Advertisement
*_Typing📲_
________________qq
*_MATAYEN ƘWARAI SARAKAN ADO DA ƘAWATA JIKI DA KWALLIYA KUNA INA NE?._*
_Maza ku garzayo da gudunku ga mutunuyar taku maida tsohuwa yarinya ta sake dawo muku da sabon salo, sabon sunfarin kayan gyaran jiki na mayika da sabulai ƴan gaske💃🏻._
*Kayan kwalliya na mg’s skin care zasu maidaki shalele ƴar ƙwalisa tamkar wata ɗan daren sha biyar koda kina da kishiya ƴar Morocco bata girgizaki ba, balle saurayi ɗan son ƙyale-ƙyale da ƙawa ga burwallensa😂💃🏻*.
Advertisements
_Kayan mg’s skin care nada matuƙar sirrika da inganci irin wanda sai an gwada akansan na ƙwarai.
*MUNADA KAYAYYAKI KAMAR HAKA*👌🏻
Hajiyata shin menene matsalanki, pimples ne?
Spot? sunburn,acne, stretch marks, knuckle, wrinkles, Black head,ko kinshafa Maine yabatamiki jiki
Inamai shaidamiki cewa ynx ne lokacin dayakamata kiyake dukkan wadannan kema kidinga fita sakayau abunki baruwanki da kunshe fuska ko kice sekinyi makeup hjy fita zar abunki kinuna ainihin natural beauty dinki😍domin kayanmu gbdynsu organic ne babuna bleaching zssu sa ki haskaka fatarki tayi ta kyalli kamar madubi ze fiddomiki d ainihin natural beauty dinki ne😘kunaji barin fadamuku wani Abu billah wannan prdcts damuke dashi ynx Koda kudinki seda rabanki domin duk sunzarce nabaya ankaramasu abubuwa dayawa masu matukar anfani agyaran fata🤗Ina Wanda basasan shafa Mai koda sabulun kawai kike anfani dashi inamai tabbatar Miki zkg ynd jikinki zekoma luwai luwai😘
Soap:3k
Beauty kit:12k
Chat:08062991549
Advertisements
07066210195
Call :07046881166
08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg’s skincare
amare inakara shaidamuku duk wacce tayi anfani d kayanmu Bata bukatar gyaranjiki sedai ra’ayi🥰
Masoya kunanan kauna yanda nakwashe aljihu domin nafarantamuku kuyi achieving goal dinku pls Nima kunanan kauna kufarantamin😪🤠aljihuna yafarfado hilis karnakoma kauyenmu🥲
Yar shawarmannan duk nasaba😤 hilis kugarzayo arabani da kaya🤝
Nd guest what🤩
Duk Wanda yy siya 10k zuwa sama zesamu Karin gift😃
Pamper your skin🧖♀️
Shine like a bride👰🏻
Glow🧚🏻♀️
______________________
*_Chapter Forty Nine_*
………..Kamar almara Hibbah ta koma normal, dan cikin ikon ALLAH ma yau da ta kasance ana gobe tarewar tata idan ka ganta bazaka taɓa ɗaukar ta jigata jiya ba. Baƙi sun fara isowa daga ɓangaren dangin Hajiya mama da mai jiyyarta ta sanar dasu ta waya bisa Umarnin hajiya maman ba tare da sanin Ummi ba. Sai abokan arziƙin Ummin na nan cikin gari dake zuwa dan shirin abincin gobe idan ALLAH ya kaimu ɗin, tunda tace biki zatai sosai akan tarewar autar ta. Sannan kuma itace uwar ango ma ta wani fanin dan Isma’il ya cancanci hallaci daga garesu bayan na bashi Hibbah kuma.
_______________
Su Habib ma da suka dage da shiri daga can ɓangarensu sun ƙagara gobe idan ALLAH ya kaimu tayi Aunty Queen ɗinsu ta dawo gatesu, dan sunyi matuƙar kewarta duk da suna gaisawa da ita su ta wayar Ammar da Master ya basu number. Sun ma zo sun ganta sau biyu bada sanin Master ɗin ba duk da dai Ammar ya gumtsa masa batun zuwan nasu. Dan lokacin shi bayanan ma saboda ƴan tafiye-tafiye da yayi a ɗan tsakanin nan akan wasu ayyukan dayake son kalmashe bakinsu dan hutu yake son ɗauka dogo dazai raɓashe ya ƙwalle da amaryarsa.
*_RANA BATA ƘARYA……_*
Tabbas rana bata karya sai dai uwar ɗiya taji kunya. Dan kuwa a yau aka tashi da gagarumin bikin ƙarin girma daga headquarter na ƴan sanda bisa ƙoƙarin mai gayya mai aiki I.G da wasu manya-manya da suka bada gagaurumar gudunmawa domin girmamawa ƙoƙarin su Master ɗin akan zaƙulo su Dr Sufi dake gidan yari sunacin azabar rayuwa data cututtukan da suka taso musu bisa ƙazantar homo da suka aikata. Dan takai ko a cikin prison ɗin yanzu ba’ako buƙatar son zama kusa dasu saboda shegen warin da sukeyi. master kam shi ba’a ma batunsa. Dan wani irin ƙuraje ke fito masa a jiki na allurar poison ɗin da Master yay masa. Hakama Abba Halilu yana nan yanacin azabar ƙafa da alamun ruɓewarta duk ya bayyana gareshi.
Wani irin gyara da ado na musamman akaima harabar headquarter ɗin tun a yammacin jiya. Zuwa yau kuwa aka ƙarasa ƙawata ko ina har an fara tarbar manyan baƙi tun kusan ƙarfe bakwai na safe.
Dan ta ko’ina duk wani mai ruwa da tsaki akan wannan taro yana can yana ƙoƙarin shiryawane domin isowa akan lokaci. Musamman ma amarya mai tariya biyu Hajiya mandiya Muhhibat Aliyu Hamza Gwarzo mai zamani😂😜. Dan wata irin tsadddiyar riga mai azabar ƙyau kalar sararin samaniya su Habib suka aika mata da ita tare da duk wani abinda zai cika adon nata da ƙawatashi. Sai kayan kuma da zatai amfani dasu a wajen ƙwarya-ƙwaryan walimar da suka shirya nacin abinci daga bakwai na dare zuwa goma. Da farko Master da suka sanar masa ya tirje sai da Abdull yasa baki da ƙyar ya taushesa ya amince. Dan koba komai yana son ganin farin cikin ƴan kannen nasa kuma ta wani fanin. Itama mai gayya mai aikin yasan zataso hakan kodan ya goge laifinsa na nanata zancen satota da bata gajiya dayi idan tsiwar ta tashi, tare da ɓoyema ganinta da yayi tamkar almara.
Cikin ƙanƙanin lokaci mai kwalliya ta tsantsarama Hibbah da zuciyarta ke cike da ɗoki da kewar son ganin mijinta. Sai dai tanata ƙoƙarin dannewa a zahiri. Ana gab da kammalawa Ammar ya shigo yake sanar musu suyi sauri harsu Master sun iso za’a wuce. Babu ɓata lokaci mai kwalliyar ta kammala mata komai ta fito tsaf tamkar wata ƴar daren sha biyar. Ga ƙibar da tayi ta ƙara ƙawata tsarin shigar tata masha ALLAH.
Ummi kanta da su Zahidah kasa haƙuri sukayi sai da suka tanka wannan ƙyawu da Hibbah tai. Su Yaya Muhammad dake jin wani ɗunbin farin ciki suka zagayeta suna zuba mata ruwan hotuna.
A haka suka fito da Hibbah harabar gidan inda su Master ya ke tsumayen fitowar ta su. Akan su Habib da ke zagaye da shi cikin shiga iri ɗaya tamkar wasu bodyguard ta fara sauke ido. Taja gajeren numfashi da satar kallon mai gayya mai aiki dake sanye cikin wasu Haɗaɗɗun suit sky blue kalar kayan jikinta. Shi kansa tun fitowar tasu yay mutuwar tsaye yana jan wani hargitsatstsen numfashi da ajiyar zuciya har su Habib na iya jinsa.
Kunyar Ummi data Yaya Muhammad ta hanashi xuwa ya tareta ya rungume ko zaiji nutsuwar abinda yakeji na ratsa ɓargonsa zuwa cikin jini. Maimakon ya nufi Hibbah sai ya matso kusa da Ummi cikin girmamawa ya gaisheta. Ummi ta amsa cike da fara’a tana sanya masa albarka shi da su Habib da suka ƙaraso suma suna gaida Ummin.
Ya gaisa dasu Yaya Muhammad ma sama-sama kowa ya shiga mota dan jiransu akeyi. Duk da tsokanar da su Habib kema Hibbah bata iya cewa komai ba dan gaba ɗaya idanun Master sun hanata sukuni. Duk yanda yaso daurewa ya kasa. Suna shiga motar da Habib ya kawosa a ciki ya jawota jikinsa ya rungume. A tare suka saki ajiyar zuciya suna sake ƙanƙame juna har yana mamakinta. Habib dai yi yai tamkar bai gansuba yaja motar suka fice a jere da sauran nasu Yaya Muhammad.
A cikin kunnenta ya raɗa mata “I miss you so much Baby luv”.
Hibbah da ɗunbin kewarsa da kunya ke zagaye da ita ta sake cusa kanta jikinsa tana mai shaƙar ƙamshin turarensa da yay mata matuƙar daɗi. Itama a hankali tace, “Ni dai bana kewarka”.
Sassanyan murmushi ya saku da ɗago fuskarta ya sumbaci goshinta. Kasancewar Habib a wajen ya sashi daurewa bai tsotse janbakin ba. Bai kuma sake magana ba har suka isa wajen taron daya gama cika fam da nutane.
Tarba ta musamman ta mutunci suka samu. tare da wajen zama da aka tanada dominsu. Ba’a wani ɓata lokaciba wajen fara gudanar da taron daya tara manya-manyan mutane. Inda aka gabatar da abubuwa masu yawa tare da kyaututtuka ga su Master. Aka kuma tayasa murnar aure da kowa ke ɗauka yanzune yayisa. Daga haka akaci akasha taro ya tashi lafiya.
A yanzu kam dole Hibbah tabi su Ummi suka koma gida tare dan ƙarasa shirin miƙata gidanta nan da anjima. Dan acan ɗinma sun baro baƙi sosai dan ma su Mama Jiddah nan dasu Ummansu Zahidah.
Kamar da wasa sai gashi anyi wani ɗan ƙwarya-ƙwaryan biki a gidan su Hibbahn, anci ansha an rakwashe an ƙwalle musamman su Habib da suka jone da Ammar sukasha shaftarsu. Zuwa takwas na dare kuma aka haɗu a babban hall ɗin da aka tanada domin gudanar da liyafar cin abinci. Anan ɗin ma ba ƙaramin zauta Master gayun na Hibbah yayi ba. Dan gaba ɗaya ta wani canja masa tamkar ba ita ba. Itama kanta gayun nasa ya matuƙar ɗaukar hankalinta danko sanye yake da shadda ƴar ubansu dataji ɗinkin zamani mai ɗaukar hankali. Anci ansha su Habib sun cashe a filin rawa sai kace wasu ƴan daudu😂. Tun Master na hararsu harya shiga sahun masu dariya duk da ƙoƙarin dannewa da yay tayi. Ƙarfe goma dai-dai taro ya tashi, daga nan kuma aka ɗunguma rakkiyar amarya sabon gidansu inda Master ya ɓoye su Ummi. Zuwa yanzu an gama komai gida ya haɗu matuƙa kai kace wani ƙaramin estate ne. Dansu Musbahu kowa da sashensa matan aure kawai suke jira. Mutane basu wani zauna ba kowa ya kama gabansa akabar amarya da angonta dasu Khalid da suma gajiya ta sakasu kwanciyar wuri a sashin baƙi da suke zaune yanzu kafin matayen nasu su shigo kowa ya koma nasa sashen.
Master da dama yana gidan abinsa dan tare suka taho da ƴan rakkiyar amarya suna tafiya ya nufi ɗakin Hibbah da kayan tsarabar da aka tanadar mata dan yaga bataci komai ba a wajen liyafar.
Tana zaune a tsakkiyar gadon tana kwasar kuka kai kace yau ɗin aka fara kawota gareshi. Kayan hannunsa ya ajiye ya nufi gadon yana murmushi, cikin neman tsokana ya ɗaga mayafin yana faɗin, “Haba Hajjaju keda kika dawo wajen mijinki minene na kukan?”.
Hannu tasa ta ture nasa tana ƙoƙarin juya masa baya ya riƙota yana sakin wata siririyar dariya data nema narkar da Hibbah, dan a cikin kunnenta yakeyi. Ƙoƙarin haɗe bakinsu yakeyi tana ture masa kai cikin bore hardai ya samu nasara. Salon da yake mata da kuma halin da take a ciki yasata miƙa wuya har tana maida murtani. Sai da ya tabbatar ya sakata yin laushi sannan ya barta yana sauke ajiyar zuciya. Kunya ta sata saurin sauka a gadon ta nufi toilet dan fitsari takeji.
Ta kammala tana ƙoƙarin fitowa sukaci karo da shi zai shiga shi kuma. Hanunta ya kama yana binta da wani kallo ƙasa-ƙasa daya sata kauda kanta daga kallon nasa. “Muje muyi alwala”. Ya faɗa acan ƙasan maƙoshi tamkar mai gudin ajisu. Ba yanda ta iya dole ta bisa suka koma. koda suka yo alwalar suka fito tare suka gabatar da salla. Yaja musu addu’oi masu tsayi na zaman lafiya da haƙuri da juna Hibbah na amsa masa da amin. Bayan sun kammala duk yanda taso zillewa bai bartaba sai da ya sakata cin abinda ya shigo dashi. Gasasun ƴan shila ne da yogurt dayay mata matuƙar daɗi har tana masa cin zalama da ya bama Master mamaki. Sai dai baice komaiba ya sata yo brush da barin mata ɗakin dan tai shirin barci.
Har taji daɗi ya fita sai gashi ya dawo tana ƙoƙarin kwanciya. Badan taso hakanba ta kwanta kamar yanda shima kai tsaye gadon ya hawo yay kwanciyarsa hankali kwance.
Wata irin soyayya ce mai tsayawa a rai da zuciya da Hibbah bazata taɓa mantawa da ita a rayuwartaba Master ya nuna mata a wannan dare. Sai dai ta jigatu matuƙa dan har saida taita masa kuka da magiya amma bai sauraraba sai da ya more kwanakin kewarta tsaf. Tun a daren suka gyara jikinsu suka koma barci, da Asuba suna idar da salla bai sarara ba sai da ya ƙara dan gaba ɗaya ta dagula masa lissafin kansa, saboda gyaran da tasha bana wasa bane ba. Ga ƙaramin ciki a jikinta wanda shi baisan dashi ba yaketa faman bidiri da bireɗensa.
Yasha taɓara da shagwaɓa dan daƙyar ya lallaɓata suka dawo falo kusan sha ɗaya na safe dan ta samu ta karya. Sun sami ƙayataccen breakfast daga baba saude dasu Habib, tsananin yunwar da Hibbah keji yasata zaman dirshan ta dira kan abincin nan babu sauƙi. Tana gab da gamawa ta buɗe kular ƙarshe da nufin duba abinda ke ciki dan Master yace natane shi bayacin sa. Wani irin dukan kanta ƙamshin farfesun kifin yayi. Cikin zabura ta saki murfin kular tai baya har abin na bama Master tsoro.
Kanta ta dafe dake juya mata tana masa nuni da hannu akan ya rufe amma bai ganeba. Babu shiri ta saki aman dake taso mata dan ƙamshin kifin sake hauro mata kai yakeyi.
Da hanzari Master ya miƙe kanta ya riƙota. Ganin aman daya tsaya yake sake taso mata dole ya kwasheta da sauri suka nufi hanyar bedroom. A toilet ya direta yana riƙe da ita harya lafa. Ya gyara mata jikin yana jera mata sannu cikin damuwa da tambayarta dama bata da lafiya ne.?
Kanta ta girgiza masa a galabaice ga hawaye shaɓe-shaɓe ta sanar masa batason ƙamshin kifi ne. Mamaki ya kamashi dan yasan dai tana cin kifi ai, akwai lokacin da ya taɓa jin su Habib na sanar mata shi baya cin kifi tace saiko ta sakashi yaci wataran saboda ita kifi tamafi sonsa akan nama.
Saboda laushin da jikinta yayine ya sashi neman number Abdull domin zuwa ya dubata. Babu bata lokaci kuwa Abdull ya iso, sai lokacinne ma su Habib kejin Aunty Queen babu lafiya. Gaba daya suka ɗunguma sashen domin dubata.
Tun a kallo guda da Abdull yay mata ya fahimci cikine da ita. Amma sai ya bata tsinken gwajin ciki yace su gwada ya gani yanzun. Ana kuwa gwadawa da tsinken ciki ya nuna kansa. Wayyo farin ciki ga waɗan nan ahali ai bama acewa komai. Master kam jin abun yayi tamkar wata almara ko tatsuniya. Ya tsare Hibbah da idanunsa dake canja launi suna tara hawaye. Abdull dake kallonsa ya rungumesa yana mai tayasa murna. Hakama su Habib gaba ɗayansu suka ruƙunkumesa suna ihun murnar zasuyi ɗa.
Hibbah dai baka gane farin ciki ko akasin hakan tattare da ita. Dan tunda taji ihunsu Salis na hawa mata kai ta rarrafa ta koma ɗaki ta kwanta. Acan Master ya sameta. Ya ƙanƙameta hawayen da yake riƙewa na ziraro masa. Yana hawaye yana murmushi da kissing Hibbah tako ina. Yama rasa ta ina zai bayyana farin cikinsa a rayuwa. Godiya yaketa faman jerama UBANGIJI da kirari a zuciyarsa.
A gaba ɗaya yinin yau waɗan nan ahali sun yisane cikin wani irin farin ciki mara misali da kwatance. Duk da zuwa azhar Hibbahn ma ta martaye garau tamkar ba itaba. Sai dai ta samu tumatur ɗinta mai yawa tasha dan yanzu bata da abu mafi soyuwa sama da shi.
Duk da garau ɗin data koma dukan motsinta a idanun Master ne. Kaɗan-kaɗan saiya tambayeta mike mata ciwo? Mitake son ci?. Tun tana cemasa babu komai harta koma tura masa baki irin ya dameta ɗin nan. Ko kaɗan baijin haushi, sai ma murmushi da yakeyi kawai.
_________________________
Sam Hibbah bata wani laulayi, kifi kuwa tun daga ranar ko su Habib daina cinsa sukai a gidan. Sai wata tsadaddiyar soyayya Master ke nuna mata suna gurzar amarcinsu yanda ya kamata dan cikin nan ba ƙaramin saka masa kwaɗayinta yake ba. Gashi abin ya haɗa da zaman hutu da yakeyi a gidan harna tsahon watanni uku da aka bashi. Tun kwananta uku da dawowa gidan ita ke girkinta da Master, wani lokacin kuma taje sashen su Baba Saude suyi gaba ɗaya, musamman idan Abdull na gidan. Shafta tsakaninta dasu Habib sai abinda yay gaba. Dan ma an sama musu aiki zuwa yanzu ba zaman gidan sukeba sosai sai idan Master na bukatarsu akan wani aikin.
Komai na Hibbah ya sake canjawa. Ta buɗe ko ina ya cika a jikinta ga ƙiba cikin yana sakata masha ALLAH. Cikinta na watanni huɗu ta fara wani matsanancin laulayi da batayisa a baya ba. Ga shi Master ya koma aiki kuma. Dole Baba Saude ta dawo yini sashen nasu ko yana fita Hibbah ta koma can har sai ya dawo. Dan zuwa yanzu komai bata iyayi sai kwanciya. Ƙarin ruwa kuwa duk bayan kwana biyu sai an mata shi ake samun nutsuwa. Sau biyu Ummi dasu Zahidah na zuwa dubata. Su Yaya Muhammad kam ai basusan adadi ba. Balle Ammar yaji labari wanda kullum babu fashi idan ya dawo school sai ya biyo tanan ya ganta yake iya wucewa gida.
A cikin wannan tsukun da Hibbah ke dirzar nata laulayin aka saka aurarrakin su Habib da ƴammatansu. Zai kama dai-dai da haihuwar Hibbah insha ALLAH. Bayan saka ranar da kusan sati biyu wani aiki ya tasoma Master zuwa kudancin ƙasar. Dole ya tattara matarsa suka wuce tare dan bazai iya barinta a halin da take ciki ba. Ta tafi da kewar su Musbahu, suma ta barsu da kewarta. Dan hatta Ummi taso Master yabar Hibban anan amma dan karta shigar masa rayuwa tai shiru ta bisu da addu’a.
Sai kuma tahowar ta saka Hibbah cikin ɗunbin farin ciki dajin daɗi. Dan kai tsaye wajen shakatawa na musamman a bakin ruwa Master ya samar musu masauki. Kasancewar aikin nasa kuma na sirrine ya sai ya koma a real Isma’ill ɗinsa suka sake baje shafukan soyayya da rainon cikinsu da Master ke matuƙar so da ƙauna da fatan fitowarsa duniya lafiya. Ɗan yawon da yake da ita wajaje daban-daban yasata fara samun ƙarfin jikinta, sai dai randa laulayin ya bugar da ita kuma dole ne su kasance a gida. Akwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI sai gasu da wattani uku da tahowa har sun shiga na Huɗu.
Taso komawa gida a watan daya gabata dan a farkonsa su Zahidah duk suka haihu kusa da kusa. Sai dai aikin Master dake gab da kammaluwa ya sashi hanata zuwan sai a waya akaita tura mata hoton babys masha ALLAH. Ranar sunayen ne dai da aka haɗe ta birkice masa da kuka harda su zazzaɓi. Sai da ya haɗa da Ummi dasu Yaya Muhammad a masu lallashi sannan ta haƙura. Ammar kuwa ya dage yayta ɗauka mata videon komai yana tura mata. Dan mutane ne sosai suka halarci taron musamman dangin Hajiya mama da ƴan ƙauyen su Ummi. Ita Ummi ma har mamaki da al’ajab abin ya bata. Amma saita ɗau hakan matsayin wani hikima da rahama na UBANGIJI.
Washe garin suna akai zama na musamman da su kawu ballo game da gida da kayan gadon su Yaya Muhammad ɗin da Halilu yaso handamewa. Duk da dama an raba musu tun lokacin da babansu ya bar duniya sai yanzu aka sake raba abinda ya rage musamman gidan da suka taso dan ance su Momy su tashi. Kuka momy ta dingayi tana neman alfarmar Ummi akan a barsu su zauna Hajiya mama dake kwance tace bata yarda ba. Su Ameera su fitar da miji su Yaya Muhammad su aurar dasu. Ita kuma Momy ta koma can gidan da Mahaifin su Hibbah ya bama Halilu tunkan ya rasu ta cigaba da jiyyar Junaid.
Dole kuwa haka akayi, dan su Ameera da suka fahimci tsohuwar son tona musu asiri take babu shiri suka kawo ƴan samarinsu da abaya suka raina. Gudun kar wata matsalar ta biyo baya su Yaya Muhammad suka saka bikin a kurkusa. Dan sati uku kacal suka saka. Komai kuma daya shafi kayan ɗaki basuyi ƙyashin yimusu shi ba.
________________
A satin dasu Hibbah suka dawo a satin aka ɗaura auren su Ameera. Haka taci biki a wahale ta ƙaton ciki Ammar na mata iya shege. Daya kalleta saiya kwashe da dariya. Video kuwa da hotuna yayisu kala-kala. Tun tana kulashi harta daina dan yay bala’in taso rayuwarta gaba shi dasu Habib da ayanzu suka ɗinke abokai shaƙiƙai.
Bikin dai ba wani armashi yayi ba sosai. Dansu Yaya Muhammad ɗin ma sunfi maida hankali a shirye-shiryen nasu Habib da za’ai satin sama. Wanda Ummi ce matsayin uwar anguma I.G uban anguna. Hatta lefe su Yaya Abubakar haɗa hannu sukai da Master aka haɗa komai na birgewa da nunawa tsara. Ana miƙa amare su Ameera ɗakunansu kowa ya maida hankalinsa akan nasu Habib. Dan Hibbah ma dole ta koma gida dan Master yaƙi yarda akan zata zauna anan har satin bikin. Shi fatansa ma ta haihu lafiya kafin a shiga ruguntsumin taron………….✍
GIPHY App Key not set. Please check settings