan harma yafisa miskilanci. Amma inhar suna tare to bakin Abdull cau-cau akansa.
“Wai yaushe ka shigo haka dan ALLAH?”.
“Tun randa aka harbeka. Daddy (I.G) ya sanarmin naji bazan iya kwana a canada banzo naga rabin jiki ba.”
Dariya Master yay yana gyara zama. “Shine sai yau nake ganinka, kazo kuma kanamin iskanci anan. ”
“Tun randa kasha harbi ina gidan nan, kai ne dai kai wahalar gani saboda kana daga lungu kana tsinkar fure.”
“ALLAH ya shiryeka to”.
Master ya faɗa yana murmushi.
“Amin ya rabbi tunda addu’a kaimin. Ina madam ɗin tazo na ganta, dan na huce zuwa yanzu tunda nasa an rama mana harbinmu”.
“Mara kirki, ALLAH zai saka mata ai”. Master ya faɗa yana miƙewa. Dariya Abdull yayi yana binsa da kallo, “Eh lallai ka shiga hannu ɗan gimbiya. Da alama dai ƴar shilar nan taka tauraruwa ce cikin taurari”.
Master da ke haɗo musu coffee yay murmushi kawai batare da ya bashi amsa ba. Sai da ya kammala ya dawo falon ya ajiye a centre table ya zuba musu sannan ya zauna bayan ya mikama Abdull ɗin nasa.
“Bestie ya yarana da madam?”.
Abdull ya ɗan ɗage kafaɗa da faɗin, “Lafiya lau suke, sunata gaisheka.”
“Ina amsawa, nayi kewarsu da yawa gaskiya”.
“Karka damu suna gab da dawowa kusa da kai insha ALLAH. Ya gwagwarmaya? Daddy nata bani labarin ayyukanka da jajircewarka. ALLAH ya saka da alkairi ya ƙara girma”.
Master dake murmushi ya kai kofin coffee ɗin bakinsa ya ɗan kurɓa. “Uncle baya gajiya da yabona, shi baya tsoron kar wataran naci amanarsa”.
Harararsa Abdull ɗin yayi ya ɗauke kansa. Zaiyi magana Hibbah da batasan da zaman Abdull ɗin ba ta fito cikin shirin son zuwa gaida baba Saude yau. Ganin Abdull ɗin na kallon hanyar bedroom ɗinne yasa Master juyawa ya kalla wajen shima. Numfashi ya ɗan ja a hankali ganin yanda kayan sukai mata ƙyau, baiyi zatonma zasu mata ba a lokacin daya sayesu. Ganin ta ɗan daburce kamar zata juya yay mata alama da idanu tazo. Babu musu ta gyara ƙaramin gyalen data yafo saman wando da rigan parkistan ɗin ta nufosu cike da nutsuwa tamkar ba ita ba. Abdull da tuni ya ɗauke kansa da ga kallonta ya maida ga tv yace, “Amarya baƙya laifi ko kin kashe ɗan masu gida”.
Murmushi Hibbah tai da kaiwa zaune a kujerar da ke kusa da ita. Cikin girmamawa ta shiga gaida shi. Shima amsa mata yay da kulawa yana kallon Master da ya cigaba da shan coffee ɗinsa yana saurarensu.
“Amarya yaya kina kulamin da bestie na sosai ko?”.
Murmushi tayi, dan gaba ɗaya jitai kunya ta dabaibayeta. Sai take ganin kamar kowa zai iya fahimtar halin da take ciki tsakaninta da Master yanzun. Shi dai Abdull ya cigaba da tsokanarta ne. Yayinda ita kuma ta kasa amsawa dan kunya. Sai da ya gaji dan kansa ya barta. Master dai bai tanka musu ba har sai da Abdull ɗin yay shiru sannan ya duba Hibbahn, saboda nutsuwar tata yay masa daɗi.
“Muhibbah!”.
Ya kira sunanta a hankali. Ɗan ɗagowa tai ta dubesa da amsa masa. Ganin ita yake kallo ya sata sake maida kanta ƙasan.
Ya ɗan sake kwantar da bayansa jikin kujera yana kallon nata. “Wannan sunansa Abdul-Hakim. Aminina ne kuma ɗan uwana. Likita ne a yanzu haka yana zaune a canada tare da iyalinsa da yaransa biyu”.
Jin yayi shiru ne yasa Hibbah jinjina masa kanta. Tace, “Masha ALLAH Yaya sannu da zuwa. Ka baro su lafiya?”.
Abdull da Hibbahr ta birge ba kamar yanda yake tunanin ganintaba yay murmushi, “A lallai na samu ƙanwa kenan. To ina godiya sosai Muhibbat. Suna lafiya, suna kuma gaisheki”.
“Nagode ina amsawa”.
“Nima nagode sosai da samun tarba daga gareki”.
Kanta kawai ta jinjina masa tana miƙewa. Rasa madafar ina zata dosa ya sakata nufar kitchen, a yanda ta samu kitchen ɗin sai kawai ya birgeta taji sha’awar yin abinci a ciki. Ƙofar baya ta fita ta kitchen ɗin, wadda daga nan babu nisa da sashen su Habib. Babu wani tunani ta nufi can. Sai dai bata samu kowa ba sai baba Saude da taji daɗin ganinta. Dan sai tambayoyi take mata akan yaya take? Ina ta shiga? Yaya jikinta?.
Hibbah da itama tai kewarta harsu Habib ɗin ma da Sharifat ta amsa mata cike da girmamawa. Daga nanne suka ɗan taɓa hira har Hibbah ta sakko zancen sonyin girkin amma ta duba a can sashen babu kayan abinci.
Karan farko da baba Saude taji aranta kodai akwai alaƙa ta aure tsakanin Master da Hibbah ne? Kamar zata tambaya dai sai tai shiru. Sai ma sanar mata da tai cewar gama breakfast ɗinsu nan tun ɗazun take jiran shigowar su Salis sukai amma babu wanda ya shigo tun fitar safe da sukayi.
A nutse Hibbah ta amsa mata har baba Saude na mamakin yanda ta canja mata a ƙanƙanin lokaci. Sai dai ta danne a ranta ta bita da kallo harta fice.
Koda ta dawo sashen nasu a yanda ta fito ta kitchen da babban tray ɗin sai Abdull yay tunanin ita ta haɗo musu abincin, Master dai da kallon mamaki ya bita amma sai baiyi magana ba harta kai trayn ajiye saman centre table. Ɗan ɗagowa tai ta dubesa. “Ko akai muku dining?”.
Tsabar mamakin daya rufesa da ƙyar ya iya kaɗa mata Kansa. Kafin ya iya motsa laɓɓa da ƙyar yace, “Nan ma yayi sannu da ƙoƙari”.
Kanta kawai ta kaɗa masa tabar wajen, kitchen ta koma ta haɗo duk abinda zasu iya buƙata ta ɗauraye ta sake kawowa, kafin ta koma ta ɗauka ledan jiya data gani cikin fridge. Chocolates ne a ciki sai naman da ko taɓashi basuyi ba. Sai roban ice-cream guda ɗaya data rage. Chocolates ɗin ta ɗiba guda uku ta ɗauka naman ta koma sashen su Habib.
Yanzun kam ta iske sun dawo, dan tana shiga suka haɗa baki wajen gaisheta da kiranta aunty Queen kamar yanda suka saba. Harararsu tayi itama kamar yanda ta saba ɗin, kafin takai zaune kusa da baba Saude tana ɓare ledan chocolate ɗaya ta kai baki. Koda suka cigaba da hira sunsha matuƙar mamakin yanda take amsa musu a nutse tamkar ba ita ba, hakan yasasu fahimtar dama tsiwa ce ke damun bakinta kawai badan batasan komaiba ko bata da nutsuwa ne. Habib ma tun yana ɗan basar da ita harya saki jikinsa kuma. Itako tayi mirsisi tamkar ma bataga yana fushin ba.
Har akai sallar azhar Hibbah na nan tare da su Musbahu. Sallar ma a ɗakin baba Saude tayi abinta. Bayan sun idar kuma ta bita suka shiga kitchen tare sukai girki mai sauƙi. Baba Saude ta haɗa na master tamkar yanda ta saba.
“Ɗiyata ga abincin mijinki ko”.
Tai maganar cike da son bugar cikin Hibbahr. Har ko cikin rai Hibbah taji kunyar kalmar mijin nan. Tai ƙasa da kanta cikin sabon sanyin daya saukar mata ta ce, “To baba”.
Kafeta da idanu kawai baba Saude tai cike da mamaki fal ranta. Kenan dai hasashenta ya zama gaskiya aure ne tsakanin Master da Hibbahn. Sai taji wani farin ciki ya baibaye zuciyarta harta kasa ɓoyewa sai da ta tanka. “Oh ni ƴar nan, dama babana mijinki ne amma kuketa ɓoye-ɓoye?”.
Da sauri Hibbah ta ɗauka trayn abincin ta fice tana murmushi. Baba Saude ta ɗaga hannu sama tana ma ALLAH godiya da wannan haɗi, dan ɗari bisa ɗari taga dacewar wannan ma’aurata. Ta kumayi farin ciki matuƙa.
Hibbah ko data koma sashensu ta iske su Master basu dawo ba da ga salla da suka fita. A dining ta ajiye musu abincin yanzu kam, ta tattare falon da kwanikan da sukai amfani na ɗazun. Kitchen ta kai ta wanke. Tana tsaka da goge inda tai wanke-wanken taji ƙamshin turarensa.
Jiyowa tai ta duba ƙofan dan bataji takunsa ba. Ido suka haɗa yana tsaye jikin ƙofa ya harɗe hannaye a ƙirjinsa yana kallonta. Hararar sa tai kaɗan da ɗauke kanta. “Ni dai abar kallona gaskiya”.
“Ai sadaki na na kalla”.
Ya bata amsa da ɗage gira sama duk da ba kallonsa take ba. Hibbah dake cigaba da aikinta tai murmushi kawai. Cikin son kauda zancen nasa da idanunsa dake binta da mayataccen kallo ta ce, “Ga abinci can a dining kai da baƙo”.
Hannayensa ya warware daga ƙirjinsa ya ƙarasa takowa cikin kitchen ɗin, ta ɗan gefenta kaɗan ya tsaya tare da jingina da jikin kitchen cabinet ɗin yana kallonta. “Da gaske autar Ummi tayi hankali irin na kowace mata a gidan miji, nagode sosai da kika fiddani kunya Hibbaty”.
Hibbah dai bata yarda ta kallesa ba, amma taji daɗin ganin yanda ya nuna jin daɗinsa akan abinda tayi badan tayi tunanin tayi dai-dai ba…..
Katse mata tunani yay da faɗin, “Ki shirya idan mun kammala zamuje anguwa”.
Ɗagowa tai ta dubesa cikin wani irin shauƙi da zumuɗi. “Dan ALLAH da gaske Yaya?”.
Kansa ya jinjina mata, “Sosai ma kuwa. Ai na cancanci bada tukuyci bisa ƙyautar dana samu mai ɗunbin daraja baby luv”.
Kafimma ya rufe baki ta nufi ƙofa da sauri zata fice. Yay azamar riƙota ganin tana neman kaiwa ƙasa dan zumuɗi.
“oh-ouh nifa a dinga kula saboda ɗan tayina bai gama zama da ƙyau ba”.
Ba wani fahimtar zancen ɗan tayin nan take ba, dan haka ta amsa masa da “to”, dan so take ya saketa ta tafi tai shiri. Fahimtar hakan da yay ne shima ya sashi sakin nata kawai. Amma yayi gaba ta bisa a baya. Waya suka iske Abdull nayi, dan haka Hibbah tai bedroom harda haɗawa da ɗan gudinta…………✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI……_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*
*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
GIPHY App Key not set. Please check settings