Advertisement
*5*
Ayam data rumgume hannaye a k’irji cike da izza, salo da kuma gadara tana kallon k’wayar idonshi ita ma cikin harshen Gallois da bata tab’a sanin ta iya ba tace “Af Allan, ond byddwch yn mynd ar ol ar fy ol (zan fita, amma ka koreni a mutumce).”
Baisan sanda mamaki ya sake bayyana a fuskarshi ba, gyara tsayuwa yayi da kyau dan ya Fahim I shekarar da zaiyi kisan kan shi ce ta kama, nuna ta ya sake yi a dake yace” Ke, ke mahaukaciyar ina ce?”
Ba tare data rusuna idonta ba ta sake muskutawa ita m’a sannan tace” Sanin mahaukaciyar ina ce ni ba zai anfaneka da komai ba, kawai ka janye kalmar nan ta b’arauniya daka fad’a min.”
Hannayenshi bibbiyu ya rabka a k’ugunshi ya dafe jajayen idonshi a kan ta, ba alamar wasa a tare dashi yace” Ke ‘yar garin nan ce?”
K’urawa fuskarsa ido tayi ba tace komai ba, ganin bata da niyyar magana sa茂 ranshi ya sake b’aci, a harzuk’e ya cabki hannunta da nufin fitar da ita, da k’arfi ta fincike hannunta tana mai kallon inda ya rik’e, wani abu ta ji kamar wutar lantarki tana janta.
Kallonta ya shiga yi shi ma da tunanin ko dai abinda ya ji ita ma ta ji? Tsaki ya buga kawai ya juya ya sake shigewa ban d’akin zuciyarshi kamar zata fashe.
Ayam ma na ganin haka ta ja k’afarta data mata nauyi ta fita ita ma, a bakin k’ofar ta samu su Deeyam suna jiranta, da zumud’i Sabrine tace “Ya dai? Me ya faru 脿 ciki?”
Shiru tayi sa茂 sauka a matakalar data shiga yi, Deeyam ce tace “Ya muka ji kinyi ihu? Ko dai d’an hannu ne shi ma?”
Advertisements
Babu wacce ta amsa ma har suka koma ta inda suka fito suka koma d’akinsu suka kwanta, amma Ayam sai tayi zaune akan gado ta zabga tagumi tana sake kallon wuyan hannunta daya rik’e.
*A* wajen Umad ma saida ya ji an rufe d’akin ya fito, wajen hoton ya k’arasa ya durk’usa ya shiga tattare glass d’in, a kwandon shara ya zuba sannan ya d’auki hoton yana kallo, cikin yarenshi yace ” *Majka* (uwata), kiyi hak’uri ba laifina bane, waccen mahaukaciyar ce da ban san me ta zo nema ba.”
Ba tare daya saka kaya a jikinshi ba shi ma ya zauna kan gadon yana ta kallon hoton nan, so yake yayita zazzaga masifa ko ya ji sauk’i, amma dake mutum ne ba mai hayaniya ba sa茂 kawai yake ta tsaki shi kad’ai.
Sai dai ya k’agu gari ya waye ya bincika ya ji wacece wai ita d’in? Da wannan tunanin har bacci ya d’aukeshi bayan ya tofe jikinshi da addu’o’in tsari.
*Washe gari*
Zazzaune suke a cikin aji kowa na mazauninshi zaman mutum d’aya, sunyi shiru kuma sun nutsu suna sauraren jawabain ban kwanan da malam Pedro ke musu, yana gamawa yayi murmushi a harshen fransanci yace “To d’alibai, ni zan tafi yanzu, sai mun sake had’uwa da ku, ina muku fatan nasara.”
A tare dukansu suka amsa da “Za mu yi kewarka malam.”
Dariya yayi wanda hakan yasa Ayam juyawa ta kalli Deeyam cikin rad’a tace “Malam Pedro na dariya dama?”
Dariya Deeyam tayi a kan idon malamin, harara ya galla musu yace “Hirata kuke ko?”
Da sauri Ayam ta girgiza kai alamar a’a, shi ma girgiza kan yayi yace “Na sanki fa Ayam, da ni d’in nan ragon namiji ne da kin jima da sani hauka.”
Girgiza kai ya sake yi yace “To d’alibai, ni zan tafi na bawa sabon malamin ku dama ya shigo dan ya gabatar muku da kanshi.”
Hannu ya d’aga musu ya nufi hanyar fita, su ma hannun suka shiga d’aga mi shi, tun bai k’arasa fita ba Ayam ta mik’e ta tsaya a inda ya tsaya shi ma, irin tsayuwarshi tayi da yanda yake cije fuska ta tsuke baki ta fara magana kamar yanda yake alama tana kwaikwayonshi tana fad’in “To ni zan tafi, wani aiki ne ya taso da ake neman agazawarmu, amma ban ji dad’in rabuwa da ku ba musamman da shekara ta kusa k’arewa, amma duk da haka…”
Advertisements
Mik’ewar da duk sukayi d’aliban suna gaishe da malamin daya shigo yasa Ayam k’amewa tare da bud’e baki irin” Na shiga uku.”
Cikin sand’a kamar wacce k’wai ya fashe ma a cikita shiga takawa har ta zauna teburinta, tana jin takon takalmin malamin suna bada sauti d’a茂 bayan d’aya, saida ya tsaya tsakiyarsu sannan ya musu izinin zama.
Shiru ajin ya d’auka bayan sun zauna, shi yana k’are musu kallo su ma suna k’are mishi kallo suna fahimtar wane iri ne shi ? Zaiyi dad’in sha’ani ko kuma d’aurarrar fuska ce dashi kamar malam Pedro.
Ba tare daya juyar da kanshi ba iya idonshi kawai ya zuba mata, fuskar nan tamau da ita ba alamar annuri cikin dakusashiyar murya mai firgitarwa yace “Ya sunanki?”
Kamar sauran d’aliban ita ma d’aga kai tayi ta kalleshi dan son sanin da wa yake, idon da suka had’a yasa gabanta tsinkewa ya fad’i tare da kad’awar kayan cikinta, 脿 take kawai ta tausayawa kanta, marairaicewa tayi tana matse k’afafunta daga sama, wuwulk’ita idonta ta shiga yi cikin daburcewa da sark’ewar murya tace “A.. Yam.”
Wannan karan d’auke idonshi yayi daga kanta ya sake fad’in “Sunanki?”
‘Yar k’walla kawai ta ji ta zo mata a kan kunci, a sanyaye ta sake maimaita “Ayam.”
Takowa ya fara yi zuwa gabanta, da sauri ta sauke idonta tana kallon teburin, saida ya tsaya daf da teburin 脿 mugun kausashe yace “Ayam, baki da sunan uba ne?”
D’aga ido tayi da sauri ta zuba cikin na shi idon, hawaye taji kan kuncinta suna kwaranya, sosai maganar ta mata zafi, amma saita shanye tunda malaminta ne a aji, kanta sadde k’asa tace “Ayam Utais.”
Cikin tsananin bala’in haushinta da yake ji 脿 tsawace ya buga teburin da take zaune 脿 kai da hannu cikin d’aga muryar data sa ajin amsawa baki d’aya yace “Ayam Utais, ba’a koya miki tarbiyyar mik’ewa tsaye yayin magana da malami ba?”
Tunda ya buga tebur d’in yan matan ajin wasu sukayi ihu wasu kuma suka k’ame, kamar dai Ayam da ita ma k’amewar tayi amma fa kuma idonta cikin na shi.
Abu d’aya ya zo masa a daidai lokacin, maganarshi da babban malamin shi a sanda yake son sanin alamomin da zai ganeta, a yanzun da abun nan ya faru sai ya tuna sanda malamin yace _”Had’uwarku ta farko ba zata bada k’ayatarwa ba, saidai 脿 wurinka da zaka aje hankali, kowane motsinta zai baka al’ajabi, a zahiri mace ce kamar kowace mace, tana jin tsoron abinda zai tsorata kowace mace, saidai ba komai ke tsorata ba, akwai b’oyayyar jarumta a tare da ita, abinda ya cancanci ya bata tsoro ba shi ke tsorata ba kai tsaye, wanda kuma kai zai iya kayar maka da gaba, sa茂 kaga ita abin ado ne a gareta, saidai fa duk da haka mace ce mai birgewa, saboda tana da abinda duk wani namiji yake tsananin so ga ‘ya mace.”_
A lokacin tambayar daya masa ita ce _” Menene shi abun?”_
Murmusawa malamin yayi sannan yace _” Rauni, tana da rauni, dan bata iya kare kanta ga duk wani abun cutarwa.”_
Ajiyar zuciya Umad ya sauke ya mik’e daga rusunawar da yayi 脿 ranshi yana fad’in” Ba ita ba ce, wannan ba zata tab’a zama Zafeera da ake fad’a ba.”
Sake kafeta yayi da ido yace “Jiya da dare me ya kaiki d’akina?”
Zaro ido tayi tana kallon shi kamar taga bak’uwar hallita, sororo tayi ta rasa bakin magana, kallonta ya sake yi yace “Cire hular kanki, ki zama daidai da sauran d’aliban.”
Tsura masa ido tayi a ranta tana tunanin watak’ila fa son takura mata yake saboda yanda suka fara had’uwa, to amma ita ma zata ji dashi a haka, a hankali tasa hannu ta cire hular ta kan ta.
D’an zaro ido yayi yace” What?”
Jinjina kai yayi a dak’ile yace” Kin kad’e.”
A sanyaye ta turo baki gaba tace “Sorry sir.”
Juyawa yayi ya kalleta yana rumgume hannaye da mamakin yanda ta gagara mik’ewa tsaye sannan ta masa magana, ita wacece? Sauran d’aliban ya kalla yana sauke hannayenshi daga k’irji yace “D’alibai, sunana Umad Wudar, sabon mai koyar da ku, ina fata zaku bani had’in kai mu k’arasa zangon shekarar nan daku lafiya, ina so ku d’auke ni a matsayin malaminku mai sauk’in kai a aji, amma a wajen aji zamu iya zama abokai, hakan zai k’ara mana fahimtar juna kuma ku ji a ranku daidai na ke daku, kun fahimta.”
A tare cikin d’aga sauti suka ce” E malam.”
Jinjina kai yayi ya nuna d’alibin farko yace” Ku gabatar min da kan ku.”
D’ai bayan d’aya suka dinga mik’ewa suna fad’in sunan su, saida aka kawo kan Ayam ta mik’e ta fara fad’in” Ay…”
Da hannu ya mata alamar zauna tare da fad’in” Me ye abun dad’i a sunan naki da zan ji shi sau biyu? ”
Idonta tar a cikin na shi tace” Sorry sir.”
Girgiza kai yayi tare da jan tsaki ya kalli Deeyam dake bayan ta yace” Uhum!”
Mik’ewa tayi ta fad’i sunanta, har zata zauna yace” Ana koyar daku turanci ne a nan?”
Girgiza kai tayi tace” A’a malam.”
Kallon Ayam yayi ya yatsina fuska a zuciyarshi yace” Gidan uban wa ta iya sorryn?”
Haka aka gama gabatarwa ya shiga darasinshi ba tare da b’ata lokaci ba, awa uku suka d’auka ba hutu ba shan iska, gashi in suka had’a ido da ita sai ya galla mata harara, ita kuma haka kawai taji kamar ta samu abokin wasanta, ta k’i d’auke idonta daga kan shi sai binshi da kallo take.
Saida ya dubi agogon dake tsintsiyar hannunshi sannan yace” D’alibai ina ga anan zamu dakata, shin da mai tambaya a darasinmu? Ko kuma wanda bai gane wani abu ba?”
Girgiza kai sukayi dan magana ta gaskiya sun fahimci darasin shi sala-sala, dan haka da ya ga babu mai tambaya ya juya da niyyar tattara nashi ya nashi.
K’afa d’aya kan d’aya ta d’ora ta rumgume hannaye a k’irji tace” Sir ina da tambaya?”
Wani iska ya feso ba tare daya juyo ba dan yasan ita ce, saida ya sauke nufarfashi ya saita nutsuwarsa ya had’e b’acin ranshi sannan ya juyo a dak’ile yace” Uhum.”
Duk da ba ita yake kallo ba sai yaji gabansa fad’uwa yake kamar mai jin tsoron tambayar da zatayi, cikin siriryar muryarta tace” Sir, indai har dorinar ruwa kakkausan jiki ne da ita ta yanda alburushi baya mata illa, kenan wane irin makami ne zai iya cutar da ita kai tsaye?”
Kallonta yayi wannan karan kallo irin na k’urilla, kamar sub’utar baki yace da ita” Bomb.”
Da mamaki a fuskarta tace” To amma yallab’ai ai mu ba’a yarje mana aiki da bomb ba.”
Wani tsakin ya kuma ja ya juya zai d’auki jakarshi ta sake fad’in” Yallab’ai tambaya ta gaba?”
A hassale ya juyo yace” Ina jinki.”
Cike da son danne dariyarta tace” Ka fad’a mana zakanya tafi zaki iya farauta, me yasa to duk da shi ne namiji kuma sarki?”
Tsurawa fuskarta ido yayi dan ya fahimci ba shashashan tambayoyi take yi ba, cikin d’an saita muryarsa yace” Saboda shi zaki baya son jin rauni a jikinshi, sannan yana da son hutu kamar yanda yake da jin izza ksancewarsa sarki.”
Jinjina kai tayi sannan ta sake fad’in” To amma kuma me yasa zaki baya mu’amula da zakanyar da bata kusa cimmasa a shekaru ba?”
Tarr! Ya kalli k’wayar idonta mai kama data mage a cikin dare, sauran d’aliban ya kalla sannan ya kalleta yace” A nan ajin nasan babu wacce ko wanda bai balaga ba ko?”
Ihu suka saka tare da fad’in” E yallab’ai.”
Jinjina kai yayi fuskarshi ba alamar fara’a sannan ya sake kallonta yace” Zaki ai sarki ne, jarumtarsa da yarda da kanshi yasa baya tarayya da wacce yasan ba zata iya d’aukarsa ba.”
Cike da gadara ya juya ya d’auki jakarsa inda ajin ya kaure da ihu da maganganu, saida ya fita a ajin Ayam ta mik’e tsaye akan teburin tayi wata irin k’ara tare da tintserewa da dariya tace” Yan mata wai kun yarda?”
Duk yan matan ajin suka amsa mata da” A’a.”
Wata ihu ta sake yi tace” Ni ma ban yarda ba, abinda na yarda da shi shine mace rijiya ce, kowace irin guga aka zura mana zamu karb’a kuma mu bada ruwa.”
Caraf a kunnen Umad da bai k’arasa fita ba, juyowa yayi ya kalleta, samun kanshi yayi da sauke idonshi kan ‘yan tsiraun nonuwanta dake cikin rigar kayan makarantar, yan firit da su ta yanda zai iya had’esu duka biyu a tafin hannunshi kuma ba lallai su cika masa hannu ba, a hakan ma dan yana tunanin ta saka bras wacce zata k’ara mata aukinsu, girgiza kai kawai ya sake yi yana jan tsaki yace “Baki san me zaki yake nufi ba.”
Keb’antaccen gurin cin abincin malamai ya nufa, bayan ya gabatar da abinda yake da buk’ata sai kuma ya kasa ci ya tsaya amsa waya, Haman ne ya tambaye shi “To ya sabon aikin na ka?”
Girgza kai yayi yace “Ba dad’i.”
Dariya yayi daga b’angrenshi yace “To amma ka fara abinda ya kai ka ne? Akwai wani abu daka fara samu?”
Shiru yayi tare da sauke ajiyar zuciya, jin bai amsa mishi ba yasa Haman sake fad’in “Lafiya ko Umad?”
Shafa sumar kanshi yayi wacce har yanzu yake takaicin rabashi da ita da akayi sannan yace “Tana jaririya fa ta b’ata, kuma babu wani wanda yasan wani abu a kan ta, ta ina zan ma fara nemanta a Larhjadin? ”
Dogon tsaki ya ja wanda hakan kamar d’abi’arsa ce kafin yace “Ya binciken da na saka ka? Ka samu wani abu ne ?”
Cike dta karsashi yace “E yallab’ai, yanzu haka ma zan je wajen wani ne dan samun wasu bayanai.”
Jinjina kai yayi yana shafa sajenshi yace “Duk yanda ake ciki ka sanar min.”
Bai jira amsawarshi ba ya datse kiran ya aje wayar gefe, cike da k’yank’yami ya fara cin abincin, duk da tsabtarshi da kyau da kuma dad’i, amma shi dai bai masa ba ko kad’an,haka ya d’an tsakura ya mik’e ya bar wajen.
*Alhamdulillah*
GIPHY App Key not set. Please check settings