Advertisement
*_Chapter Fifty (End)_*
…………ALLAH kuwa ya amsa addu’ar tasa. Dan a daren data koma gida kusan ƙarfe uku ta farka da matsananciyar naƙuda da dama kusan sati kenan tanata cinta a tsaye tadaiyi shiru ne kawai dan karya hanata halartar bikin su Amira. A rikice ya miƙe ya kira baba Saude. Wadda tana zuwa ta fahimci haihuwarma ta taho.
Duk yanda yaso su tafi asibiti hakan bai yuwuba. Dan kuwa dai abin yazo inji mai tsoron wanka. Ansha fama da gwagwagwa kafin ALLAH ya sauki autar Ummi lafiya gab da kiran sallar asubahi. Ta santalo ɗanta namiji mai kama da Ubansa sak. Lokaci da Master ya ɗauki yaron sai ga hawaye na rige-rigen sakkowa kan fuskarsa dan hakan ya tuna masa da randa Mamynsa ta haifi Habib. Ya rungume yaron wata irin ƙaunarsa na rsatsa jini da ɓargonsa. Sai da aka kammala gyara Hibbah tsaf bayan sallar asuba sannan ya shiga ya ganta. Su Habib ma sai lokacin suka sani.
Wayyo zo kaga murna da ihu. Yaro kuwa gaba ɗaya suka hau rububin ɗaukarsa Hibbah na kallonsu tana dariya da hawaye ita da Master, dan Alhmdllhi batajin wani damuwa a jikinta. Amma duk da haka sai da suka fita asibiti taga likita. Kasancewar babu wata damuwa suka dawo gida da wuri. Inda suka iske matan su Yaya Muhammad dasu Ameera amare cike da gidan. Dan tuni su Idris sun baza batun haihuwar. Hotunan yaro kuwa nata yawo a wayoyin ƴan uwa da abokan arziƙi.
Master yama yaro huɗuba da *ALIYU HAYDAR, ZAKI GADANGA ƘUSANR YAƘI*. Sosai Hibbah taji daɗi, duk da dai tasan shima sunan mahaifinsa kenan. Ammar kuwa ai cayay shi akaima takwara babu wasu su daddy.
Tsaye Baba Saude take akan Hibbah hakan yasa Ummi sam bata damu da batun a maidota gida ba tunda biki zasu shiga. Kwana biyu da haihuwa aka dire tarin kayan barka daga su Yaya Abubakar na ban mamaki. Dan har sai da Master yace sunyi yawa ai. Amma suka nuna masa zama su ƙaro kuwa.
Advertisements
Dole ya tsuke bakinsa yay godiya hakama Hibbah.
★★★
Duk da ɗanyen jego dake a jikin Hibbah haka aka tsunduma hidimar biki, sai dai ita kam babu damar yawan shigi da fici. idan kuwa ta kama dole zaka ganta cikin dogon Hijjab kamar yanda Baba Saude ta tilasta mata sakawa.
Randa take cika kwanaki shida da haihuwa aka ɗaura gagarumin auren ƙannen Master guda bakwai a babban masallacin juma. Taron aure ne daya samu halartar mutane manya dama jama’ar gari talakawa irinmu yaku bayi. Dan kuwa kowa burinsa nuna halacci ga Master. Zo kaga bakunan anguna uwa gonakin auduga. Sunyi shar dasu abin sha’awa da birgewa.
Washe gari aka haɗa bikin suna da karasun biki, inda kowa ke nuna bajintarsa. Amaryar jego Hibbah tayi ƙyau harta gaji ita da jariri Hydhar, wanda gaba ɗaya kamaninsa ke rikiɗewa zuwa Habib abin zam-mamaki.
Iya jigatuwa kowa ya jigatu, anci ansha ankuma raƙashe an ƙwalle yanda ya kamata. Dan kuwa Ammar ma dai yace shimafa auren nan yakeso nanda wata guda kacal, dan maganar gaskiya bazai bari su Habib su ajiye ƴan dugwi-dugwi ba shi yana sake da baki ga Hibbah da ɗa.
Zuwa dare aka kawo amare ɗakunansu, kowa ya kama gabansa akabar su Hibbah da sauran aiki.
____________________
Advertisements
Kamar yanda Ammar ya ambata shima kam ALLAH ya amsa masa. Dan bayan bikin su Khalid da wata guda cif aka ɗaura nasa auren da amaryarsa. Hibbah kuwa ta samu nayi. ta tasashi gaba da sheri kala-kala ta rama duk bashin da yaci akanta tsaf.
Bayan bikin Ammar da kwanaki tara suka wuce Umrah ita da Master ɗinta da Hydhar. Dan Master yace yana buƙatar hutu kasancewar tayi arba’in. Sai da suka fara zuwa ƙasar dubai suka more rayuwarsu na tsahon sati biyu kafin suka wuce saudia domin gabatar da umrah. Daga saudia Canada suka nufa wajen Abdull dake shirin tattaro iyalansa ya dawo gida shima.
Zokaga murna wajen ƴaƴan Abdull din da matarsa duk da kuwa a waya suka san juna da Hibbah. Hydhar kam ya zama ɗan gata dan koyaushe yana nane da yaran. Da wannan damar su Hibbah da Oganta Master suka sake ɓarje guminsu da gajiya a ƙasar canada.
satinsu biyu cif a canada suka ruguntsumo da iyalan Abdull suka dawo gida. Inda suka iske rasuwar hajiya mama.
*_AKWANA A TASHI_*
_A KWANA_ a tashi babu wahala wajen UBANGIJI, dan kuwa cikin ƙanƙanin lokaci rana ta zama dare, dare ya zama kwana, kwanaki sun koma sati, sati sun zama wata. Watanni sun rikiɗe shekara. Kafin cikar wasu buruka shekaru sunta ninkuwa a cikin rayuwar su Hibbah.
Alhmdllhi zuwa yanzu yaranta uku, hakama su Yaya Muhammad yara uku-uku suke da, dan haihuwar ta cigaba da tafiya musu ne kamar yanda suka fara. Family ya haɗu cif ga Ummi abin birgewa. Hakama ga Master burinsa ya cika. Dan suma su Habib yaransu bibbiyu yanzu suda Ammar. Family biyu sun dunƙule waje guda sun koma zuri’a ɗaya.
Yau data kasance Friday sauri-sauri Hibbah ke ƙoƙarin kammala ayyukan gidan kafin sojojin gidan su dawo makaranta. Dan Hydhar da yaransu Habib na farko duk an sakasu, sai ɗiyarta ta biyu mai sunan Mamyn su Master suna kiranta mimi. sai na ƙarshen da shima rarrafe yake ko ina mai sunan Master ɗin. Wato Isma’il, suna kiransa Ansar.
Kasancewar duk juma’a a tare suke haɗuwa da matan su Zaidu suyi girki mai yawa da ake fita da shi sadaka shiyyasa komai bataiba a sashen nata daya danganci abinci. Sai ɗan fruit salad data shiryama Master da fura damammiya da taji kayan haɗi.
Cikin ƙanƙanin lokaci ta saka ƙamshi ta faɗa wanka, dan Ansar na wajen Sharifat data zama budurwa. Dan ayanzu hakama a wajenta take ta bar hannun baba saude dake fama da ƙafa zuwa na tsufa. Rigimar da yaketa tsilala mata ce tasa Sharifat ɗaukarsa suka tafi can compound inda matan su Adam ke girki. Dan dama ba barinta sukeyi tayi ba ita, sai dai ta duba abinda baiyiba.
Suna tsananin bata girma kamar yanda suka samu mazajensu na mata itada Masternsu. Ita kuma ta tsare mutuncinta bata bada wata ƙofar da raini zai shiga tsakaninta da wani a cikinsu ba. Yaransu duk ta haɗe da nata tana kulawa da basu tarbiyya kamar yanda suma sukeyi. Koyaya taga saɓanin zai shiga tsakaninsu zatai iya ƙoƙarin ta taga ta gyara komai cikin hikima…….
Da sauri ta buɗe idanunta saboda jin an buɗe ƙofar toilet ɗin. Ta sharce ruwan dake sauka mata a fuska tana kallonsa dan dama tasan sai shi ɗin. Harara ya sakar mata yana kwance towel ɗin jikinsa ya shigo wajen wankan da dungure mata kanta. “Yarinya kinsan dai kin saɓa doka ko? To wankanki baiyiba sai kin koma farko”.
Fuska ta ɗan ɓata da turo hanunsa dake ƙoƙarin ɗora mata soson daya haɗama kumfa. “Ban yarda da wayon nan naka ba Daddyn Hydhar. Ai yanzu muka gama waya amma baka sanarmin kana hanyar shigowa gida ba”.
“Kinma isa”. Ya faɗa da dungure mata kai ya turata jikinsa yana goga mata sosan. Son ƙwace jikinta ta cigaba dayi amma ya hana. Daga haka suka koma kokawarsu ta masoya suna dariya. Har dai takai an koma asalin soyayyar datafi ta kokawar wanka. Cikin nishaɗi da farin ciki suka kammala wankan nasu dana abinda ya biyo baya suka fito yana tsokanarta da fitinanniya.
Dariya tayi da yarfa masa ruwan hanunta. Cikin ɗaga gira tace, “Kai kuma Master na fitinannun miye sunanka?”.
“Zona faɗa miki”
Da sauri ta zille ganin zai damƙota. “ALLAH zaka makara salla ga sojojinka can kuma da alama sun dawo suma”.
Master dake ƙarasawa gaban Mirror yana goge jikinsa fuskarsa ɗauke da murmushi yace, “Aini na ɗakkosu a school. Dan yau ma tare dasu zanje massallaci. Na bar yarda su Habib namin wayo”.
Ƙarasowa Hibbah tai garesa ta rungumosa ta baya da kwantar da kanta a gadon bayansa tana murmushi. “Ina bayanka big daddy. Dan kuwa dama kullun mitar yaran nan big Daddy bai zuwa dasu massallacin juma’a ne.”
Hanunta ya kamo ya zagayo da ita ya jingina da mirror ɗin. Yaɗan lakace hancinta da sumbatar lips ɗinta. “Insha ALLAH zan gyara baby luv. Koda kinga ran juma’a ban dawo akan lokaci ba, kiyi azamar kirana ki tunamin alƙawarin sojojina”.
Rungumesa tai tana murmushi da sumbatar ƙirjinsa. Shima ya rungumetan ransa fes da tarin so da ƙaunarta.
Da taimakonta ya shirya cikin ɗanyar shadda fara ƙal harda murza hula. Itama ta kimtsa sauri-sauri suka fito tare suna baza ƙamshi. A falo suka iske su Hydhar daketa faman hayaniya har an gama shiryasu cikin nasu shaddojin farare tas irin ɗaya mazansu da matansu. Da gudu sukayo kan Hibbah duk suka rungumeta suna faɗin “Big Mommy Oyoyo”.
Durƙushewa tai itama cikinsu tana mai rungumesu da faɗin “Oyoyo sojojin big daddy Ya school?”.
Atare suka amsa mata da Alhmdllh. Ta miƙa hannu ta kamo Mimi dake gefe tana tunzura baki fuskarta duk hawaye. “Kai! Kai waye ya jangwalo min uwa a gidan nan ne?”.
Duk juyawa sukai suna kallon mimin har Master dake amsa waya. Mimi ta sake taɓe baki tana nuna Sudies. “Yaya Sudies ne ya cimin cake ɗina a wajen Ammi”.
Katse wayar Master yayi, ya zirata aljihu yana matsawa inda Mimin take. Cak ya ɗauketa tare da sumbatar kumatunta. “Mamyna shine shagwaɓa kuma bai tashi ba sai yanzun?. Maybe rowanki kikai masa shiyyasa ya ɗiba ai.”
“Big daddy ƙaryane, nima ta shamin juice ne shiyyasa na mincini cake ɗinta”.
Cewar Sudies yana matsowa kusa da Master. Dire Mimi yayi kusa da Sudies ɗin ya ɗan duƙo gabansu ya kama hanunsu ya haɗe waje guda. “To tunda kowa yama kowa a shirya. A yafema juna kuma”.
Kallon juna Mimi da Sudies sukayi, Sudies yasa hannu ya sharema Mimi hawayenta. “Sorry sweet heart bazan sake ba ki yafemin”.
Mimi dake murmushinta mai kama dana Hibbah tace, “Nima sorry yaya Sudies ka yafemin”. Sai suka rungume juna. Tafi su Hydhar suka farayi musu kamar yanda aka koyar dasu. Master dake murmushi ya sumbaci kumatunsu ɗaya bayan ɗaya yana sanya musu albarka.
Hibbah dake dariyar wannan hali na Mimi da gaba ɗaya ita ta biyo tace, “Mamana to azo amin oyoyo ɗin idan an huce”. Da gudu Mimi tazo ta faɗa jikinta.
Master yay dariya da faɗin “Like mother like daughter”.
Su Habib dake tsaye suma duk suna kallonsu dariyar suke musu. Suka ƙaraso cikin falon Khalid ɗauke da Ansar daya amso hanun Sharifat. Yana ganin Master ya fara miƙa masa hannu. Amsarsa yay yana faɗin, “Oh my sweet Darling ina ka shigane ban gankaba”. Ya sumbashi kumatun yaron mai tsanain kamanni da shi da kullum ake gaddama a gidan akan waya biyo?. Hibbah da Habib dai sai dai suyi dariya kawai dan sunsan Master ne tamkar yayi kaki ya ajiye.
★
Ganin zasu makara salla suka fice. Aka bar Ansar na kwasar kuka shi sai ya bisu. Lallashinsa Hibbah ta dingayi daga ƙatshe ta goyasa dai.
Ana idar da salla basu jimaba a massallaci suka dawo, can cikin garden aka kai tabarmi aka baje tamkar yanda suka saba. Cikin ado da gayu suma matan su Musbahu duk suka iso garden ɗin, cikin girmamawa suke gaida babban yaya Master. Shiko yana amsa musu da kulawa tamkar yanda ya saba. Gaba ɗayansu har baba saude suka ci abincinsu hankali kwance zukatansu fes da farin ciki. Bayan sun kammala su Hibbah suka gyara wajen yara kuma suka fara wasansu.
Bayan sallar la’asar kowa yayo shiri cikin kayan ƙwallo su Habib da yaran har Master suka baje a compound suna wasanninsu cike da farin ciki da tsantsar ƙaunar junan da baka isa cewa suɗin ba jini ɗaya baneba. Basu bar wajen ba sai magriba. Sai da sukai har sallar isha’i suka dawo gidan, kowa ya nufi sashensa domin hutawa da iyalansa.
Washe gari gaba ɗayansu suka dunguma gidan Ummi yini. Idan wannan satin sukaje, wani satin sai su Yaya Muhammad da matansu suma da yaransu suzo nan. Lahadi kuma kowa ya ɗauka matarsa su tafi inda yake buƙata. Ko gidansu ko yawon da shi yafi buƙata.✍😭
_Alhamdulillahi_
_To masoya nima dai bara na shaƙata anan dan maganar gaskiya na rubutu. Abinda na faɗa dai-dai ALLAH ka haɗamu a ladan. Wanda nai kuskure ALLAH ya yafe mana baki ɗaya._
*_Littafin TAKUN SAƘA ƙirkirarren labarine bawai gaske ba. Idan kayi karo da abinda kai kake gani a mahangarsa tamkar bazai yuwu ba sai ka ɗaulesa matsayin nishaɗi da marubuci kansa domin ƙawata labarin sa. Abinda yazo domin tunatarwa kuwa sai ka gwada shi ko zaka dace. Wanda ya baka haushi kayi haƙuri haka rayuwa take dama ba komai akeyi dan birgewa ba. Wanda ya baƙanta ranka ma kayi haƙuri rayuwa akwai zaƙi a cikinta akwai ɗaci. Abinda kaso gani baizo a yanda kaso ɗin ba kayi haƙuri ajizancine irin na ɗan adam mai mantuwa da gaggawa._*
_Akoda yaushe ZAFFA BIYAR na godiya a gareku masoya, yanda baku gajiyaba wajen bibiyarmu, muma bazamu gajiyaba wajen yi muku godiya da ƙaunarku akoda yaushe. ALLAH ya barmu tare, alkairinsa yakai gareku aduk inda kuke a faɗin duniya😘😍😘😍😍😍🤙🏻_.
*Na yafema dukkan wanda ya ɓatan rai a wannan rubutu, nima ina neman afuwa da gafarar kowa dan zata iya yuwuwa wannan shine littafi na ƙarshe da _Bilyn Abdull_ zata rubuta a duniya😭🙏🏻. ALLAH ka gafarta mana ka gafartama iyayenmu. ALLAH yasa ranar mutuwarmu ta zama ranar farin ciki a garemu. ALLAH ka zaunar da ƙasarmu lafiya ka azurtamu da shuwagabanni na gari. Ka shiryemu muma talakawan ka gyara mana zukatanmu gurɓatattu*😭😭😭🙏🏻
_Sai mun haɗu a zafafa na gaba idan da rabon hakan_.
*_BILYN ABDULL CE😘🤙🏻_*
_______________________
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI……_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*
*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
GIPHY App Key not set. Please check settings