Lu’u Lu’u 13

Advertisement

*13*

 

A k’ofar babban b’angaren motocin suka tsaya, da sauri suka firfito suka jeru suna jiran fitowarshi inda d’aya a ciki ya bud’e mishi k’ofa, k’afarsa d’aya ya fara zurowa mai sanye da takalmi kalar maroon k’irar turkey amma ba k’afa ciki ba, karasa fita yayi gaba d’aya cikin sauri ya tunkari shiga ciki suka rufa masa baya, saida suka kai daf da falon suka tsaya sai biyu da suka bi shi zuwa ciki, tunkarar matakalar da yayi yasa shi d’aga musu hannu alamar su dakata kafin ya shiga takawa da sassarfa kamar zai yi gudu.

D’aki na biyu a jerin corridor ya k’wank’wasa, bai jira izini ba ya bud’e ya shige dan yasan wacce ke d’akin ba zata iya bashi izinin ba, cak ya tsaya yana kallon sanyin idaniyar tashi, wani annuri ne ya ziyarci fuskarshi sanda ya d’ora idonshi akan kyakyawar fuskar dattijantakarta, a hankali kuma har sanyayyan murmushi ya bayyana a fuskar shi ba tare da sanin shi duk dan shauk’in ganin *mahaifiyarsa*.

Bai yi k’asa a gwiwa ba tunda yasan ba zata iya motsa ko da k’afarta ba yasa shi saurin k’arasawa gareta, saida ya zagaya b’angaren hagunta sannan ya durk’usa kan gwiwarshi d’aya, hannunshi na hagu yasa yana shafa gashin kan ta yana mayar mata da shi baya, tattausan murmushi yake sakar mata hannun dayan shi kuma ya sak’alashi cikin na ta, a sanyaye ya furta “Fy Mam (mahaifiya ta, a yaren Gallois).”

Farin cikin ganin mahaifiyarshi da kuma tsananin tausayin halin da take ciki yasa shi jin wata k’walla na taruwa masa a gefen idon shi, cike da k’arfin halin son kawar da ita yace ” Fy Mam kina lafiya ko?”

Idonta dake rufe ya kalla wanda yasan ba dan bacci take ba da ta amsa masa da ido, k’urawa fuskarta ido yayi cikin muryar jimami da alhini ya sake fad’in “Komai ya kusa zuwa k’arshe fy Mam, na samota dana tafi, kuma zan tabbatar na kawo miki ita har nan, bansan ko nayi kuskure ba, amma dai dole ne sarki Musail ya d’and’ani hukunci, dole ya ji rad’ad’in rashinta yayin da zai hangeta a cikin gidan nan, amma kuma babu yanda zai yi, ko ta zama ajalinsa, ko ta zama silar rugujewar duk wani iko na shi, wannan bai dameni ba, zafi da tashin hankalin da zai shiga na rashinta ma kawai ya isheni.”

Sake damk’ar hannunta yayi tare da sako hawayen daya gagara tsayar da su cikin k’unar zuci yace” Sai na d’aukar miki fansa fy Mam, a dalilinshi ne kike kwance ba kya motsa ko da yatsanki, a sanadiyarshi ne mahaifina ya rasa duk wani farin cikinshi, a sanadin shi ne na rasa d’an uwa na…”

D’ora goshin shi yayi a hannunta yana zubar da hawaye, wannan d’umi hawayen dake sauka hannunta ne ya farkar da ita, saidai ido kawai ta zuba masa tana kallon sumar kan shi, saida ya ci kuka mai isarshi ya d’ago kan shi ya zuba idonshi a fuskarta, suna had’a ido ya saki murmushi yana share k’wallan shi yace “Fy Mam, kin tashi ne?”

Ido kawai ta zuba mishi ba tace k’ala ba, murmushi shi dai kawai yake sakar mata, hannunshi na cikin na ta yana ta mammatsawa, banko k’ofar d’akin da aka yi aka shigo yasa shi d’aga idonshi ya kalli k’ofar, kan farin gemun mahaifinshi ya fara sauke idonshi kafin gaba d’aya farar fuskarsa, wani bayyanannan murmushi ya saki ya mik’e tsaye da hanzari ya tunkareshi, shi ma sarki Wudar da farin cikin ganin gudaliyarsa kuma magajinshi yasa shi bud’e hannayenshi yana fad’in “Fyddai (d’ana).”

Advertisements

Da fara’a shi ma ya rumgumi mahaifin na sa yace “Fy nhd (mahaifina).”

Sosai suka rumgume juna kowa na shak’ar k’amshin junansu, cike da so da k’auna sarki Wudar ya d’an bubbuga bayanshi hakan yasa suka d’ago suka kalli junansu, da farin cikin sake had’uwa da sukayi Wudar yace “Yaro na ya kake?”

Da fara’a ya sunkuyar da kai yace “Ina lafiya mahaifina, kamar yanda kake gani.”

Jinjina kai yayi yace “Ya akayi ka zo baka sanar dani ba? Baka so na san da zuwanka ne?”

Kallon fuskarshi yayi yace “Amma yanzu ya akayi ka sani?”

Da fara’a ya amsa masa da “Abokinka ne ya sanar da ni, Haman.”

D’an girgiza kai yayi tare da k’yabta idonshi alamar sam bai ji dad’i ba, nuna masa mahaifiyarshi yayi yace “Ka ga jikin na ta ko? Har hanzu Umad k’ok’ari nake akan rashin lafiyar mahaifiyarka, izuwa yanzu abun ya daina bani mamaki sai ma tsoro.”

Jinjina kai yyi yace “Mam ta kusa samun lafiya Ba, insha’Allah.”

Da mamaki sarki Wudar ya kalleshi yace “Me ka fad’a a k’arshen?”

Girgiza kai yayi alamar ba komai, sai kuma ya sunkuyar da kai yace “Ka gafarce ni mahaifi na, ni zan je b’angare na.”

Da alamar mamaki a fuskar sarki Wudar ya kalleshi yace “Sosai nake mamakin sababbin halayanka Umad, wai me yake damunka ne?”

Kallon fuskar mahaifin na shi yayi, irin kallon nan na tsaneke kallo na basira, a take kuma ya d’auke idonshi ya mayar k’asa yace “Sarki na, zan sanar da kai komai da zaran mun zauna.”

Advertisements

Bubbuga kafad’arshi yayi ya jinjina kai alamar gamsuwa, cikin nutsuwa yace “Ka huta da kyau, zuwa dare zamuyi tafiya.”

D’an kallonshi yayi da mamaki sai kuma ya sunkuyar da kai yace “To Ba.” Da ido ya masa izini da zai iya tafiya, a ladabce ya rab’ashi ya fita a d’akin, hadiman dake bakin k’ofar ne suka rusuna masa alamar gaisuwa, bai kula da su ba sai wucewa inda zai sadashi da na shi b’angaren.

A kasalance ya k’arasa had’add’en b’angaren shi, cike da gajiyar tafiya ya shige b’alle mab’allansa amma kuma idonshi a lumshe yana tunanin _”Ina take? Shin zai iya samunta a cikin gidan nan kuwa?”_

Ajiyar zuciya ya sauke ya bud’e idonshi tare da jefa rigarshi kan gado ya nufi ban d’akin shi yana tunanin tabbas idan suka zauna zai fad’awa mahaifinshi ya fa jima da canza addininshi.

Tunda ya fita sarki Wudar ma ya k’arasa kusa da uwar d’akinshi, sunkuyawa yayi ya sumbaci goshinta ya kalli fuskarta yace “Ina son ki, anjima zanyi tafiya ki min addu’a, zan je cinikayyar lu’u lu’uta, ba zan dawo gidan nan ba sai da ita.”

Sake sumbatarta yayi sannan ya fita a d’akin cikin rakiyar hadiman shi biyu dake take masa baya.

*Egypt*

Irin yanda ta ga suna d’aukaka lamarinta da kuma yi mata komai daban yasa ta jefawa kan ta tambayar *wacece ita*? Dan yanda ta ga hatta da ruwan wankanta kalarsu daban, wata irin kalar pink mai duhu ga kuma wasu furannin flowers da aka zuba a ciki, uw uba k’amshin da ruwan ke fitarwa, yanda suka tsaya a kan ta bayan ta fito suka dinga shiryata kamar yar tsana, wata doguwar riga kalar ja suka wacce kamar da tattausan leshe aka d’inka ta har jan k’asa take, kamar yanda ta nuna bata so haka suka barta da fuskarta babu kwalliya, saidai farar hodar ruwan da aka shafa mata wacce ta dace da kalar fatarta, jan bakin da suka shafa mata a leb’enta kalar ja, duk da gashinta gajere sosai haka suka shafe mata shk da mayuka suka mishi gyara mai kyau sannan suka d’ora mata kambu mai kalar ruwan zaiba kuma kamar hasken lu’u lu’u, hakan sai yasa ta fito kamar wata sarauniya tayi kyau kamar ba gobe, bandejin kanta kam wani sabo suka nad’a mata kafin su shiga take masa baya su fito.

Ta siririn corridor suka bi da ita, ko da suka kai bakin k’ofar b’angaren na shi suka tsaya, d’aya a cikinsu ce ta bud’e mata k’ofa alamar ta shiga, kallonsu tayi kafin ta tattare rigarta ta shiga takawa a hankali, kamar yar k’auye haka ta shiga k’arewa babban falon kallo, amma abun mamaki duk kyau da had’uwarshi bai kai na falon da waccen garjejen k’aton ya ce falonta ne ba a cewarta fa, tana cikin juyowa ta inda kujerun zama na alfarma kirar Italy suke kawai ta zabura tare da sakin yar k’ara tace “Ahhhhhh!”

Sai kuma tayi shiru ta sake tsura musu ido, da d’an hanzari Bukhatir ya k’araso gareta yana fad’ad’a murmushi yace “Kwantar da hankalinki gimbiya.”

Wani kerere ta shig binshi da kallo tana had’e fuska da kula yatsina ta, k’ofar dake fuskantar ta aka bud’e, Zafreen ce ta shigo ita ma ta shirya sai dai babbanci na nesa ne tsakanin shigar Ayam da ta Zafreen d’in, sauk’akk’an riga ce doguwa kalar fara wacce ta saukar mata har k’asa, gashinta a sake yake da kuma bandeji a kan ta saidai alamu sun nuna ita ma an canza mata wani ne.

A wani gadarance Ayam ta d’auke kai daga kallon Zafreen ta kalli Bukhatir dake gefenta ta dafe k’ugu tace “Malam fad’a min me nake yi a nan? Waye kai kuma me yasa ka kawo ni nan? Sannan wannan kayan bana son su a sama min k’ananu.”

Shi dai da fara’a a fuskarshi ya nuna mata maza da matan dake gefensu duk sun mik’e tsaye yace “Muje ki gaisa da mutanenki tukuna.”

Lumshe ido tayi mai nuni da ka fara kaini bango kafin ta tunkaresu da tafiyar sauri, tana zuwa gabansu ta tsaya tana kare musu kallo, daga bayanta Bukhatir ya nuna mata wani dattijo yace “Gimbiya Zafeera, wannan shi ne sarkin gida, ma’ana duk masu aikin gidan nan a k’ark’ashin saka idonsa suke.”

Cikin girmamawa dattijon ya rusuna yana mata wani yare da ba larabci parsi da Bukhatir ke yi ba, amsawa tayi a mutumce a kuma ladabce kamar ba yau suka fara had’uwa ba.

D’an kawar da kan ta da zatayi ta kula duk mutanen har da Zafreen da Bukhatir sun zuba mata ido, nuna mata d’ayar yayi yace “Wannan kuma ita ce shugar mata, daga yanzu kuma zata zama mai kula da ke.”

Ita ma a wani harshen ta gaisheta, ba tare da tayi tunanin komai ba ta amsa mata a mutumce, har yanzu ma kallonta suka ci gaba da yi, Bukhatir kuma da musamman yasa aka samo masa mabanbanta yare dan ya tabbatar da abinda Laika ta fad’a masa na cewa canza yare kawai take sakin baki yayi yana kallonta, haka saida suka gaisa da kowa su kan su ma’aikatan a tsorace suka k’arasa gaisawa da ita, dan bakinta da yanayinta bai nuna koyen yaren tayi ba, kowane amsashi take da k’warewa a harshenta.

Kallonsu yayi yace “Zaku iya tafiya zan nemeku.”

Wani kallo ta watsa masa wanda yana had’a ido da ita yasa shi jin fad’uwar gaba, a wulak’ance tace “Da kasan suna jin yarenka me yasa baka basu izinin yi min ba?”

D’auke idonshi yayi daga cikin na ta ya shiga kame-kame yana fad’in “A… A… Am… Dama, ni ma ban sani ba.”

Sama da k’asa ga kalleshi ta yatsina fuska tace “Mak’aryaci.”

Da mamaki ya waro ido ya kalleta sai kula ya jinjina kai ya maida kallonshi ga Zafreen yace “Kin shirya ne? Dan. Dreba na jiranki zai mayar dake inda kike so.”

Da zumud’i Zafreen tace “E, amma ita fa?”

Had’e fuska yayi yace “Babu ruwanki da ita, ki je kawai.”

Gyara tsayuw tayi ta rumgume hannaye tace “Ba zai yiwu ba, na wa mahaifina alk’awarin zan koma tare da ita.”

Takawa yayi cike da izza ya tsaya gabanta yace “Zafeera ta zo kenan babu komawa, idan zaki je ki je, idan ba zaki je ba sai tare da ita, to ki sani zan sama miki d’aya daga cikin ma’aikata ki aura sai ki zauna a nan da lasisi.”

Cike da fad’a tace “Kai har ka isa ma, ba zan je ba kuma tare da ita zan bar nan.”

Girgiza kai yayi yace “Kar ki ce zaki kawo min wasa a nan, a halin da ake ciki yanzu na fara jin rayuwata ta fara d’aukar saiti daga zuwanta yau, na rantse miki da Allahn da nake bautawa ko ubanki ya zo nan ba zai rabani da ita ba.”

Gyara tsayuwa tayi tace “Lallai kana son tak’aloma kan ka yak’i da dakarun Khazira, ka sani sarkina ba zai barka ba, dan buk’atar da yake wa Zafeera ta take wacce kake mata ta shanye, dan haka ina mai baka shawara da ka gaggauta sakin yarinyar can mu tafi kafin mutuwarka ta riskeka.”

Da sauri ta k’arasa gabansu cike da masifa ita ma tace” Wai ku tsaya malamai, su waye ku? A kan wa kuke magana? Me kuka shirin aikata min ne da kuke jayayya haka kuma a kai na?”

Da lalama Bukhatir ya juyo gareta yana fad’in” Kin ga kwan…”

Da k’arfi Zafreen tace” Ba wani hankali da zata kwantar, kinga ke *k’anwata ce*, uwar mu d’aya kuma ubanmu d’aya, iyayenmu nemanki suke kamar zasu yi hauka.”

A hassale Bukhatir y kalleta yace” Amma ai ke neman kasheta kike, ni kuma kareta nake son yi daga sharrinku.”

Hannaye ta d’aga musu tace” Ya isa, ya ksa haka.”

Kallon Bukhatir tayi ido cikin ido ta tsareshi da su tace” Fad’a min, wacece ni? Ni d’in nan wacece?”

Janye idonshi yayi daga cikin na ta yana sunkuyar da kai yace” Zafeera, gaskiya ta fad’a, ke yar uwarta ce.”

D’aga mi shi hannu ta sake yi alamar yayi shiru, dafe kan ta tayi ta nuna kanta tana kallonshi tace” Ka ga da ni da wannan bamu da wata alak’a ta jini, makarantarmu ce kawai d’aya, ina ga fa kuskure kuka yi kuka d’auko ni a zuwan wacce kuke nema.”

A hankali Zafreen ta tako gabanta ta rik’o sark’ar dake wuyanta ta nuna mata tace” Kinga wannan sark’ar, a duk duniya zaki sameta ga wacce ta kasance mata ce a gurin sarkin Khazira, hakan kamar al’adace da aka gada iyaye da kakanni, wannan dake wuyanki mahaifiyarmu ce ta baki ita.”

Yanda take kallonsu galala yasa Zafreen fad’in” Ki yarda dani Zafeera, idan kin amince ki biyoni mu je tare, zaki gani da idonki kuma zaki ji daga bakin mahaifiyarmu.”

Girgiza kai tayi da taji yana mata wani nauyi yana kuma d’aukar zafi sannu sannu tace” Ku taimaka ku had’ani da iyaye na, na rok’eku.”

Cikin rarrashi Bukhatir yace” Shikenan na ji, yanzu ki kwantar da hankalinki kinji, zan kawo miki su kafin nan ki saki ranki, nan gidanki ne kiyi abinda kike so, kin ji?”

Jinjina kai tayi alamar to, Zafreen ta kalla kamar wata bak’uwar hallita a gurinta, wai yar uwarta? To ko dai bugun da aka musu a kai Zafreen ta samu matsalar k’walwa, ko kuma dai garin mahaukata aka kawota.

Da sauri ta kalli Bukhatir da ta ji waya na kururuwa a aljihunsa, yana ciro wayar ya duba mai kira ya kallesu ya musu nuni da yana zuwa, d’ora wayar yayi a kunne ya d’anyi nesa da su.

Kallon juna suka dinga yi har saida ya dawo kusansu ya kalli Zafreen yace “Tafiyarki ta fasu yau, sai zuwa gobe da safe.”

Da sauri tace “Saboda me? Ni bana so na kwana a nan, gidanmu zan je ni ma,tare da k’anwata.” Ta k’arashe tana kallon Ayam da ita ma ta kalleta da mamaki.

Ba alamar wasa yace mata “Saboda zamu karb’i manyan bak’i ne, daga yanzu zuwa lokacin da zasu iso an rufe shiga da fita.”

Da mamaki ta yatsina fuska tace “Su waye wannan?”

Saida ya nufi hanyar fita yace “Sarkin Giobarh.”

Da kallo suka bishi saida ya fita Ayam ta kalleta tace “K’anwarki?”

Dariyar baki da hankali ta mata ta juya ita ma ta bar d’akin duk da kuwa ta ji Zafreen na fad’in “E k’anwata ce ke, kuma nan gaba kad’an zaki san da haka, ki jira ki gani har nan mahaifina zai zo ya d’aukeki.”

Ganin ta fice bata kulata ba yasa ta jan tsaki ta bita da harara tace “Shegiyar banza, gidan uban wa ta iya yarukan nan?”

Sake wurga mata harara tayi ta k’ofar data fita tace “Sai na kasheki zan huta, indai har na kwana a nan to a nan zan kasheki saodai su d’auki gawarki.”

Buga k’afarta tayi alamar jin haushi ta juya ita ma zuwa inda ta fito tace “Banza.”

*04:30*

Tuni gidan ya kaure da hayaniya sakamakon dirowar bak’i daga masarautar Giobarh, sarki da kan shi tare da d’anshi mai jiran gado, mota takwas ta sauke inda fadawa da hadimai da ma’aikata suka shiga take musu gaba da baya da kuma gefe gefensu, inda suka had’e da mutanen Bukhatir wanda yayi iya k’ok’arin sa duk da bai karb’i sarautar ba, amma dake Ayam na hannunshi ya fara jiyo k’amshinta sai kawai ya tara jama’a shi ma aka musu maraba har zuwa babban falon.

 

*Alhamdulillah*

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like

YAU DA GOBE 27&28

Advertisement   🅿️27&28 …..wani irin zabura tayi had’e da k’ok’arin turesa….amma takasa k’arfi ba d’aya ba. Gogan kuwa baya…