Advertisement
*7*
Ta b’angaren wurin kwanan hadimai da bayin gidan suka bi suka wuce, yanda hadiman suka yi tsuru suna kallo cikin jimami ana wucewa da sarauniyarsu yasa duk suka ji ba dad’i, a sanyaye take wucewa har saida suka kusa shiga ta wata kusurwa, d’aga kanta tayi dake k’asa ta kalli wani d’aya daga cikin fadawan gidan, wani k’ayataccen murmushi ta sakar masa ta juya harshenta zuwa larabcin parsi tace “Ko ta halin yaya kayi k’okari ku had’u da ita, ka sanar mata ta fad’a musu su ninka kulawarsu da saka ido a kan ta, dan komai ya kusa fitowa fili.”
Sake fad’ad’a murmushi tayi ta d’ora hannunta akan shi kasancewar matashi ne tace “Ka kula da kan ka.”
Duk da hawayen dake taho mishi saida ya rusuna mata yana jinjina kai alamar karb’ar sak’onta, wucewa sukayi haka hadiman wasu ke kuka wasu kuma jimamin ne kawai a fuskarsu, a haka aka shiga da ita wata hanya dake sadar da mutum zuwa k’asa, tafiya sukayi mai nisa a cikin wurin da zaka rantse a wata duniyar kake ko kuma wani ramin b’era ne, banda jan fitilun da suka haska gurin da zai kasance mai duhun gaske.
A hankali suka fara isowa kurkukun inda d’akunan suke a laye kowane mutum d’aya ne a ciki, k’ofofin bak’in k’arfe ne da manyan kwad’on da ake datse k’ofar, daga sama kawai ake k’aramar tagar da iya fuska zata iya lek’awa ta ga na ciki.
A b’angaren dama ya bud’e mata wani d’aki ta shiga sannan ya mayar ya rufe, babu komai a d’akin banda shafaffen simiti, baya ga haka babu komai a d’akin dan ko wuta babu kuma ba wata taga bayan wacce ke jikin k’ofar, ko haske iya na fitilun dake corridor wurin ne ke d’an haskaka sauran d’akunan.
A hankali ta sulale ta zauna a wurin tana fashewa da kuka, kukan ba wai na canjin daya risketa bane a take, na yanda ‘yarta da kuma marik’anta zasu kasance, tasan dole su sake jajdadda nemanta, suna samunta kuma kasheta zasuyi, wannan tunanin yasa ta yin kuka kamar zata shid’e.
*Giobarh*
Advertisements
Suna had’uwa da mutumin ya mik’o masa k’aramar farar takarda a nad’e, karb’a Haman yayi ya bud’a takardar ya karanta sannan ya kalleshi yace “Ka tabbata?”
Jinjina kai yayi yace “Na tabbata yallab’ai.”
Shi ma jinjina kan yayi ya fito da dunk’ulen kud’i ya bashi yace “Nagode.”
Da sauri ya karb’a yana fad’in “Ni ma nagode yallab’ai, idan buk’atar wani abun ta taso ka nemeni kawai.”
Jinjina kai Haman yayi amma bai ce komai ba, lafiyayyar motarshi ya shiga cikin salo da k’warewa ya tayar ya bar gurin, tafiya yayi mai nisan gaske kafin ya isa ga lambun da aka bashi kwatancen.
Fitowa yayi a motar ya tunkari shiga ciki, k’ofar da akayi da siraren k’arafu na ya tura ya shiga yana ta kalle kalle da son hango mutum, saida ya kai tsakiyar lambun ya ji motsi ta gefensa, waiwayawa yayi hakan yasa shi ganin mutum tsaye ya d’ana bindigarsa a kan shi yayi shirin kare kansa.
Gyara tsayuwa Haman yayi ya fuskanci mutumin ya d’aga hannayenshi sama yace “Kwantar da hankalinki, ban zo nan dan na cutar da kai ba, ni ba mugu bane.”
Saida ya sake saitashi da bakin bindigar yace “Ta ya zan yarda da kai? Waye kai ? Kuma me ya kawoka sansani na?”
Hannu d’aya Haman yasa aljihu ya fito da bajon shi ya nuna masa yace “Ni sunana Haman Bahar, jami’in bincike ne na farin kaya, na rok’eka ka tsaya muyi magana.”
Kallon tuhuma ya masa yzce “Na kasa yarda ba cutar da ni za ka yi ba.”
Cikin ankarewa Haman ya zura hannunshi bayan rigarshi a k’ugunshi ya ciro bindigarshi mai lasisi ya jefa a k’asa kusan k’afafun mutumin yace “Wannan shi ne, na rok’eka ka saurare ni, na zo ne muyi magana akan b’atan yar sarki Musail, an tabbatar mana da kai ne bafaden da kasan jakadiyar sarauniya Juman, dan ku ne masu gadin bakin k’ofar shiga masarautar kai da mijin ta mai sunan Utais.”
Sak’e yayi tare da sauke bindigar yayi k’asa da ita, ba tare daya daina tsareshi da ido ba yace” Me kake son sani daga gareni?”
Advertisements
Gyara tsayuwa ya sake yi yana sakin numfashi yace” Kai ne mutumin da ka san mutanen nan guda biyu, sannan daga majiya mai k’arfi kai ma nemanka akayi aka rasa shekara d’aya da b’atan gimbiya Zafeera, dalilin b’acewarka nale son sani, da kuma inda zan samu Habbee da Utais.”
Wani d’an murmushi yayi tare da juyawa yana tafiya yace” Tambayarka ta d’aya kam zan amsa, amma ta biyun ka manta da ita.”
Da sauri ya bi bayanshi tare da sunkuyawa ya d’auki bindigarshi ya mayar a mazauninta yana fad’in” Me yasa ka ce haka?”
Bai amsa mishi ba har saida suka shiga wani falo, wuri ya nunawa Haman ya zauna yana k’arewa d’akin kallo, tsaye yayi a kan shi yace” Shayi zan kawo maka ko ruwa?”
Girgiza kai yayi yace” Ko d’aya, nagode.”
D’aga kafad’a yayi irin oho d’in nan sannan ya zauna kujerar dake fuskantar Haman d’in, k’urawa juna ido sukayi kafin yace” Ina jinka.”
Gyara zama Haman yayi yace” Me yasa ka bar masarautar Khazira?”
Cikin sakin fuska yace” Dalili ne mai k’arfi, umarta ta akayi da na bar k’asar, ba ni ne bari dan ina so ba.”
Da mamaki yace” Waye ya umarceka?”
Ba tare da kwalo kwalo ba yace” Sarauniya Juman ce.”
Wani sabon mamakin ne ya kama shi yace” Sarauniya Juman kuma? Amma me yasa?”
Gyara zama yayi ya sauke ajiyar zuciya yace” A duk masarautar ni kad’ai na iya yaren k’asar Azarbhaijan, hakan yasa ni da su Habbee muke hira a tsakaninmu dan su ‘yan k’asar ne.”
Da matsanancin mamaki Haman yace” Akan haka ta umarceka kayi nesa da masarauta?”
Jinjina kai yayi alamar e, ba tare daya shanye mamakin ba yace” In hakane kuwa kar ka ce min sarauniya na da hannu a b’atan yarta?”
Wata yar dariya yayi sannan yace “Ka canka daidai.”
Girgiza kai Haman yayi yace “Amma ta ya ta iya jurewa haka? Me yasa ma tayi hakan?”
Cikin rashin sani yace “Wannan ne kuma ban sani ba, abinda na sani kawai shi ne ta kub’utar da ‘yarta.”
Jinjina kai Haman yayi yace “Na ji wannan, yanzu zaka taimaka min ka fad’a min inda zan samu su Habbee?”
Girgiza kai yayi yace “Kamar yanda na fad’a maka ka manta da tambayar nan, dan ni ma ban sani ba.”
Murmushi Haman yayi yace “Kaga, ka daure ka fad’a min, idan ma wani abu kake so ni ka fad’a min zan baka, binciken nan yana da mahimlanci a gareni.”
Mik’ewa yayi tsaye yace “Na fad’a maka ni ban san inda suke ba, sak’o kawai nake isar wa da sarauniya.”
Shi ma tashi yayi tsaye yana sauke numfashi yace “Amma ta ya kake isar mata da sak’on?”
Ajiyar zuciya mutumin ya sauke kafin yace “Kana neman k’ureni ka sa na karya alk’awarin dana d’auka.”
Cikin rarrashi Haman yace “Kai kanka nasan za kayi farin ciki a ce yau farin cikin sarauniyarka ya dawo ta dalilinka, gimbiya Zafeera yarinya ce da muka fuskanci girman lamarinta, dalilin hakan rayuwarta ta shiga cikin had’ari mai girman gaske, muna son sani wani abu a kan ta dan bata kariya ne daga masu son cutar da ita.”
Jim yayi yana kallon Haman na tsawon dak’ik’u, muskutawa yayi yace” Na yarda da kai yallab’ai, ba dan komai ba sai dan abinda ka fad’a gaskiya ne cewa rayuwar gimbiya Zafeera na cikin had’ari.”
Numfashi ya sauke kafin yace” Zaka samu cikakkun bayanai inda suke a wajen wata tsohuwa dake k’auyen Larhjadin. ”
Cike da zumudi Haman yace” Me ye sunan tsohuwar? A wane gari ne?”
A nutse yace” Ruman, k’auyen *Tankara*.” (Mai Dambu ta mu ina godiya da wannan kyautar, Allah bar zumunci)
Hannu ya mik’a masa cike da jin dad’i yace “Nagode sosai,na ji dad’in had’uwa da kai.”
Jinjina kai yayi shi ma yace “Ni ma haka, fatan nasara.”
Murmushi yayi sannan suka saki hannun juna ya fita a lambun gaba d’aya, a hanyarshi ta zuwa k’auyen Tankara ya kira lambar Umad, dan yayi niyya yau zuwa gobe sai ya samo bakin zaren nan, dan sun jima suna doguwar tafiya saboda yarinyar nan, abinda ya fi basu wahala kuwa shi ne kafin su samu wanda zai iya basu bayanai a kan ta, da k’yar suka samu wata baiwa da sarki Musail ya ma ciki, amma saiya koreta saboda a lokacin yana cikin tashin hankalin neman Zafeera, ita kuma haushin yanda ya koreta bai sakata a layin k’wark’wararsa ba ma bare ta zama matarsa yasa ta fad’a musu bafaden da taji suna wani yare da su Habbee.
*Umad* na tsaka da jinjina k’arfin halin Ayam na marin da ta wa Zafreen ya ji k’arar wayarsa, da sauri ya d’aga ya d’ora a kunne amma bai ce komai ba, Haman da yasan komai ne ya fara fad’in “Kana ji?”
“Umm.” Ya fad’a a k’asan mak’oshi, d’orawa da “Na samu mutumin nan Umad, ya ban adreshin d’aya mutumin kuma na sameshi.”
A zabure ya tashi tsaye yace “To ya kukayi? Me ya ce?”
A tsanake yace “Ya fad’a min komai, yanzu haka zan je k’auyen Tankara ne.”
Da mamaki Umad yace “Tankara kuma?”
“E.” Ya fad’a kai tsaye, da alamar tambaya yace “To amma me yasa?”
Kamar yan1 gabanshi ya shiga girgiza kai yana fad’in “Umad lamarin nan fa ya wuce yanda kake tunaninshi, wai ma kasan da sarauniya Juman ita ce ta sa aka d’auke yarinyar dan ta kub’utar da ita?”
Da mad’aukakin mamaki Umad ya shiga zagayen d’akin hannunshi akan k’ugunshi yace “Idan na fahimceka sarauniya Juman ita ta umarci jakadiyarta Habbee da mijinta da su gudu da yarinyar, haka kake nufi?”
Jinjina kai yayi yace “Tabbas kuwa hakane.”
Wani shak’iyin murmushi Umad yayi sannan yace “Hummm! Sannu sannu dai, komai ya kusa fitowa fili.”
Zura hannunshi yayi aljihu yana takawa a hankali yace “Shikenan Haman, ka ci gaba da bincika mana komai a tsanake, Allah ya kiyaye ka.”
Murmushi yayi yace “Nagode, sai na kiraka.” Lumshe matsakaitan idonshi yayi alamar to kamar suna kallon juna.
*Khazira*
Hankali tashe babban malamin ya iso fada, sai ga sarki Musail na ta kewayar d’akin ya cire babbar rigarshi ya aje sai zufa yake, cikin tsawa da hargagi ya kalli malamin yace “Babban malami ta ci amanata, Juman ta ha’ince ni, shin soyayyar dana nuna mata ce ta gagara? Ko kuma butulci ne irin na mace?”
Jim ya d’anyi kamar zai ba wani damar fad’an wani abu, sai kuma yay saurin fad’in “Yanzu me ye abun yi baban malami? Ya zanyi na samota ta dawo gareni? Ina so na kamata da hannaye na, Dhurani bana so na mutu yanzu.”
Ya k’arashe maganar yana d’aga murya, cikin rarraba ido Dhurani yace “Sarki na, wannan ai abu ne mai sauk’i, mu takura gimbiyar mu har sai ta fad’a mana.”
Khatar ne yayi saurin fad’in “Da zata fad’a ai da ta fad’a, shekaru ashrin fa muka d’auka muna bilinbituwar nemanta, a gaban idonta muke yi da me ta tab’a taimaka mana?”
Sarkin yak’i Adah ne ya d’an jinjina kai duk da ba’a buk’ace shi ba yace “Gaskiya ne, amma ko bata fad’a da bakinta ba mu zamu nemota.”
Kallonshi sarki Musail yayi yace “Adah bana son wasa, wane irin nema ne baku mata ba ? Tun kana da k’ruciya kake yawon nemanta, sai yanzu ne zaka ganta?”
Sunkuyar da kai yayi yace “Sarki na, sa’ilin da zamu kai sarauniya kurkukun sabah sun yi wani yare ita da d’aya daga cikin bayinka, bana tamtama cewa maganar da sukayi ta shafi gimbiya Zafeera.”
Da saurin bala’i sarki Musail ya tunkareshi yace “Wanene shi? Me suka tattauna?”
Girgiza kai yayi yace “Ban sani ba ya shugabana, dan kafin ta masa magana saida ta canza harshe.”
A bala’in tsawace yace “Waye shi a gidan nan, je ka kawo min shi nan.”
Sunkuyawa yayi alamar amsawa sannan ya juya cikin takon k’arfi yaf fita a falon, bai d’auki lokaci ba ya dawo waccen bafaden na bayanshi, gefe sarki yak’i Adah ya tsaya shi kuma ya zube har k’asa yana gaishesu, saidai a zahirinshi da bad’ini hankalinsa a tashe yake, ba ka da abun zargi ma ka ji tsoron amsa kiran sarki Musail bare kuma shi da yake ji a jikinshi asirinsa ne ya tonu.
Cikin daka tsawa sarkin yak’i Adah yace “Kai k’ask’antaccen bawa, sarki yana so ya ji abinda kuka tattauna tsakaninka da sarauniya Juman?”
D’aga kai yayi ya kali sarkin yak’i jikinshi na makyarkyata, kame-kame ya fara ya rasa me zai ce da shi, a sukwane sarki Musail yayi kan shi, kafin ka ce me ya saka k’afa ya hankad’ashi ya fadi kwance, kafin ya tashi yasa k’afar ya take masa k’irji, cikin k’araji yana zazzaro ido yace “Zaka fad’a min ko sai na kasheka a banza? Ka sani duk wanda yace zai shiga tsakani na da cikar burina kamar wanda zai taimakawa mak’iyana kyautar takobi ne dan yak’ata, dan haka ba zan bar shi a raye ba, yanzu fad’a min me ta fad’a maka?”
Cikin tashin hankali da tsananin tsoro yace” Sarki na, shugaba na ka min rai karka kasheni, ta ce ko ta halin yaya na isar da sak’onta, na fad’a mata ta ninka saka ido akan gimbiya.”
A tsawace ya sake fad’in” Wacece? Kuma a ina take?”
Cikin rawar jiki yace” Wata tsohuwa ce, a k’auyen Tankara.”
“Me sunanta?” Dhurani ya tambaya daga gefenshi, cikin rawar leb’e yace “Ruman, Ruman ne.”
K’atuwar takobin dake k’ugun sarkin yak’i Adah ya jawo, kafin kowa ya ankara kawai ya sokawa bafaden nan ita a tsakiyar ak’ogwaronsa ta hudashi zuwa wuya, wani huci ya shiga saukewa ya mik’awa Adah wuk’ar yana fad’in “Duk wanda ya yi k’ok’arin hanani kasheta to shi ma kasheshi zan yi, sarkin yak’i.”
Da sauri Adah ya amsa yana rusunawa, juya baya yayi yace “Ka d’ebi wasu daga cikin mayak’anka ku nufi Tankara, idan tana nan ku taho da ita, idan kuma hakan ya gagara ku sanar da ni, ni zan je har inda take sannan na kasheta da hannu na.”
Amsawa yayi da “Angama Ranka shi dad’e.” Kafin ya kama hannayen gawar nan ya jashi k’iiiii har ya fice da shi a falon.
*Larhjadin*
Ba wani yammaci bane sosai, amma dake makarantar akwai wadatar shuke shuke sai tayi luf sai iska mai sanyi dake kad’awa, duka d’aliban mata suna tsatsaye bakin mota inda dreban ke jiransu, suna cikin shiga ta kakin ma’aikatan gandun daji, riga da wando kalar shud’i da babu kwalliya, saidai daga yanayin d’inkin da wasu ado da akayi ga rigar zai shaida maka masu tsaron k’asarsu ne, bak’ak’en huluna ne a kan su sun daidaita musu zama cikin k’warewa, ga kuma takalminsu bak’ak’e k’afa ciki sai k’yalli suke sun d’auresu tamau da d’amara.
Gyara tsayuwarta tayi tana murgud’a baki tace “Wai malamin nan bai san lokutan karatu dana hutu bane? Ya zai shanya mu a nan?”
Sergent d’in colonel ne ya tsaya gabansu cikin d’aga murya yace “Ayam Utais, yallab’ai canal (colonel) na san ganinki yanzu a ofishinshi.”
Waina idonta tayi ta kalli Deeyam da ita ma ke kallonta tace “Wai ni sai yaushe ne canal d’in nan zai barni na huta?”
Murmushi Deeyam tayi tana rik’e d’amarar k’ugunta a hannu tace “Ranar da ke ma kika barshi ya huta, ba ke kullum ‘yar masifa ba ce.”
Turo baki tayi gaba alamar rashin jin dad’i sannan ta nufi hanyar tafiya tana fad’in “Sai na je kuma yayi ta sadda kai k’asa kamar ya ga gyatumarshi.”
Yanda aka mata d’inkin daidai da zubin hallitarta yasa kayan suka karb’eta da kyau, duk da bata da wasu mazaunai na a zo a gani, amma dake ta d’aure da zanzaro sai hakan ya basu damar juyawa.
Motocin data gani da suka amsa sunansu masu bala’in kyau da kuma shek’i yasa ta k’ura musu ido a ranta ta ayyana “Ko dai bak’i a ka yi?”
Suna kai wa bakin ofishin ya ja ya tsaya ya nuna matata shiga, kallon shi tayi t tab’e baki sannan ta kama hannun k’ofar ta murd’a, k’afa d’aya ta fara zurawa ta shiga a matuk’ar nutsuwa da kuma wani irin kwarjini da izza, tana k’arasa shiga kamar dai mutanen ciki ita ma sai ta zuba idonta tana k’are musu kallo.
Canal dake kujerarshi ya had’e hannaye wuri d’aya sai rarraba ido yake, amma tana shigowa ya mayar da hannayenshi k’asan teburin ya koma kallon takardun gabanshi kamar wanda ya ga aljana. Waziri Khatar kuma na kujerar dake fuskantar ta canal d’in fuskarshi a matuk’ar had’e yanda zta gigita mai kallonta, ga shigar da yayi ta alfarma ita kad’ai zata sa ka rusuna mishi ka d’auka sarkin ne da kanshi.
Sai Zafreen dake tsaye bayan wazirin ta rumgume hannayenta ta k’urawa Aya d’in ido. Sai kuma wanda zata iya cewa shi bata san me ya kawoshi nan ba, dan in wannan yana zaune ne saboda marin da ta wa Zafreen, to shi kuma fa? Yallab’ai Umad kenan, gashi dai cikin kakinshi a shirye tsaf, amma kuma ya barsu suna jiranshi har yanzu gashi za’a zo a nemi b’ata mata rai.
Yanda ta tsaya gaban tebur d’in yasa canal d’aga kai ya kalleta, suna had’a ido kawai sai ya ga kamar hararanshi ma take, da sauri ya mayar da kanshi ga d’aya daga cikin fadawa biyun da Khatar ya shigo da su yace “Rufe k’ofa.”
A ladabce bafaden ya rufe k’ofar a lokacin ta juya ta kallesu sannan kuma tasan da zamansu, maida kallonta tayi ga canal d’in tace “Yallab’ai ka ce kana son gani na.”
D’aga kai yayi ya kalli fuskarta, amma abinda Umad dake zaune yana tsare kowa da ido ya lura da shi shine yanda yake ta yawo da idon na shi ya kasa tsayar dasu a kan fuskarta bare ya kalli idonta, hakan yasa shi dasa alamar tambaya aka wannan lamari.
Cikin taushin murya yace “Ayam, me ye dalilin da yasa kika mari gimbiya Zafreen? Shin ban fad’a miki ki fita a sabgarta ba?”
Gyara tsayuwarta tayi ta juya ta kalli Zafreen d’in, sai kuma ta kalli waziri daya cika fam yana jiran fashewa, tab’e baki tayi ta kalli canal tace “Tun ranar ai na fita a harkarta, ita ce ta sake shiga hurumi na.”
Wata irin tsawa ya daka mata tare da buga tebur din ya mik’e tsaye yana fad’in “Ke d’in banza, wacece ke da zaki ja da ita? Kinsan matsayinta a makarantar nan kuwa? To ko yanzu ta so z…”
A hassale ta kalleshi gaba da gaba ta zazzaro idon ta wanda launin shud’i yayi wani kore-kore ga mai kallonsu, cikin tsiwa da fad’a tace “Waye kai da zaka min tsawa? Uba na ne kai ? Na sanka ne? Ka zo d’aukar mata fansa ne? To ina jira kayi yanda zakayi da ni.”
Sake k’ura masa ido tayi ta nunashi da yatsa manuniya tace “Malam murya k’asa, ni ba kowa bace amma haka kawai nake jin na tsani a d’aga min murya, kuma a jinina nake jin kamar ina da izzar da zan hukunta duk wanda ya min hakan cikin d’anyan kai.”
Juyawa tayi ga canal, tuni ya gyara zamanshi yana ta k’yak’yabta ido, tabbas da yana da addinin musulunci a lokacin daya shiga karanto addu’ar tsari da shed’anu, sam bai yarda da Ayam dan lamarinta tsoro yake bashi, shi fa babu kamar ma yanda jikinshi ke d’aukar b’ari idan ya hangeta kawai, har ya kan tambayi kan shi k’awayenta da sauran mutane basa jin hakane ? Sai kuma ya ba kanshi amsa watak’ila dan sun saba da ita ne shiyasa, dan sun fad’a mishi tun suna yara suke tare tun a makarantar *Ansawwd* (ma’ana *inganci*).
A sanyaye kamar ba ita ba tayi kalar tausayi tace “Canal yarinyar nan fa marin k’awata tayi, kuma ka sani kai ma bana son a tab’a min k’awayena, to me yasa zan k’yaleta?”
Cikin sub’utar baki yace “Gaskiya ne, na sani Ayam, yanzu kiyi hak’uri ki je na jiranki zaku tafi jeji.”
Wani k’ayataccen murmushi ta saki tace “Shukran.”
Sakin baki yayi a ranshi yace “Yau ma wani yaren?”
Juyawa tayi cikin takon k’arfi da salo ta fita a ofishin babu wanda yayi yunk’urin hanata, Umad dake zaune mik’ewa yayi ya sarawa canal d’in sannan yace “Yallab’ai da izininka zan tafi.”
Da hannu ya nuna masa k’ofa alamar ya tafi d’aya hannunshi kuma na share gumi da yayi, saida Umad ya fita Zafreen ta girgiza kan ta ta dawo hayyacinta, rarako idonta tayi tace “Kutumar can, wacece ita?”
Khatar daya kasa anfanuwa tunda ta shiga kora masa bayani ko k’yabtawa bai yi sai yanzu, cikin fitar hayyaci da rashin sanin me ya fad’a yace “Ta musamman.”
“Me?” Zafreen ta fad’a a tsiwace, kamar mari ta gaura masa haka ya zabura ya juya ya kalli canal, cikin masifa ya shiga fad’in “Dama haka kake mata kashedin? Wai wannan wace yarinya c da kai kan ka ke tsoron had’a ido da ita? Me ta taka a k’asar? Dan gwamnati ta d’auki nauyin karatun ta ba shi ke nufin zata taka kowa ba, ka fad’a min wacece ita?”
Tsura masa ido canal yayi yace “Wacece ita?”
“E, wacece ita?” Ya fad’a a zafafe, numfashi ya sauke sannan yace ” *Abinda idonka ya nuna maka*, ita d’in ita ce, bayan haka bansan komai ba.”
Tsaki Khatar ya ja tare da juyawa ya kalli Zafreen yace “Zo muje gimbiya.”
Da sauri suka fice a ofishin canal na kallonsu, saida suka fita har da bayinsu shi ma ya ja tsakin yace “Aikin banza, naga ma kai ka fini firgita da lamarinta tunda suman tsaye ka yi, can kuje ku k’arata da matsalarku da ita ni ku daina sakani, tunaninta kad’ai hawan jini yake tayar min.”
*Ayam* kam na fitowa ta kawo daf da motocin da Khatar ya zo ta tsinkayi muryar Umad yace” Ke.”
Yi tayi kamar bata ji ba ta ci gaba da tafiya, sake fad’in yayi” Ke.”
Nan ma ko waiwaye bare hasa ran zata tsaya, saida ya bushi iska ya daddage yayi ta maza yace” Ayam.”
Cak ta tsaya tare da juyowa tana murmushi tace” Na’am yallab’ai.”
Gyara tsayuwarta tayi saida ya k’araso yana d’an cije leb’e da mamakin kenan ta ji banza ne ta masa? Tsareta yayi da ido kamar mai son gano wani abu a fuskarta sannan yace” Me yasa kika wa babban mutum fitsara? Dama rashin kunyarki ta kai haka? Sannan me yasa kika mareta?”
Ajiyar zuciya ta sauke irin ka dameni d’in nan sannan ita ma ta zuba idonta a na shi a yaren Italy tace”…
*Saura k’iris a rufe free page, hanzarta ki biya na ki, farashin mai sauk’i ne.*
*Alhamdulillah*
GIPHY App Key not set. Please check settings