Advertisement
*_Chapter Forty Four_*
…………Ba’a ƙaramin harmutse su A.G suke ba. Dan ƙaimin da suke nunawa akan neman master yasa mafi yawan al’umma maida hankali garesu da son ganin yaya za’a kwashe. A gefe kuwa sunyi zaman meeting yafi sau goma shi da su Alhajin Mande. Gaba ɗayansu sun fita hayyacinsu cikin lokaci
ƙanƙani. Babu iyalai babu kuɗi. Dan ma mutane manya irinsu da suke huɗɗar arziƙi nata tura musu kuɗaɗe ana musu jaje. Hakanne ya ɗan sanya zukatansu ƙarfin ringa zaman meeting akan Master ɗin da suka kasa samun bakin zare koda guda akansa. Sai dai ga al’umma sai faman cika baki suke akan suna gab.
Yau ma kamar kullum bayan A.G ya gama da zaman meeting ɗinsu na jami’an tsaro nan yayo gidan hutun Alhaji Mande. Inda gaba ɗayansu sun hallara ne domin tattaunawa tamkar yanda suka saba.
A kallo guda da zaka musu zaka fahimci ɗunbin damuwar dake tattare da rayuwarsu, da yawansu hawan jini neman bugesu yake, wasu kam dama suna da shi ya motsa yana neman fin ƙarfinsu. R.D da yafi kowa jigata ya duba A.G idanu jajur dan sai da ya kora giyarsa yay mankas ko zaiji ɗan sanyi a ransa.
“A.G ya ake ciki ne wai? Har yanzu matsiyacin nan ba’a gano inda yake a fake ba?”.
Kai A.G ya girgiza masa, shi kansa har wata ramar dole yayi a kwana ukun nan. Cikin rauni da ɗacin murya yace, “Lamarinsa ya fara bani tsoro gaskiya. Dukan hanyoyin da muka sani ada da mafakarsa jami’anmu sun shiga amma babu alamarsa. Sannan babban abinda ke ban mamaki ko yaransa su katafila banga alamar zamuga kowa ba, idanma kunyi tunani ya jima baya barin mu haɗu dasu. Anya kuwa yaron nan ba ƙasar nan ya bari ba…”
“Ƙasa kuma? Haba A.G ya kake wannan maganar tamkar ba jami’in tsaro ba. Tayaya zai iya ƙetare wannan ƙasar bayan bala’in da yake ciki ta ko’ina nemansa akeyi. Kadai sake wani tunanin amma ba wannan ba. Idan ma ance yabar ƙasa su kuma iyalanmu fa?”.
Advertisements
“Gaskiya ne Engineer. Nima dai nafi yarda da cewar wanine ya bashi mafaka kodai a cikinmu, kokuma wanda ya sammu, danni nama fara zargin acikinmu ɗin nan akwai maiyi mana SARAN ƁOYE wlhy…”
A harzuƙe Dr Sufi yace, “Haba Alhaji Sallau ya zakai wannan maganar haka babu daɗin ji. Shekararmu nawa tare babu wanda ya taɓa munafuntar wani sai a yanzu da muke a tsaka mai wuya. Naga yaron nan tare ya kwashe mana kuɗaɗe, yay kidnapping iyalanmu. Ta yaya za’a zargi wani kuma banda dai son zuciya!!”.
A harzuƙe Alhaji Sallau ma yace, “Ya kakemin ihu danna faɗi gaskiya. Dan an sace iyalanmu tare an kwashe mana kuɗi sai ya zama lallai zukatanmu ɗaya. Ai wanda ma zai munafuncemu ɗin zai iya yarda a kwashi kuɗin nasa da iyalan dan ya bada ƙafa. Ya dawo cikinmu kuma yana jin sirrikanmu yanda bazamu taɓa sanin ina matsiyacin nan yake ba. Inba da saka hannun wani acikin namu ba tayaya za’ai wannan ɗan iskan yaron da muka raina da hannunmu yafi ƙarfinmu. Yanda kukasan ya mana magani muka dinga barin masa tarin kuɗi a hannunsa mun gagara cewa uwar komai ma sobada mu manyan lusarai ne…..”
Alhajin Mande ya katsesu a tsawace da faɗin, “Kai ya isa haka dan ALLAH. Dr Sufi, Alhaji Sallau ya kamata ku barmu muji da damuwarmu. Idan hankali ya ɓata hankali ke nemosa ba wannan haukar naku ba.”
Engineer da ransa ya ɓaci shima yace, “Faɗa musu dai dan ALLAH. Kai nifa bama irin tunaninku duk nakeyiba a yanzun. Tunanina tun a daren jiya ya karkata ne ga wata katoɓara da mukayi”.
“Tami?”.
Cewar R.D cikin rawar jiki.
Engineer yace, “Ta kawo Halilu cikin al’amarinmu na kwanaki. Bana raba ɗayan biyu Halilu yasan ina yaron nan yake. Kuma ko tantama babu ranar da yazo suka haɗu da shi koda ya fita bai tafi ba laɓewa yay yaji sirrinmu. Kugafa ya yashe masa accaunt shima amma bai ɗaukar masa iyalai ba. Sannan matar tasa da ƴaƴan ɗan uwansa mun aika dan a ɗauka mana su an tarar basu a gidan har wajen aikinsu. Ya kamata ku sakama wannan batun alamar tambaya. Yanda Halilu yake mayen kuɗi ace an yashe accaunt ɗinsa harda kuɗin daya ƙwallafama rai amma zuciyarsa batako bugaba. Wannan al’amari da matuƙar mamaki yake”.
Kusan gaba ɗayansu sun nutsu suna sauraren Engineer ne. A fuskokinsu kuma zaka tabbatar da zancen nasa na shigarsu matuƙa. Alhajin Mande yace, “Wato Engineer kanka naja matuƙa. Kuma wlhy Halilu komai zai iya aikatawa akan kuɗi. Ka tuna abinda sukaima Alhaji Dauda shi da Balele. Karku manta yaranmune fa su, amma yaran nan har wani gasar sayen motoci da gina gidaje sukeyi damu. Bayan mune muka sakasu a harkar nan muka kuma jiƙasu da dukiyar da suke taƙama da ita. Lallai a nemo mana Halilu ya amsa tambayoyi”.
A take duk suka gamsu da hakan. Babu wani ɓata lokaci A.G ya kira yaransa biyu ya aikasu gidan su Hibbah ɗakko Halilu.
(Kawunmu🤔🙆🏻😱).
Advertisements
★★★
Tunda abinnan ya faru Abba baida maraba da zararre. Bashi kawai ba hatta hajiya mama da momy basa cikin hayyacinsu. Yaranma kansu hankulansu a tashe yake. Dan suma ba ƙaramin shanawa suke da dukiyarba gashi yanzu komai an yashe. Ga Junaid babu lafiya hakama Abban. Duk wani motsinsa zakaji yanata surutai da lissafin kuɗaɗe. Koda mai gyaran karaya ma ya dawo domin duba ƙafarsa data goce ranar ansha fallasa. Dan surutai yayta zubawa harda yanda ya ƙulla alaƙa da master. Hankalin su Momy ya tashi, indama ALLAH ya taimakesu dagasu sai su sai ko mai gadi daya taimaka musu suka riƙesa. Mai gyara kuwa basa tunanin ma yana fahimtar inda zantukan na Abba suka dosa. Bayan an kammala gyaran suka sallamesa da abinda ya samu. Surutan Abban ne yasa suka banka masa maganin barci. Koda ya farka kuwa sambatun yake yana kuka da faɗa musu yawan kuɗinsa da master ya yashe.
Hajiya mama da lamarin keta sake birkita mata tunani ta kora su Momy waje ta kulle ɗakin tanama Abba tambayoyi. Bai ɓoye mata komai ba akan kuɗaɗen da yaso handamewa dan mafita yake nema yanzun. Hankalin Hajiya mama a tashe ta yarfa masa mari tana kuka. “Yanzu nan Halilu sokai ka kashemin jikoki kenan? Inda kamin bayani duk yanda zanyi kuɗin su dawo hannunmu ni ai zanyi. Koda kake ganin bana kula su Muhammadu ina sonsu kodan Aliyuna. Uwarsu ce kawai ni bana ƙauna dan bata da tsarki ƴar zina ce. Yanzu ai gashi nan mu bamuci kuɗinba wani matsiyaci ya cinye harda nakan daka tara da guminka. ALLAH wadaranka Halilu lusarin banza. Wlhy ni haihuwarka bata amfaneni da komaiba, dama kai ka mutu aka barmin Aliyuna. Dan ni dai tunda na haifoka duniyarnan banda masifu da tashin hankali babu abinda kake jangwalomin. Ga waɗannan shegun ƴaƴan naka nan riɗa-riɗa a cikin gida suna kallon kansu dai-dai damu babu aure”.
Takaici yasa Abba saka ƙafarsa mai lafiya ya hankaɗa Hajiya mama dake kusa da shi zaune a bakin gadon ta faɗa. Wata irin wahalliyar ƙara ta saki tana dafe ƙugu dan azaba. Da gudu su Momy suka iso ƙofar sai dai kuma a rufe. Yanda Hajiya mama ke ihu da kururuwar ƙugunta yasa dole aka kira maigadi ya ɓalle ƙofar. Kafin su shigo ta haɗa gumi tayi kashirɓan dan azaba. Duk kanta suka rufu, yayinda Abba ya juya musu baya yana kwasar kukansa shima.
Yanda take jera kalaman tsinuwa ga Halilu da gaba ɗaya zuci’arsa ne ya bama su momy mamaki suka shiga tambayarta miya faru?. Cikin kuka da azaba tai musu bayanin shine ya turota a gadon. Bakuma zata yafe masa ba. Sudai komai basu iya sunce ba. Dan sun lura Abban da Hajiya maman neman basu sabon ciwon kai suke bayan wanda suke ciki. Ga gida zagaye da jami’an tsaro an hanasu fita ko ƙofa.
Ganin yanda hajiya maman taƙi nutsuwa ya sakasu banka mata maganin barcin itama dan bazasu iya da kwakwazonta ba. suna ganin ta tafi sukai kama-kama suka kaita ɗakinta suka zubar a gado suka fito. Abban ma maganin barcin suka ɗirka masa dansu sami lafiya.
Wannan abu daya faru a jiyane ya saka ƙafafun Hajiya mama kumbura suntum kafin safiya, dan kuwa dai da gaske taji ciwo a ƙugunta. Hankalin su momy yaɗan tashi sai dai basu wani damuba. Dan sukam dai dama tsohuwar ta gallabi rayuwarsu da hanasu rawar gaban hantsi komai saita saka baki. Suna tsaka da jajanta yanda zasuyi da hajiya mamar sai ga yaran su A.G wai sunzo kai Abba asibiti. Jin hakane yasa su momy cewar a haɗa da hajiya mama. Da farko sunƙi yarda dan Halilu kawai akace su ɗakko. Sai dai gudun kar jami’an da aka zagaye gidan dasu su zargi wani abu tunda su ba nasu bane su duka yasa su kiran su A.G suka sanar musu. Umarnin ɗakkosu duka suka basu, dan a ganinsu ma kawo hajiya maman zaisa Halilu ya faɗi gaskiya ko bayaso ai……
______________________
Tunda ta kammala shiryawa dan harda yin sabon wanka taketa faman leƙen falon. Ji take kamar ta kora Abdull a gidan amma babu dama. Sarai master na sane da ita amma ya basar abinsas cigaba da hirarsu shi da Abdull. Dan abincin ma basu cisa ba sai gab da la’asar. Zuwa sannan Hibbah ta cika da takaici harta koma ɗaki ta kwanta harda su kuka. Kiran sallar la’asar ne ya sata miƙewa ta ɗauro alwala. Koda master ya shigo yin alwalar shima batako kulasa ba. Shima baice mata komai ba ya shige toilet yayi abarsa yazo ya fita.
Bayan sun dawo salla Abdull baima shigo ba shi kaɗai ya dawo ciki. Yanzun ma Hibbah na kwance a inda tai salla tana jinsa tai likimo. Komai baice mata ba ya nufi toilet bayan ya rage kayan jikinsa. Cikin ƙanƙanin lokaci sai gashi ya fito yana raɓar ruwa da alama wanka yayo.
Fitowar tasa tayi dai-dai da miƙewar Hibbah dake faman kumbura baki na haushi. Da sauri ta juya baya saboda kallon datai masa. Shiko ko’a jikinsa ya nufi gaban mirror. Shiryawa ya farayi a nutse yana kallon duk motsinta ta cikin mirror ɗin. Harya kammala baya tunanin tako kalli sashen da yake. Sai da yazo gabanta yana baza ƙamshi cikin ɗanyar shadda getzner dake ta maiƙo da ɗaukar ido ɗinkin haf jamfa na zamani. Duk da ba wannan bane karon farko da Hibbah ta fara ganinsa cikin manyan kaya a fuskar Isma’il, sai ta samu kanta da saki baki tana kallonsa batare dama ta sani ba, dan gani take tamkar bashi baneba wanine daban.
Ɗan duƙowa yay ya hure mata idanu. Ta shiga ƙyaƙyƙyaftasu da saurin kauda kanta zata juya masa baya. Ƙugunta ya riƙo da kamo hanunta na dama ya zuba mata link ɗin da zaisa a hannu. “Miye na juyawar bayan lada kike samu idan kina kallona madam”.
Sake ƙasa Hibbah tai da kanta duk da yana maganar ne da ƙoƙarin ɗago fuskarta dan son su haɗa idanu amma taƙi yarda.
“Fushi kikeyi ne?”.
Ya sake faɗa yana ɗago haɓar tata sosai duk da taƙi kallonsa. Kanta ta girgiza masa da zare hanunta daya zuba mata link ɗin a ciki. Shima komai bai sake cewa ba ya miƙa mata hannun nasa. Cikin son ɓoye kukan dake son taso mata ta ce, “To ka sakeni sai na saka maka”.
Babu musu ya saketa, ta sauke ƴar ajiyar zuciya da fara saka masa link ɗin. “Nagode”.
Ya faɗa a hankali yana binta da kallo. Batace komai ba ita dai. Sai da ya ɗakko ledar da taga ya ajiye a gefen gadon ya saka cikin hannunta ne ya sata ɗagowa ta dubesa. Ido suka haɗa, dan haka ta kauda nata. “Na miye?”.
“Ki saka su ina jiranki a falo”.
Daga haka ya nufi hanyar fita ya barta da binsa da kallo. Iska ta ɗan shaƙa ta furzar tana buɗe ledar ganin ya fita. Sai kuma ta fiddo kayan cikin ledan. Lass ne mai ƙyau kusan kalar kayan jikinsa, sai mayafi babba da takalma da bag masu ƙyau suma. Mamaki ya kamata da tunanin inda ya samosu yaushe kuma ya kawosu ɗakin? Rashin amsa ga kowa yasata fara cire na jikinta ta canja. Sai ga kaya ɗas a jikinta tamkar an gwada. Ita kanta tasan tayi ƙyau koda ba’a faɗa ba, saita samu kanta da sakin murmushi. Tsaf ta shirya ta sake gyara fuskarta, ɗan kunne da sarƙan ta ɗauka a hannu bayan ta saka takalmin ta cire tarkacen takardun cikin bag ɗin ta ɗan jefa turare da ƙananun abubuwa irinsu handkerchief da ɗan Norse mask saboda tsaro.
Master dake zaune a falon yana waya a nutse takun takalmanta yasa shi ɗago idanu ya zubama ƙofar. Ya ɗan fusgo numfashinsa da ke neman harɗewa. Duk da ba tun yau yasan kwalliya na ɗaukar jikin Hibbah ba idan tayi, sai yaga yauɗin ta zamar masa ta musamman. Dan ta fito a amryarta ne ƴar gaske abin sha’awa. Ga ƙuruciyarta ta bayyana kanta tamkar amaryar ƴan shila😜.
Harta ƙaraso garesa baima sani ba. Daga can sai faman hello-hello wanda suke wayar ke faɗa amma bama yajinsa…
“Yaya dan ALLAH ka samin”.
Maganarta ta katse masa tunani har yaji hello ɗin wanda suke wayar. Yanke kiran yayi yana jan ɓoyayyar ajiyar zuciya tare da miƙa mata hannunsa ta ɗora masa sarƙa da ɗan kunnen. Hannun nata ya kamo ya zaunar da ita akan cinyarsa. Hibbah ji take kamar ta nutse dan kunya. Amma dai ta daure ta dake zuciyarta. Ɗan kunnayen ya fara saka mata. Kafin sarƙar. Yanda numfashinsa keta sauka mata a jiki sai faman matse jiki take. Shi kansa kasancewar tasu a haka ba ƙaramin canja masa salon gudin jini yake ba, ya dai daure ya gyara mata sarƙan bayan ya saka da gashinta daya fito ta ƙasan ɗan kwalin kasancewar irin ɗaurin nan tayi da ake yayi.
“Nagode”.
Ta faɗa a hankali tana miƙewa daga jikinsa. Idanunsa kawai yaɗan lumshe da jinjina mata kai shima ya miƙe. Gaba yay ta bisa a baya, su dukansu sunajin wani shauƙi a ƙasan zukatansu wanda basusan kona minene ba. Tunda suka fito compound ɗin Abdull keta ƙyalla musu hotuna dan yanda suke tafiya a jere gwanin birgewa. Daka gansu kaga ango da amarya da ke ji da tashen more lokacinsu. Master da ya harari Abdull da yaƙi daina hotunan ya buɗe ma Hibbah baya da mata nuni da ta shiga. Shigar tayi, sai da ta zauna ya ɗan ranƙwafo ya gyara mata mayafinta daya sakko sannan ya rufe. Shima shi da Abdull suka shiga.
Su Habib dake laɓe suma sunata musu hotuna harda masu video suka shiga tafawa da juna suna dariya ganin motar ta fice. “Wayyo soyayya ruwan zuma”. Cewar Khalid yana dariya.
Salis yace, “Bari kawai master zai ƙonemu a gidan nan. Babban yaya ashe ya iya soyayya haka kallon tara saura kwata yake mana”.
Dariya suka sanya su duka kowa na faɗin albarkacin bakinsa cike da shaƙiyancin su. Sai dai zukatansu fal suke da tarin farin ciki dan burinsu dama suga master ɗinsu a cikin nishaɗi da farin cikin rayuwa tamkar yanda suma yake burin ganinsu akoda yaushe………✍
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI……_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*
*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
GIPHY App Key not set. Please check settings