TAKUN SAKA 47

Advertisement

*_Typing📲_*

_______________________
*_MATAYEN ƘWARAI KUNA INA NE?._*
_Maza ku garzayo da gudunku ga ƴar zuru mamar zee-zee mai kayan mata na maida tsohuwa yarinya💃🏻._
*Kayan matan ƴar zuru zasu maidaki shalele ƴar gaban goshin maigida koda kina da kishiya ƴar birnin shehu😂💃🏻*.
_Kayan ƴar zuru nada matuƙar sirrika da inganci irin wanda sai an gwada akansan na ƙwarai. Idan da ƙyautar gida akemiki a master room kikai amfani da kayan ƴar zuru Nigeria za’a baki harda jirigin sama na yawata ƙasashen duniya😉💃🏻_.
*MUNADA KAYAYYAKI KAMAR HAKA*👌🏻
Kaza akwai 10k
15k
5k
Tsimi 5k 10k
Matsi 5k
Gumba uku 2k 
Zumar gorun tula syrup3k
Garuka 3k
Cicccibi 5k
Zakara 20k
Zabo20k
Humra 
Turaren tsugunni 
Butar tsarki
Maganin infection
Tsimin tabaje 
Turaren al,ajab 
*Muna maraba da maisayen ɗaya ko sari, kayanmu garantee ne in har basuyimaba zan maidama kudinka*.
 
_Address maberar jariri bayan FGC sokoto_ 
08068526455
*Zaku iya saving number ta domin ganin hajata*
Zaku iya samun mu amanhajar
Facebook
Istagram
Yar_zuru_mamar_zeezee- kyn_mata.
Sai kunzo🥰🥰🥰🥰💃🏻👌🏻.
_____________________
*_Chapter Forty Seven_*
……….Su Hibbah na baje a falo suna kwasar hira ita da su Zahidah dake ta mata sheri itama cikine da ita, dan ta matsa musu tunda ta ƙyalla ido taga cikunna a jikinsu. Shinefa suma suka tasata gaba da nasu tsokanar Ammar na tayasu da dariya wai wayaga auta da ɗa. Tun tana kai ƙararsa wajen su Yaya Umar harta koma jifansa da throw pillows tana kukan taɓara.
         Hatta Ummi kasa daurewa tai saida tai dariya dan taɓarar autar tata sai ita. Kiran da yaya Abubakar yayma Ummi ne ya sanar mata bazai kwana a gida ba ya sakasu barin Hibbah ɗin suka koma hirar rashin dawowar Master shima. Suna cikin zancen kuma sai ga ɗan halak ɗin ya kira Ummi shima ya sanar mata Hibbah zata kwana anan shi wani uziri ya riƙesu tare da yaya Abubakar. Addu’a tai musu na fatan alkairi baki ɗaya.
      Yana katse kiran kuma ya kira Ammar yace ya haɗasa da Hibbah. Amma ya jata gefe dan yasan halin kayarsa. Da ƙyar Ammar ya danne dariyarsa ya kama hannun Hibbah suka nufi bedroom ɗin Ummi.
      Zatai magana ya manna mata wayar a kunnenta ya fice. Hibbah dake hararar Ammar dake mata gwalo zai fice tace, “Mai kan gwanda kawai”.
         “Nine mai kan gwandan?”.
Sassanyar muryarsa ta daki dodon kunnenta a bazata. Dan tama manta waya Ammar ya saka mata a kunne. Idanu taɗan waro tamkar tana gabansa. “ALLAH shine shaida ni dai bada kai nake ba da yaya Ammar nake”.
        Master dake goge jikinsa dake raɓar ruwan wanka da ga can yay murmushi yana ɗan lumshe ido. “Ki shirya ganinan zuwa zan ɗaukeki”.
       Kamar tana gabansa ta marairaice fuska. “Dan ALLAH ka barni na kawana wajen Ummi”.
      “Idan na barki ni kuma na kwana da wa?”.
     Ƙasa-ƙasa batare da tunanin zaiji ba ta ce, “To da dawa kake kwana?”.
“Okay hakama zakice, to nama fasa barin ki shirya kawai”.
      “Dan ALLAH kayi haƙuri bazan sake ba”.
      Yanda tai maganar da alamar kuka ya sashi danne dariyarsa da ƙyar. “Idan na barki duk bashin da kikaci zaki biyasa in kin dawo”.
      Da yake so take a barta babu tunanin komai tace ta amince. 
    Murmushi ya sakeyi yana ƙoƙarin shiryawa. “Okay tunda hakane sai ki fara da sumba ɗaya ƙwaƙwara yanzun nan kona taho”.
      “Ni dai a’a dan ALLAH”.
“Oh to ki shirya ganinan zuw…..”
       Kafinma ya rufe baki ta mannama wayar kiss da yazo masa cikin kunne a bazata. Sai kuma ta yanke wayar ƙitt. Duk yanda yaso dannewa ya gagara sai da yay dariya yana girgiza kansa da ajiye wayar ya cigaba da shirinsa.
         Gudu-gudu yay shiri ya fito dan su Habib na jiransa a falo. Barka da fitowa suka shiga yimasa har yakai zaune. Lap-top ɗin dake ajiye saman centre table ajiye ya ɗauka yana gyara zamansa ƙafa ɗaya kan ɗaya. Cikin maida hankalinsa ga abinda yake a ciki ya fara magana batare daya kallesu ba. “Salis, Khalid, Habib. Kune zaku shiga cikin gidan. Khalid kaine zaka fara bubbuɗe ko ina ta yanda idan ya farka zaiyi tunanin kuskure akai wajen buɗesa. Sannan Salis ka tabbatar ka ajiye dukkan abinda zai iya gani da zai taimaka masa neman su A.G a farko kafin kowa, ko cikin yaransa. Da zarar kun kammala duk wannan Khalid sai kai masa allurar da Abdull ya baka. Kasancewar tanada ƙarfi zai saurin farkawa ya kuma dawo hayyacinsa da wuri. Habib zai amfani da wannan damar ta komawa da ga can ta bayan Windown ɗakin da yake ciki kayi wayar ƙarya akan abinda zaka shirya kansa a halin yanzu. Daga nan sai ku koma tacan sama bayan ƙarfen nan ku ɓuya har sai ya fito a gidan sannan ku kirani”.
      Cikin girmamawa suka amsa masa. da hannu yay musu nunin suje, tare da cilla musu key ɗin mota. Salis ya cafe.
    Sai da suka fice ya ɗago ya duba Adam tare da miƙa masa key ɗin Napep. “Kaje ka jira a bakin layin, da zaran sun kira ya fito ka ɗaukesa zuwa duk inda ya sanar maka zaine. daga nan na sani”.
       “Okay Master”.
Adam ya faɗa shima cike da girmamawa.
     Bayan fitarsa shima yaɗan cigaba da aiki, bayan wasu mintuna ya dubi Musbahu da Idris da Zaidu. “Nasan da ya samu damar fitowa babu wanda zai nema a halin yanzu sai yaransa biyu daya yarda dasu fiye da kowa bayan ni. Dage, da Katafila, Musbahu, Zaidu baku da matsala da hakan, dan kun iya komai nasu, ga wayoyinsu nan sai ku ɗauka, zaku haɗa hannu da Adam wajen kaisa inda su A.G suke”.
       Suma cikin girmamawa suka amsa masa tare da ɗaukar keys ɗin mashin guda biyu da wayoyin suka bar wajen domin zuwa suyi nasu shirin. Ya dubi Idris daya rage, “Kai kuma zamu kasance tare da kai anan domin bibiyarsu da ga nan har zuwa lokacin dazan fita”.
      Kansa ya jinjina masa shima, tare da neman waje ya zauna. Waya Master ya ɗauka, yay kiran yaya Abubakar da ya kammala haɗa jami’an da zasuyi aikin tare a can, bayan sunyi magana akan duk yanda tsarin zai kasance ya ajiye wayar da maida hankalinsa ga Idris.
_______________
        Tafiyar kusan mintuna talatin da wani abu ya kai su Habib inda suka nufa, gida ne madai-daici dake cikin sabuwar anguwa, duk da akwai duhun dare haka suka ajiye motar acan baya da gidan sosai suka ƙarasa da ƙafa. Kamar yanda Master ya tsara musu suyi basu ƙetare magana ko guda ba duk sukayin. Bayan Khalid ya kammala nasa aikin na bubbuɗe ko ina ya shiga ɗakin ƙarshe daya buɗe. Ƙugu ya riƙe yana maibin ɗakin da kallo hannunsa ɗaya rufe da hanci, lafiyayyen ɗaki ne madai-daici mai ɗauke da toilet a ciki, sai gado ƙarami na ƙarfe irin na ƴan makaranta da kwanon cin abinci da kofi. Daka gani dai ɗakin baida maraba dana ƴan prison. Cikin nutsuwa ya tsaida idanunsa akan mutumin dake kwance bisa gadon fuskarsa buzu-buzu da gashi har kansa kai kace mahaukacine. Yayi datti matuƙa, na jiki dana sutura, ga wani wari dake fitowa daga jikinsa mai ban tashin hankali. Sai dai babu alamar yunwa tattare da shi ko kaɗan. Khalid ya ɗanja numfashi da ɗage kafaɗa yana zaro syringe dake ɗauke da ruwan allura a aljihunsa. Matsawa yay jikin gadon yayma mutumin, yana zarewa bai tsaya wasa ba yay wuff ya fito da ga ɗakin yanama Habib ƙaramin fito alamar ya kammala nasa aikin.
      Rufe bakin Khalid keda wuya mutumin ya farka, zumbur yay ƙoƙarin miƙewa, sai dai azabar data ziyarci jikinsa na harbin dake a hannunsa da ƙafa wanda Master yazo yay masa shi a daren shekaran jiya tamkar yanda akai masa ya sashi sakin ƴar ƙaramar ƙara. Sai da ya ɗan ja numfashi sannan ya ƙarasa miƙewa da ƙyar yana cizar lip ɗinsa na ƙasa. Ɗakin yabi da kallo cikin ƙunar rai da zuciya, tsahon shekaru biyu kenan yake a ciki batare da yasan wanda ya kawosa ba. Tun yana gwada ƙoƙarin fita harma ya haƙura yasama sarautar UBANGIJI ido. Ana bashi abinci wadatacce ana kuma kula da lafiyarsa. Amma akan bugar da shi da maganin barci a wasu lokutan ta hanyar abincin da ake bashi. Kamar shekaranjiya, sai da aka buhar dashi sannan aka harbar masa ƙafarsa da hannu. Gigitar shigar bullets da azaba ya sashi farkawa, sai dai baiga wanda ya harbesan ba dan harya fice a ɗakin, sai bayan kusan awa guda ya jigata matuƙa sannan yaronsa daya yarda da shi fiye da kowa ya shigo, cikin wata sabuwar azabar ya cire masa bullets ɗin yana zuba masa maganganun da har yanzu daya farka bazasu bar gigitashi ba. 
      Jin kamar ana magana ta bayan window ne ya sakashi nutsuwa yana saurare. Tabbas komai ya shiga kunnensa, tamkar yanda Master yay fata kuma yayi yunƙurin ganin ya gwada miƙewa ya gudu. Cikin azabar zogi da ƙafarsa ke masa da raɗaɗi ya miƙe da ƙyar, dan bayan cire bullets ɗin ko paracetamol Master bai bashiba dan rage zafin ciwon. Gwada buɗe ƙofar yayi, sai ko gata ta buɗe. Jikinsa har rawa yake wajen turo illahirin jikinsa waje sosai dan gani yake mafarki yake tamkar yanda ya saba. Sai dai ganin ya fito falon sosai ya sashi saki wata dariyar ƙunar rai da zuciya. Tare da jerama kansa kirari irin na gawurtattun arnan saman dutsin nan. Cikin tafiyar dake nuna ƙashin kafafunsa sunyi sanyi saboda zaman waje ɗaya ya nufi hanyar fita ƙofar falon, dan ya haƙƙaƙe a ransa yau zai bar gidan nan koma ta halin yaya ne. Duk inda auta (Master yake cema auta) yake sai ya halaka rayuwarsa kafin kowa. 
        Ba kai tsaye suka buɗe masa ƙofar falon ba dan karya zargi komai, sai da ya ɗan sha wahala kafin ta buɗe duk tunaninsa ƙwazonsa ne. Daga falon ma zuwa tsakar gidan da ƙyar ya iya isowa ƙofar waje, sai dai itafa a rufe take dan haka yay tunanin haura katanga. Kasancewar dukanin hanyar da zata bashi sauƙi na barin cikin gidan sun bar masa ya samu damar haura katangar tunda dama horarrene ba saboba. Dukan abinda ke faruwa su Habib na kallonsa harya fito cikin layin, ya jima a kwance bayan dirowarsa daga katangar kafin ya ƙara tashi ya fara tafiya cikin haɗa hanya, cikin sauri Habib ya dannama master waya ya sanar masa.
       Sosai Master yay mamakin yanda aikin ya tafi a sauƙaƙe, yanke kiran yay ya maida ga Adam. Adam dake daga farkon layi a napep yana gani ya ɗaga cikin sauri.
        “Maza ka tada napep ɗinka ka taresa gashi nan zai fito”.
     “Okay master ”. Adam ya faɗa yana ƙoƙarin sakama napep ɗin key. Cikin azama yabi umarnin Master. Cikin ɗan shawagi tamkar ya ajiye mutum ya shigo farkon layin, yay reverse kamar zai juya ya fita cikin sa’a ya haske mutumin. Ƙasa yay da fitilar sai kuma ya sake haskashi. Tabbatar da shi ɗinne ya sakashi burga napep ɗin zuwa gabanshi, Cikin hanzari ya fito yana ambaton “Subahanallahi mai gida kana lafiya kuwa?”.
     Hannu kawai mutumin ke iya jinjina masa, cikin matuƙar wahala ya fara magana. “Ka fitar dani a layin nan yanzu-yanzu, ko nawane zan baka saurayi”.
      “Babu damuwa baba, kaga taho muje, ko’ina kakeso zan kaika, ina fatan dai lafiya”.
        Bai iya bama Adam amsa ba harya taimaka masa ya shiga napep ɗin, sai da Adam ya tada napep ɗin suka bar layin ya dubesa daga kwancen da yake a baya. “Yaro ko zaka aramin wayarka?”.
      “Babu damuwa baba gata”.
Kamar yanda Master yay hasashe number *Katafila* kuwa ya fara lodawa a wayar ta Adam ɗin, da farko bata shiga ba kamar yanda suka tsara, sai a na biyu. Koda ta shigan kuma su Zaidu basu ɗaga ba harta yanke. Sai da ya sake kira cikin tashin hankali dan sune kaɗai damarsa a yanzun. Tana gab da tsinkewa Zaidu ya amsa. 
         Cikin muryar gawutattun marasa ji irinsu Katafila Zaidu ya fara magana. “Kai waye da duhun daren nan hakane?”.
       Wani sanyi ne ya ratsa zuciyar mutumin, sanin halin katafilansa baya son jira ya fara magana da sauri-sauri. “Master ne Katafila na!”.
      “What!!?. Kai ALLAH ganganne wannan, gagarar da mukai mukune ta sakaku fara canja layi na yi mana shigo-shigo da oga. To ku sani bazaku taɓa sani kojin komai ba dan oga ya muku zarrah”.
      A karon farko master ya kece da wata shegiyar mahaukaciyar dariya da har ta bama Adam tsoro da mamaki. Duk da a yanda yake haka ya fara jerama Katafila kirarin da shi kaɗaine ke masa shi duk duniya. Cikin nuna alamar mamaki da ga can Zaidu yace, “Kai oga!!”
       “Tabbas nine Katafila. Ka fadamin kuna ina dan ma kuɓuta daga hannunsu, maza faɗamin”.
         “A’a oga, kai dai faɗamin inda zamu sameka gani nan ni da Dage a ɓoye muke muma saboda farautarmu da ake dare da rana tun bayan ɓacewarka”. 
       Wani sanyi ne ya ratsashi na daɗi, ya mikama Adam wayar akan yayma su Katafila ɗin kwatancen inda zasu haɗu. Babu musu Adam ya amsa ya kwatanta musu yanda Master ya tsara musu dama tun farko. 
          Turyan-tiryan Adam ya isa har inda su Zaidu suke, waɗanda gaba ɗaya sun canja kamanni daka gansu kaga ƴan sara suka zam. Sai wani rangaji suke da magana uwa ta bugaggu. Cikin wata irin zabura master ya miƙe zaune saboda jin muryar su Dage, suma ihu suka buga da faɗawa cikin napep ɗin suka cikuykuyesa a dole su murnar ganinsa sukeyi. Adam ya danne dariyarsa da ƙyar yana toshe hanci, dan tunda ya ɗakko master wani shegen wari ke bugar hancinsa. Su kansu su Zaidu da ƙyar suka iya daurewa warin nan. Harda hawayen drama kuwa sukayi su a dole ogansu ya dawo.
         Adam dake nuna kamar a tsorace yake dasu, cikin marairaicewa yake tambayarsu ina zai kaisu?. Musbahu (Katafila) ya duba Adam ɗin sheƙeƙe ya ɗauke kansa yana maidawa kan master. “Oga ko’ina a hargitse take a yanzu haka. Dan wani na amfani da sunanka yana ɓarna ta maƙudan kuɗaɗe, inaga yanzu babu inda ya dace mu kaika sai wajensu A.G, sune kawai zasu baka mafaka har komai ya lafa”.
           kai kawai master ya jinjina musu, dan har yanzu ya lura basu fahimci akwai harbi a jikinsa ba. “Ni yanzu banda lambar kowa, tayaya kenan zamu sami wani a cikinsu?”.
      Zaidu (Dage) ya zaro ruɓaɓɓar wayarsa, “Ai oga kwantar da hankalinka, inada ita a zane kan kwakuletata bara a danna mas kira”. Batare da ya jira cewar master ɗin ba ya dannama A.G kira. Ba’a ɗaga ba sai da tana gab da tsinkewa. A.G dake a tsakkiyar su Alhajin Mande ana sabon meeting yay musu alamar suyi shiru yana kaiwa kunne.
         Daga nan Zaidu yace, “Hallo yallaɓai Dage ne na master mai jurar wahalar duniya!”.
      “What!?”.
A.G ya faɗa yana miƙewa a zabure. Zaidu dake saurarensa yace, “Yes yallaɓai. Yanzu haka muna tare da oga mun tsintosa acan bayan gari, ya kuma tabbatar mana kai kawai yake son fara gani dan bakinsa da goro…”
       “Kai dalla saurara bana son yaudara. Ni shegen yaron nan zaice yana son gani bayan ya halaka rayuwata, kama tabbatar masa inhar ya bari idona yaga nasa to ko kashinsa wani bazai gane ba ok;. Yana gama faɗa ya yanke kiran.
      Duk da Zaidu yaji mi A.G ɗin ya faɗa sai cewa yay ai yace su ƙarasa yana gidan hutun Alhajin Mande. master dai bajin A.G yay ba, dan haka ya aminta kawai dan yasan su Dage bazasuci amanarsa ba. Zaidu ne ya dinga nunama Adam hanya duk da kuwa shima ya sani sarai.
____________________________
       Dukkan abinda ke faruwa Master yana saurarensu ne tiryan-tiryan da ga gida, dan haka yanajin sun ɗauka master ya miƙe ya hau shiri a gaggauce. Yanayi yana waya dasu Yaya Abubakar da suma ke shiri daga can station. Yayinda su I.G suma ke daga can suna jiran tsammani dan Master ya kirasu akan samun inda ainahin master ɗan ta’adda yake a daren nan. Cikin kanƙanin lokaci Master ya fito cikin shiri yana soke bindigu biyu cikin jikinsa.
       “Idris ka kula da komai yanda ya kamata. Ko yaya ka fahimci matsala da ga su Adam kai saurin sanarmin dan su A.G sun wuce dukan tunanin mai tunani.”
       “Okay Master ALLAH ya bada nasara”.
     Kai kawai Master ya jinjina masa. sai da ya je ƙofa ya tsaya yay addu’a kafin ya fice cikin zafin naman da ALLAH ya azurtashi da shi. Mashin ɗin dake can gefe a fake ya nufa, sai da yay addu’a nanma ya haye samansa yay masa key. Da sauri maigadi dayaji motsinsa ya fito ya buɗe masa gate ɗin.
      Akan hanya Master dasu Yaya Abubakar suka haɗu, su kusan ashirin duk cikin shirin kota kwana. Tun a farkon shiga anguwar datai tsitt alamar mutane sunyi barci suka faka motocin da suke ciki. Duk fitowa sukai, hakama Master ya sauka a mashin ɗin nasa yana sauraren abinda ke faruwa daga can ta ɓangaren su Zaidu ta abin da ke a kunnensa. Cikin tawagar yaya Abubakar ɗaya ya karaso gaban Master ɗin da bullet proof jacket ya saka masa. Yana gyara masa ita suna magana da yaya Abubakar akan yanda zasu zagaye gidan hutun na Alhajin Mande da su A.G ke a ciki suna sabon meeting…….
       Acan ɓangaren su A.G kuwa a kiɗime yakema su Dr Sufi bayanin wai yaron master ne ya kirashi akan ga master ɗin nan yana son zuwa inda suke. A zabure suma suka miƙe har suna haɗa baki wajen ambaton sunan master ɗin.
        Engineer yace, “Anya kuwa ba wata gadar zare yake neman ƙulla mana ba?”.
       “Komaima zai iya dan yaron nan shaiɗanine. Amma karku manta a yanzu muna a gaɓar neman mafitane akan iyalanmu da dukiyoyinmu. Ina ganin kodai yarasa yanda zaiyi ya gudu ko makamancin haka shiyyasa ya dawo garemu”.
        “Tabbas maganarka na’akan hanya R.D, inaga mu bashi damar zuwan amma mu taresa cikin ɓadda kama muma”.
       Duk sun gamsu da zancen Alhaji Sallau, dan haka a take A.G ya danna kiran no ɗin da su Zaidu suka kirasa. Bugu biyu kuwa suka ɗaga sai dai basuyi maganaba. Dr Sufi daya amshe wayar a gadarance yace, “Yazo muna jiransa”.
      Batare daya jira cewar su Musbahu ba ya yanke wayar. Murmushi sukayi suna kallon juna batare da master ya lura ba dan kwance yake har yanzu jikinsa babu ƙarfi. Cikin ƙanƙanin lokaci suka iso dan dama dai suna gab. Maigadi da dama yasan da zuwan nasu sunayin horn ya leƙo cikin kare fuska da suka haske masa. “Wane mara mutuncine haka wai?”.
       Dira Musbahu da Zaidu sukayi sunama maigadi kurari, ƴar hararar su yay sannan ya fara maƙyarƙyata irin dai ya tsoratan nan. Zaidu ya kai masa halbi yana zagi da faɗin, “Mara mutunci kaine zaka goya oga har cikin gidan nan kuwa. Maza zoka duƙa ya hau bayanka. Bin umarninsu yayi, cikin rawar jiki yazo ya tsugunna, Adam ya taimakawa master ya hau bayan maigadi. Suna ganin ya shiga cikin gidan suka koma napep Adam yaja suka kauce dan Master daga can yana sanar musu suyi maza subar wajen suna gab da gidan.
       Su A.G na ɓaɓɓoye maigadi ya shigo goye da master yana nishi da ƙyar, zubesa yay ƙasa kusa dasu Abba da zuwa yanzu da ƙyar suke numfashi dan azabar wahala. A.G ne ya fara fitowa da sauri a inda ya ɓuya riƙe da bindiga. Maigadi ya ɗaga hannu sama yana makyarkyata daja baya. “Oga ka rufan asiri ka sauke wannan abar, baƙone gashinan, ya kuma tabbatarmin kunsan da zuwansa”.
     A.G dake tsaye kan master da bindiga yayma maigadi nuni daya fita. Da gudu kuwa ya fice har yanacin tuntuɓe. Bai tsaya a gate ɗin ba yay waje bisa umarnin Master shima.
        A.G dake bin master da kallon mamaki cikin daka tsawa yace, “Munafuki da wannan salon kazo kuma? To ai ka makaro dan zuwa yanzu mu babu abinda zakai ka layance mana”.
         Da mamaki master ke duban A.G ɗin. “A.G kardai kace baka ganeni ba. master ɗinku ne fa, kodan ka ganni da wannan gashin buzu-buzu, ku bani abun aski na saukesa nasan zakufi fahimta ta”.
       Harbin ƙafarsa A.G yayi a fusace. master ya saki wahalalliyar ƙara. A dai-dai nan suma su R.D dake laɓe suka fito kowanne hannu da makami. Zasu fara lugudarsa ya zabura gefe cikin magiya da roƙon su saurareshi. Dan sai yanzune ya tuna cewar su Dage sun sanar masa akwai wani Master dake basaja da shi yana aiki. Ya buɗe baki zai fara musu bayani kawai sukaji an banko ƙofar falon da masifar ƙarfi har sai da suka zabura. Su Master ne da suka shigo cikin gidan da sanɗa. Tamkar ƙyaftawar ido sukaima su A.G zobe a cikin falon.
       Yaya Abubakar ya daka musu tsawa akan su ajiye makaman hannunsu koya fasa kan mutum. Cikin rawar jiki dabin ƴan sandan da kallon mamaki su A.G auka shiga ajiye abubuwan hannunsu suna ɗaga hannaye sama na alamar surrender.
      Master daya kasance shi kaɗai a waje ya shigo falon cikin takun izzarsa da ƙasaita yana tafa hannaye. Gaba ɗayansu suka maida hankalinsu ga ƙofar dan son ganin wanene zai shigo. A wani irin zabure duk sukai baya, domin ganin wani Master ɗin kuma. Suka duba yaya Isma’ill suka duba master na ainahi dake zaune shima yana dubansa. Kafin wani a cikinsu ya sami damar cewa wani abu Master yakai hannu bisa face ɗinsa ya zare mask ɗin dakesa su kallesa a master ɗan ta’adda. Sai ga fuskarsa ta ainahin Muhammad Shuraim da jami’an tsaro suka sani ta bayyana.     
         Master yakai zaune yana wata shaƙiyyar dariya da ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya ya kaɗa musu yatsun hannunsa uku. “Hy! Guys”. Yay magana da muryar master ɗan ta’adda. Cikin sake rikicewa suka dubesa, suka dubi master dake zaune fuska buzu-buzu da gashi. A zafafe master ɗan ta’adda ya nuna Master yana girgiza musu kai, “karku yarda da wannan matsiyacin yaron, bakowa bane face yarona, shine ya ari dukkanin salona yazo muku a suffata bayan ya ɗaukeni ya ɓoy…….”
         “Relax! Relax oga. Miye na zazzari bayan nima da kaina zan iya faɗa”. Isma’il (Master) yay maganar cikin tsantsar rainin wayo da kai hannu saman face nashi ya shafa a hankali.
     “What!!!?”.
A.G ya faɗa cikin rawar jiki har yana neman faɗuwa. Hakama su Alhajin Mande wani irin aradu ne ya saukar musu bisa kawuna cikin ƙanƙanin lokaci, Abba dake kwance duk yanaji da ganin komai ya saki wani marayan kuka ianunsa akan yaya Abubakar sa Master.
            Master dake dubansu yana murmushi ya tsaida idonsa akan A.G. “Haba ɗan sanda ya da firgita haka?! A tunaninka kaine kawai ka iya mufunci da salon makirci nacin amanar ƙasa? No, no my dear akwai ƴan iska a saman iyawarka masu tasowa irina!!!!”.
      Master yakai ƙarshen maganar a matuƙar hargitse yana doka hanun kujera da ƙarfi tamkar face nashi zatai aman wuta. Basu kawai ba, hatta su yaya Abubakar kallon razana suke masa. Dan gaba ɗaya ya juye musu tamkar bahagon zaki, Abba da gaba ɗaya suffar Master ta dawo masa irin ranar daya illata Junaid ya fara rawar jiki da faɗin, “Wlhy shine, shine wlhy A.G. shine ya illatamin yarona!”.
       Ina babuma wanda yasan yanayi duk da kunnuwansu na saurarensa. Yaya Abubakar ya fahimci idan Master yay fushi babu sauƙi, dan koyaya kuke da shi sai kaji shakkar koda kallonsa ne. Ganin Master ya ɗauka bindiga Yaya Abubakar yay saurin nufosa, sai dai kafinma ya iso harya harbata a ƙafar A.G. wata irin gigitacciyar ƙara A.G ya saki da kaiwa ƙasa durƙushe. 
          Cikin gargaɗi da waro manyan idanunsa masu tamkar zaki ya ke nuna A.G da ɗan yatsa. “Wannan harbi ne na razana matata da ka dingayi!!”. 
        Wani irin kuka A.G keyi na azaba, zufa ta gama wanke jikinsa sharkaf kamar wanda yay wanka. Yaya Abubakar dake ɗan bubbuga kafaɗar Master ɗin alamar lallashi yace, “Please Cool down Shuraim”.
     Komawa Master yay ya lafe jikin kujerar yana saki tagwayen ajiyar zuciya a jajjere. Ji yake kamar ya harbesu baki ɗaya tun anan ya huta kawai. Dubansa yakai ga ɗaya a cikin yaransu na ƴan sanda. “A ciremin gashin fuskar wannan”.
        Cikin saurin ɗan sandan yace, “Okay sir”. Yana nufar master da zuciya ta kumesa, ji yake kamar ya miƙe ya damƙi Isma’il (Master) yay gunduwa-gunduwa dashi. Dan babu abinda ke masa kaikawo a rai sai irin ɗunbin ƙaunar daya nuna masa a baya da yarda ta haƙiƙa, ashe shi ɗin jami’in tsaro ne dama. Cike da mugunta ɗan sanda ɗaya ya kama hannayensa ya banƙare ta baya yasa masa handcup, wani ya duƙa ta gabansa ya fara aske gashin fuskarsa dake buzu-buzu. azaba ta saka master fara ihu dan aski ne mai kama da ana tsigar gashin da hannu dan azaba.
        Sauke gashin da aka gamayine tsaf ya bayyana ainahin fuskarsa. Tabbas su A.G sun sake tabbatar da wannan shine master ɗinsu, suna mamakin taya akai basirarsu ta toshe haka har suka gagara fahimtar badashi suke tare ba sai a yau da guri ya ƙure musu. Wayar Master ce ta katse musu tunani.
           Yana zaune har yanzu ƙafa ɗaya kan ɗaya tamkar wani jinin sarauta. Magana yake cikin fushi da harzuƙa. “Sir a yanzu haka mun sami nasarar kamashi tare da iyayen gidansa, sai dai dalilin gaddamar da sukai mana kowannensu ya samu harbi”. Ya ɗanyi shiru alamar saurare. Sai kuma yace, “Okay sir” yana sauke wayar a kunnensa. Da idanu yayma zaratan ƴan sandan dake tare da su magana. Kamar jira suke suka shiga ɗana kunamun bindigunsu. Rikicewa su R.D sukayi dan tunaninsu kashesu Master ɗin yace ayi. Kafin suyi yunƙurin tashi ƴan sandan nan sunbi ƙafafunsu da harbi tako ina. Cikin ƙanƙanin lokaci falon ya rikice da ihu, Hajiya mama dake a sume ta kawo numfashi, dan duk abinda ake ita bama ta sani ba. Yaya Abubakar kuwa sarai ya ganta ita da Abba ya nuna baima san da zamansu a wajen ba dan Master ya bashi dukan bayanan Abba ya gani.
          Cikin abinda bai wuce mintuna goma ba sai gasu kwance wanwar a ƙasa suna ihu da kururuwar azabar harbin da suka sha, a dai-dai nan ƴan sandan da I.G ya sake turowa suka iso gidan tare da tawagar wasu ƴan jarida duk da kuwa asubahi ma tayi…………✍
*_MATAYEN ƘWARAI KUNA INA NE?._*
_Maza ku garzayo da gudunku ga ƴar zuru mamar zee-zee mai kayan mata na maida tsohuwa yarinya💃🏻._
*Kayan matan ƴar zuru zasu maidaki shalele ƴar gaban goshin maigida koda kina da kishiya ƴar birnin shehu😂💃🏻*.
_Kayan ƴar zuru nada matuƙar sirrika da inganci irin wanda sai an gwada akansan na ƙwarai. Idan da ƙyautar gida akemiki a master room kikai amfani da kayan ƴar zuru Nigeria za’a baki harda jirigin sama na yawata ƙasashen duniya😉💃🏻_.
*MUNADA KAYAYYAKI KAMAR HAKA*👌🏻
Kaza akwai 10k
15k
5k
Tsimi 5k 10k
Matsi 5k
Gumba uku 2k 
Zumar gorun tula syrup3k
Garuka 3k
Cicccibi 5k
Zakara 20k
Zabo20k
Humra 
Turaren tsugunni 
Butar tsarki
Maganin infection
Tsimin tabaje 
Turaren al,ajab 
*Muna maraba da maisayen ɗaya ko sari, kayanmu garantee ne in har basuyimaba zan maidama kudinka*.
 
_Address maberar jariri bayan FGC sokoto_ 
08068526455
*Zaku iya saving number ta domin ganin hajata*
Zaku iya samun mu amanhajar
Facebook
Istagram
Yar_zuru_mamar_zeezee- kyn_mata.
Sai kunzo🥰🥰🥰🥰💃🏻👌🏻.

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like