Advertisement
*16*
Daga b’angaren Habbee ta numfasa tace “Gimbiyata, ki gafarce mu, tabbas kan ki zai d’aure idan kika ji b’oyayyan sirrin dake tattare da ke, watak’ila ma ki kasa yarda damu, amma dai gaskiya ce wacce kowa ya san ta ban da ke kawai, fatana kawai idan kinji gaskiyar nan kar mu zaba ababen zarginki bare ki hukunta mu.”
Rud’un data shiga ne yasa sai ta ji kamar bata fahimtar, sai kuma tayi k’arfin halin saurin fad’in” Dakata Mah, wai ke ma ya kike neman kin d’aure min kai ne ? So kike ki tabbatar min akwai alamar gaskiya a zantuttukan mutanen nan kenan?”
Numfashi ta sauke har saida ta ji sautinshi a kunnenta kafin tace” Hakane ranki shi dad’e.”
K’ank’ance idonta tayi tana karkad’a yatsanta tace” Kenan gaske da yarinyar nan tace ni yar uwar ta ce? Kuma mahaifinmu shi ne…”
Da k’arfi tace” Kai… Ina ba zai yiwu ba, kuna yanzu Mah?”
Saida Habbee ta kalli lafiyayyen d’aki da suke sannan tace” Wani waje ne mai sirri ne, ya ce kar mu fad’a saboda tsaronmu na wuyansa.”
A harzuk’e tace” Ina kuke mah? Ina son ganinku yanzu.”
A ladabce Habbee tace” Kar ki damu gimbiyata, zamu had’u nan kusa.”
Advertisements
D’auke wayar tayi a kunnenta ta mik’a masa tarz da fad’in” Ina son ganinsu yanzu, ya za’ayi?”
Mik’ewa yayi tsaye yana huro iska ya kalli fuskarta, saida ya mayar da wayar aljihunsa a nutse yace” Ki gane Ayam, rayuwarki na cikin gagarumin had’arin da ubangiji ne kad’ai yasan iyakarsa, ba wai wani banza bane ke neman rayuwarki, masarautu ne suke wawarki, yayin da wasu daga gefe ma suka nemanki ruwan a jallo, dayawansu a shirye suke da su biya bilyoyin kud’i dominki, wasu alkairi ne a zuk’atansua game da ke, wasu kuma akasin haka, na d’auki alhakin kula da ke ne dan na ga na hana masu nemanki cin nasara a kan ki, ki bani dama ki kuma kwantar da hankalinki, hakan zai bani damar ceto rayuwarki.”
A sanyaye kuma a ladabce cikin sigar tausayi tace” Wane irin had’ari ne na ke ciki haka?”
Kai tsaye yace mata” Had’ari ne da ya kai matakin kisa, kamar yanda na fad’a miki kowa da manufar sa ta son samunki, wasu na nemanki ne kawai dan su kasheki.”
Tsoro k’arara ya bayyana a tare da ita ta zazzaro ido ta ji kayan cikinta na neman yamutsawa, ckkin muryar d’ar-d’ar tace” Me na aikata musu haka da suke son kashe ni?”
Da hannu ya mata alamar ta zauna kan gadon, zaunawa tayi tana rarraba ido dan tsorl ya gama kamata, a cikin aljihunsa ya ciro takarda, zaune yayi kusanta ya warware takardar ya mik’a mata yace” Karanta.”
Karb’a tayi ta fara karanta takardar dake nuni a cikin littafi aka cirota ko kuma an buga irinta ne, ba wani dogon bayani bane a takardar face zanannun zanen da aka tsara kuma aka wassafasu a cikin tsari ta hanyar fad’in _” A wace shekara ce? A wane wata? Wace rana ce wannan? Babu wanda zai sani a cikinmu, saidai alamun bincikenan malaman babbar fadar k’asar Texanda dake birnin Khazira ya tabbatar da za ta zo, za’a haifeta ne kawai dan zuwa da sabon tsari sannan ta wanzar da adalci, zuwanta shi zai kawo k’arshen duk wani azzalumi ko da sarkin dake mulki ne, zatayi mulki na ban mamaki da ba’a tab’a kwatanta irinshi a k’asar ba, zata kafa tarihi da dubbanin shekaru zasu shud’e ana magana a kai, tambayar a nan ita ce, *talakawan gari ne zasu haifo wannan biwar? Ko kuma cikin msu kud’i ne da iko ? Ko kuma dai wannan lu’u lu’u zata fito ne daga masarautar khazira*?”_
Da mamaki ta kalleshi dan abun bai wani d’ad’ata a k’asa ba tace” Me wannan ke nufi? Jaridar yaushe ce? Ko kuma labarin film ne, kana so na fito jarumar?”
Wani murmushi ya saki dan sosai ta bashi dariya, gyara zamanshi yayi yace”Kin fahimci me labarin ke magana a kai?”
Jinjina kai tayi ta yatsina fuska tace” Kusan haka.”
Shi ma jinjina kan yayi yace” Ayam wannan rubutun wani babban mutum ne yayi shi, wannan mutumin shi ma yana da baiwa irin ta wannan da akayi magana za’a haifa, sanadin baiwar da Allah ya masa gaba d’aya masarautar khazira aka shiga girmamashi, sanda ya sanar da abinda zai faru gaba ba kowa ya yarda ba, saidai kuma an zuba ido ana jiran tsammanin a ga ta inda wannan zab’abb’iyar zata sake fitowa.”
Gyara zama ya sake yi ya sauke numfashi yace” Shekara ta dubu biyu daidai wata na hud’u sarauniyar khazira ta samu ciki, tun samun cikin na ta sai wasu alamomi suka dinga bayyana mata a mafarkinta, bayan ta sanar da babban malamin fadar k’asar wanda yake jika ne ga waccen zab’abb’en, sai ya sanar da ita ai tana d’auke da cikin wannan ‘yar baiwar ce, sai gashi kam bayan wata shida ta haifi yarta mace wacce aka lak’abawa sunan *Zafeera* tun kafin ma a haifeta, wanda Zafeera yake nufin haske marar yankewa, a wajen wasu haihuwarta zai kawo k’arshen matsaloli da dama musamman na mulkin zalinci da sarki ke yi a wannan lokacin, amma a wajen wasu bayhanarta sharri ne da kusantowar rugujewarsu, hakan yasa a daren da aka haifeta, tun bata bud’i ido ta kalli mahaifiyarta ba sai aka nemeta aka rasa.”
Advertisements
Cike da jimami da rashin jin dad’i Ayam tace” Ayyah, to amma ya mahaifiyarta tayi? Gaskiya akwai tashin hankali.”
Siririn murmushi yayi yace “Ba kamar yanda kikayi hasashe bane.”
Gyara zama tayi tace “Ban gane ba?”
Kallon fuskarta yayi yace “Mahaifiyar da kan ta ne ta b’atar da ‘yarta ta hanyar damk’a amanarta ga amintacciyar jakadiyarta da kuma mijinta.”
Waro ido tayi tace “Toh? Amma gaskiya tayi k’ok’ari, kuma hakan ya k’ara tabbatar min da soyayyar uwa daban take.”
Jinjina kai yayi alamar gamsuwa sai kuma yayi shiru, ita ma d’an shiru tayi na dak’ik’u sai kuma ta kalleshi tace “To amma mahaifinta fa? Ban ji ka ambace shi ba.”
Ajiyar zuciya ya sauke ya tsura mata ido yace “Ba da sanin mahaifin yarinyar ta bada ita ba.”
“Me ya sa to?” Ta tambaya tana tsareshi da ido, mik’ewa yayi tsaye ya juyo ya fuskanceta yace “Akwai wani al’amari ne a tare da shi mahaifin na ta, amma yanzu ba zan sanar da ke ba kai tsaye.”
Mik’ewa tayi ita ma tace “Me yasa to?”
D’auke idon shi yayi a cikin na ta yace “Ki tambayi wani abun daban ba wannan ba, lokaci ne zai fahimtar dake waye shi d’in.”
Girgiza kai tayi ta gyara tsayuwa tace “To amma me yasa ka bani wannan labarin? Kana da wata alak’a ne da masarautar Khazira ?”
Kallonta yayi sosai cikin tattausan murya yace “Bana da wata alak’a da ita, ai kin gani ni ga masarautar mu nan, amma fa ke kina da alak’a da wannan masarautar.”
Ya fad’a yana nunata da yatsa, zaro ido tayi tsabar mamaki sai kuma ta k’ank’ance su tana kallonshi kamar bata gane me yace ba, a hankalce ta shiga d’ora duka kalamanshi a mizani kafin daga bisani ta kalleshi tace” Wace irin alak’a? Na rok’eka Umad kar ka ce min labarin daka bani ina da nasaba da shi.”
Hannayenshi biyu ya zuba cikin aljijun rigarshi ta sanyi bak’a mai hula sannan ya kalleta yana sauke numfashi, jinjina mata kai yayi sosai sannan ya d’ora da fad’in” Tabbas, labarin dana baki ta ko ina kina da nasaba da shi, Ayam ke ce wannan yarinyar baiwar, ke ce lu’u lu’un Khazira, Ayam ke ce *Zafeera*.”
Zuba masa ido tayi, jiri ne ta ji ya fara d’ibarta, da d’an sauri ta shiga sauke numfashi tana girgiza kai tana so tayi magana, saidai tashin hankali da halin ba zatar data shiga ya fi knarfin d’aukar hankalinta, kafin ta ankara jirin nan ya kwasheta ya zubar a k’asa, dan dama tana tattare da matsananciyar yunwa ga baccin data kasa samu tayi.
Da azama ya sunkuya yana girgiza ta da kiran sunanta, d’ora yatsanshi yayi daidai hudar hancinta ya saurari sautin fitar numfashinta, tabbatarwa da yayi tana numfashi yasa shi saurin d’aukarta cak ya shinfid’e kan gadon, zaune yayi daf da ita yana kallon fuskarta cike da tausayinta, hannunta ya kama ya dinga shafa tafin hannunta yana murzawa da sauri sauri, a hankali kam sai ta fara d’an motsa idonta amma kuma bata bud’esu ba.
Sunkuyar da kan shi yayi kamar zai sumbaceta ya kira sunanta “Ayam.”
Jujjuya kan ta ta fara yi tana yatsina fuska tace “Na’am, Mahh… Mah.”
Sakin tafin hannunta yayi ya shiga murza tafin k’afarta, sannu sannu ta fara bud’e ido har ta bud’esu tas a kan rufin d’akin, da sauri kuma sai ta kalleshi suna had’a ido ta yunk’ura zata tashi, luuuuuu da ta ji tayi d’akin ya juya mata yasa ta komawa ta kwanta, kamar zata fashe da kuka tace “Yallab’ai kira min iyaye na, ina so ‘a gansu yanzu, na rok’eka ka taimaka.”
Mik’ewa yayi tsaye yana had’e fuska yace “Ki kwanta ki huta yanzu, zan sa a kawo miki abinci ki ci, da safe zamuyi koma menene.”
Fashewa tayi da kuka marar sauti ta dafe goshinta tace “Me yasa ba zaka fahimce ni ba yallab’ai, abinda kuka zo mi da shi safiya zuwa daren nan ya girmi tunani na, ko a tatsuniya ban tab’a kawo hakan zai faru ba, ta ya lokaci d’aya zaku nuna min wad’anda suka reneni ba su ne iyayen da suka haifeni ba? Ta ya kuke so na yarda da ku haka?”
Sauke numfashi yayi yace” Na fad’a miki iya abinda zan iya yanzu, zuwa safe zamu ci gaba da tattaunawa.”
Yana fad’a ya fice a d’akin inda ta bishi da kallo, kasa kukan tayi mai sauti sai marar sauti hannunta kuma dafe da kan ta saboda yanda yake juya mata.
Ba’a d’auki lokaci mai tsayi ba wata matashiyar jakadiya ta shigo d’auke da faranti a hannunta shak’e da kayan abinci, ajewa tayi cikin ladabi tace “Ranki shi dad’e ga abinci inji yarima na, da wani abu da kike da buk’ata?”
Mik’a mata hannu tayi tace “Kamani na tashi.”
Da sauri ta kamata tayi zaune, a raunane tace “Bani ruwa.”
Sunkuyawa tayi a ladabce tace “Amma ranki shi dad’e yallab’ai Umad ya ce ki fara da ruwan d’umin nan, hakan zai ba wa hanjinki damar warwarewa.”
Jinjina kai kawai tayi almar to, tana kallo ta had’a mata tea da zuma kad’an a ciki ta mik’o mata ta karb’a, a hankali ta dinga kurb’awa tana sha, saida ta shanye tas ta mik’a mata kofin ta ajiye.
Bangon d’akin ta kalla inda agogo ya nuna mata k’arfe 01:15, sake mik’a mata hannu tayi tace “Taimaka min na sauka, ina so zan shiga ban d’aki.”
Da taimakonta ta shiga ban d’aki, da fari fitsarin dake mararta ta so tsiyayewa, sai kuma ta cire kayanta ta shiga baho ta dinga tsala wankanta tana k’arewa ban d’akin kallo, had’uwarta da tsabtarta duka sun birgeta, ga rigar wanka kala uku a jere haka ma towel, mayukan wanke baki da shampoo had’a da turaren baki da na ruwa, sam sai ta manta ma da dare ne ta dinga anfani da komai kamar wata gasar zata tafi, sai da ta ji agogo tayi alamar k’arfe biyu ta buga yasa ta fitowa sanye da rigar wankan data sauko sosai a hannayenta rigar kuma har ta kusa sauka a k’afafunta.
Tana fitowa ta samu matashiyar nan durk’ushe da alama ita take jira, da mamaki tace “Wai dama kina nan baki tafi ba?”
Da ladabi tace “Ban tafi ba ranki shi dad’e, ina jiran umarninki ne ko kuma idan da wani abu da kike da buk’ata.”
Numfashi ta sauke ta k’araso gaban gadon ta zauna tace “To yanzu zuba min abinci na ci sai ki tafi ki kwanta ke ma, dare yayi fa sosai.”
“To ranki shi dad’e.” Ta fad’a tana mik’ewa, saida ta gama had’a mata lafiyayyen abincin ta ajiye mata gabanta har da ruwa da lemu, kallonta tayi tace “Ki je kawai, da safe kya zo ki d’auke kwanukan.”
Jinjina kai tayi ta fita tana mata saida safe, a ladabce kuma a hankalce ta shiga tsakurar abincin tana yi tana nazarin duk abinda ya faru daga safe zuwa daren nan, sai ta ji kamar tayi dariya saboda a almara take ganin abun, sai kuma ta kyab’e fuska ta matso k’walla saboda jin kamar zuciyarta na son yarda da abinda suke fad’a mata.
Tana kammala cin abincin ta koma ban d’aki ta wanke bakinta ta dawo, ruwa tasha kad’an sannan tayi zaune, ta jima zaune kafin ta gyara ta kwanta ta ja zanin rufa lallausa ta rufe jikinta ko rigar wankan bata cire ba.
*Egypt*
Kamar da wasa mai kula da ita ta tabbatar da bata d’akin, fargaba da firgici sai ya hanata fad’a masa ta shiga neman hanyar da zata sanar masa.
Yana tsaye tare da Zafreen ta dafe k’ugu ta matsa ya mayar da ita gidansu ko ta jaza masa bala’i, cike da jin haushinta yace “Kiyi duk abinda zakiyi, ba zan mayar da ke d’in ba sai gari ya waye.”
Juyawa yayi ya shige ciki kai tsaye d’akin da Ayam ta ke ya nufa, bai samu kowa a d’akin ba amma dake har da mai kula da ita su biyun sai kawai ya fito da tunanin ko sun shiga zagayawa da iga ne a gidan, yana fitowa suka had’a da d’aya daga ciki ta dawo, da mamaki ya k’are lata kallo yace “Ina gimbiya take?”
Da ladabi tace “Tana ciki yallab’ai, ita ce ta aikeni na samo mata wannan.”
Ta fad’a tana nuna furanni masu kyau, da mamaki yace “Amma kuma bata ciki, me ta ce miki zatayi da su?”
Girgiza kai tayi tace “Gaskiya ban sani ba ni ma yallab’ai.”
Tureta yayi gefe ya fita a b’angaren ya shiga zagayawa duka gkdan amma shiru, b’angaren ya sake dawowa sai kuma ya ci karo da d’aya mai tsaronta sai gumi take ido sun mata jajir, cikin daka tsawa yace “Ina gimbiya ta?”
Cikin i’ina da tsoro ta shiga masa nuni da hannu tace “Yallab’ai ni ma, wallahi ban san inda ta shiga ba.”
Da matsanancin mamaki yace “Baki san inda ta shiga ba? Kika ce bako san inda ta shiga ba?”
Gaba d’aya ya tashi hankalin gidan ta hanyar sa wa a bincike ko ina, ta b’angare d’aya kuma waya yake amsawa daga waje yana bada masaniya daga masu taimakonshi, dattijon nan dake tare da shi yana gefe tsaye ya kalleshi yace” Yallab’ai. ”
A hassale yace” Me ye?”
A ladabce yace” Ina ga fa kamar sarki Wudar raina mana wayo sukayi.”
Zazzaro masa ido yayi yace” Kamar ya?”
A sanyaye yace” Ina tunanin su suka d’auke ta.”
Jim yayi yana sake rarako idonshi waje ya jinjina kai yace” Kuma fa haka zai yiwu.”
Jinjina kai yayi yana murmushi yace” Lallai sarki Wudar ya nemi tashin hankali da ni, kuma zai ga abinda ya fi k’arfinshi.”
Kallon dattijon nan yayi yace” Zuwa wayewar gari zai samu sak’o daga sarkin Khazira. ”
*Yan uwa kuyi hak’uri da wannan dan Allah*
*Alhamdulillah*
GIPHY App Key not set. Please check settings