Zee Baby Book 1 Page 12

Advertisement

*πŸ‘‰πŸ»12*

….ko kallona baiba yaja motar bakin get ya tsaya mai gadi ya bude masa ya fice nutsuwata na tataro na cire tsoro cikin tsiwa nace” malam meye hadinka dani da zaka wani daukoni bakace kowa yayi rayuwarsaba na fita sabgarka to meye hadinka dani kuma inane zaka kaini ko kawai jaraba son ayi fada to ni yau banayi zaman lafiya nakeso asaukeni ko ci kanki bai ceba ya harba motar kan titi yana tukinsa cikin nutsuwa wayarsa ta dauki ringing hannusa daya ya tura cikin kwantacciyar sumar kansa yana shafawa bai daga kiranba saida ya katse aka sake ya dauki wayar yai picking ya Kara akunne cikin amon muryashi mai dadin sauraro yace”hello ya akayi ne? OK ina saman hanya ya tsinke kiran yaci gaba da driving dinsa tsaki naja” aikin banza wlh idan nutum yaci zalina Allah yana ganinsa baima San tanayi ba har suka isa hospital honr yayi aka bude masa babban get ya cinno hancin motar cikin asibitin parking space ya shigar da motar yai parking ” wai malam lafiya kakawoni mustashfar ko wata cutarwar zakamun wayoyinsa ya kwashe ya fito daga cikin motar bude mata motar yai fuskarsa babu alamun rahma ya kalleta bai maganaba ya mata nuni ta fito duk taji tsoro ta dake Dan yau taci alwashin bazata bari ya zalumcetaba irin wancan Karo cike da rashin kunya tace” baza’a fitaba ko Ana Dole bai maganaba Dan lokaci zata bata masa ya duko ya janyo hannuta da karfi ya fizgota waje buge hannu tayi ” wlh malam ka kiyayi tabamun jiki ta fada cikin fitsara motar ya rufe dan yasan tsiwar karfin hali take zuciyarta fal tsoro gaba yasata

sai tsoki take masa bai dai kulataba Dan yasan daga yau bazata iya masa abun da take masaba haka suka ratso tsakiyar hospital d’in kowa sai kallinsu yake cike da shawarsu dan sunyi mugun dacewa ga tsantsar kamar da sukeyi saide ita zaka gane balarabiya ce duk fatarta tasa duhu ko ina sai gashesa akeyi amatsayinsa na babban doctor hannu yake daga musu yana wucewa itako sai harare harare take Office d’insa ya saka key ya bude har an gyara tsaf sai kamshi yakeyi kin shigowa tayi hankadata yayi da karfi saida ta fadi ya murza key bai kalli inda take ” Allah ya isa mugun banza kawai meye hadinka dani murmushin gefen baki yai yaje ya zauna kan lumtsumemiyar kujeran da ke gaban katon table din mai cike da takardu laptop ya kunna yakira waya banji me yaceba ya kashe takaici ya cikani ganin ya maidanin banza na Mike tsaye ina kallonsa ” idan kai ka haihu ka budemun kofa na fice waya ya dauka ya danna wata number bugo daya aka daga ” murmushi yai morning my sweet baby ya gida kansa ya dafe ” oh wlh na manta sorry bari zan biyo idan na taso daga gun aiki OK bye zan kiraki da rana love you too ya fada yana murmushi ya tsinke kiran ko kallo bai ishanba gu na nema na zauna naga iya gudunsa Dan yau nayi alkawalin kirta masa rashin mutumci Nima knocking din kofar akayi ya Mike ya nufo kofar cikin takunsa na kasaita da isa farin gilashin yamasa kyau cikin isa yake takunsa kana ganinsa kasan karkarfan Namijine tsayaiye ko kallo bata ishesaba hararasa tayi baima san tanayi ba tsaki taja” aikin banza kawai mai kyan Dan miciji yajita sairai amma ko kallonta baiba ya saka key ya bude kofar hamzane dauke da tire kayan breakfast ” good morning Yallabai ” morning hamza ykk?? ” Alhmdllh doctor ya bashi hanya ya shigo yaje ya ajiye ya gaishe da zee baby yai kin amsawa tayi tabisa da harara har ya fice kofar ya rufe ya dawo ya zauna cup din tea ya dauka yanasha anutse mik’ewa tayi ta nufi gunsa Dan yunwa takeji ” malam likita ni yunwa nakeji banci komaiba ganin bazai kalletaba

yasa ta saka hannu ta dauki plate mai soyayen dankalin turawa da kwai da cinyar kaza asoye ta koma gun zamanta abayar jikinta tacire ta ajiye tayi zamanta da dogon wando da guntuwar rigarta gashinta ya sabka har gadon bayanta rabi ya rufe mata fuska anutse yakeci har ya gama hamdala yai ya Mike yaje toilet ya wanko bakinsa da hannusa danna wata yar na’ura yayi ba’afi muntuna biyar ba aka fara shigowa ganin Dr wata latijuwa ta fara shigowa acikin girmamawa zee baby ta gaisheta ita ya fara dubawa nabiyu ko namijine saurayi Wanda zuciyarsa dab take da bugawa sosai Dr Sardauna yai masa fada ya rubuta masa maguguna yace zai kwantar dashi har kwana biyu ta ukku ce da ta shigo wata zankadediyar budurwace asuma ke damunta Dr Sardauna na tsaka da dubata zee takeson mata rashin kunya babu gaira babu dalili ta fara zaginta ganin basu kulata ba ta iskosu tayi tsaye kansu fur ta hanashi yaba yarinyar kulawa saboda bayason surutu Dole ya dago ransa abace” ke matsa kiban guri jikinsa ta matso ta rumgumeshi ta fara kukan shagwaba ” wlh Dr bazaka dubata ba danme zaka rika tabata nadamar kawota hospital yai amma da ya tuna zai kunsa mata bakin cikin da bazata iya mantashi ba wuyanta ya damko ya kifa mata Mari ya hankadata wani daki ya murza key yaci gaba da aikinsa saida ya duba mutum sama da ashirin tun tana ihu da buga kofa har tagaji ta bari sai karfe sha biyu ya samu ya huta su Daddy sunzo amma yace ya mata magani Allura bacci ta awa biyar yamata bazasu samu ganintaba Mahabeer sawunsa biyu Dr Sardauna yace sai yamma zata farka Dole ya hakura ya koma gun aiki, Dr Sardauna ya shiga duba marasa lafiyar dasuke kwance a asibitin duk da yasa an dubasu amma yabi su daya bayan daya yana dubasu cikin fara’a yake duba kowa yana kara musu kwarin gwiwa hakan nama marasa lafiyan dadi ba kadan ba

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

karfe daya da rabi ya fito daga masallaci yin sallah Office ya bude ya shiga ya dauki abayarta ya bude ya wurga mata ” maza tashi kiyi sallah kafin watan cin ubanki ya kama yanaji ta rama k’asa k’asa yana ciza bakinsa ya jinjina kai fitowa tayi taje tayi Alwalla ta shimfida dadduma sai Allah ya isa take masa” kuma yanzu zanyi Addu’ Allah ya hadaka da cutar dan kanoma ka kasa zaune ka kasa tsaye ko kallo bata isheshiba tsadaddan agogon hannusa ya kalla saura minti ashirin yashiga tiyata wacce itace ta hanashi cin uwar zee baby soyake sai ya fito bayan mintina goma akayi knocking din kofar ya bada izinin shigowa Dr Ruma ce ta shigo da sallama sai wani lankwasa take amma cikin taitayinta dan tasan halin Dr Sardauna ” doctor mun gama shiryama komai lokaci yayi Dr Nabil yace na kiraka ka fara fuskarsa ahad’e yace ” Ok bai sake maganaba ta juya zata tafi ” kallon banza zee tama Ruma ” ke bazawara wlh kunji dai kunya ke yanzu haka kike yawon tsakiyar maza idan ba salon iskanciba da tallaar jiki kalli wani breast dinki duk ya saki sai kace mai shayarwa koda yake bazawarce ai dukda hausarta bawai ras take yintaba amma Ruma ta fahimta idanu Dr Sardauna ya zaro kallonta ruma tayi dan batason raini ” ke yarinya shiga taitaiyinki kowama dan iskane zan tataka ki anan ” kut wa zaki taka ki taka uwarki dai shegiya mai kirar agwagwa gadan gadan Ruma ta nufo zee baby wacce take zaune ko motsi ba taiba dan ta shiryawa ruma yada zata kadata Dr Sardauna yace” Ruma jeki wlh batada hankaline maganine aka kawota batasan me take fadiba jin yada Dr yakirata anutse abunda bai taba mata ta tsaya ta juyo tana kallonsa fuskarta dauke da murmushi sai wani fari take da idanu” ok Dr babu damuwa tunda batada hankali amma da na nuna mata iyakarta ai bata rufe bakiba zee baby ta watsa mata mari ta makaleta sai yakushinta take da cizo duk inda tabi ta kare zee ta tare karfi Ruma tasa saboda girmansu ba dayaba zee siririya ce Ruma akoshe take babbar macace tana dab da murkusheta zata danne zee aikuwa tayi sauri ta janyo kafar Ruma sai ji kake dim Ruma ta fadi kasa wanwar samanta zee ta Haye idanu Dr Sardauna ya zaro waje ya kauda kansa dan Ruma kusan tsirara take siket din ya tatare mik’ewa yayi cikin sauri dan sai cizonta take itako sai jibgar zee baby takeyi babuji babu gani yazo ya dauke zee baby cak daga saman ruma sai wutsul wutsul take tana dukansa rumgumeta yayi gam ya matseta ya ruko hannnuta da take dukansa yana murzawa ahankali yana buga bayanta sai ashar take durawa Ruma ganshinta ya tatara mata da ya rufe mata fuska ya kalleta “wlh idan bakimun shiruba zaki sani tantiriya fitsarariya kawai. shiru tayi ta tura kanta kirjinsa tana gunguni ya kalli Ruma ” dr yi hakuri jeki zanci ubanta dakyau wlh sai na rama miki ai na gayamiki mahukaciya ce mik’ewa tayi cike da kunya ta fice amma azahiri dukan da tama zee yafi wanda zee baby ta mata ita dauriya tayi

Cike da mugunta ya yaketa daga tsaye ta fadi” Ashhhh Allah ya isa mugu ban yafeba bai mata maganaba dan bashida lokaci da harara ta bishi ” wlh indai haka zakayi rawu ka hadu da wahala kwarton banza na mata ko ina kana yawo da mata kunji kunya kai dasu ransa yayi wani irin baci amma bai yi magana ba ya cire agogon hannusa da zobunan sa har biyu Wanda fadar tsadarsu bata lokacine ya ajiye ya dauki Rigar aiki yasaka yanaji tana masa tijara ya fice ya murza mata key daga waje yana Addu’ar Allah karya sa ta masa, wata bannar dakin tiyatar ya shiga, zee jin ya rufeta ta koma ta hau kujerasa ta zauna sai dube dube take taga abin barna tunawa tayi fah dama yana binta bashi kar yaje ya ilatata hakura tayi da barnar tayi zamanta dam tsoro fal zuciyarta don yanzu ma batasan nufinsa ba wayoyinsa ta shiga dubawa dukansu ya kashesu ajiyewa tayi, gilashin sa ta saka ta dauki rigarsa ta sanyi sai futinanan kamshi take rumgume rigar tay akirjinta tana shakar dadadan kamshinsa idanu ta lumshe nan bacci ya dauketa saman kujerasa dama ga gajiyar damben da tayi, karfe biyu da minti talatin da bakwai cif cif Dr Sardauna ya fito daga daga d’akin tiyata ya cire rigar yaba Dr Nabil yana goge zufa ya barsu da sauran aikin yana fitowa suka hadu da Mahabeer ” Dr namu ya babyna?” my bro wlh yanzu na fito daga tiyata kuma yanzuma saura awa biyu ta farka ” ok bari na koma bayan la’asar zan dawo dan Allah ka kulamun da ita kafasan amaryace murmushi Dr Sardauna yai ” sai fa yaune za’a sa muku ranar har tazama Amarya Ok idan ta farka kafin ka dawo zan kulama da ita rumgumeshi Mahabeer yayi yana godiya ya sakeshi” na tafi Daddy yace yana kiranka akashe?” eh da zan shiga tiyata ne na kashesu ya fada yana nufar Office d’insa Mahabeer ya tafi, key ya saka yabude ya shiga ya rufo tana kwance saman kujerasa ta rufo fuskarta da rigarsa bacci take cikin nutsuwa haushine ya turnikeshi duk girman Office din tarasa gun kwanci sai kujerasa da yake zama toilet yashiga yajima sosai kafin ya fito yana murmushi mugunta ya nufi gunta kusanta yaje ya tsaya yana kallonta kirjinta duk awaje tunda ta fitar da abaya lokacin da zasuyi dambe da Ruma daga ita sai yar karmar riga pink colour da wando dogo komai nata awaje surata mai cike da kyawun kallo baki ya tabe k’asa yai da murya zainab yau zaki san kin shiga gonata saida na hadaki da girman Allah karki kuma yarda kishiga sabgata amma kika ki kin sa narasa abubuwa masu mahimmaci awayoyina kinso hadani da macan da nafiso aduniya kin ciramun Suit kala ukku Wanda nafi kauna amma ni zan barmiki dafi mai zafi shegiya mai ruwan karuwai dubi yada take shegiya mai ruwan yar tsana wlh sai nabarki da dafi mai zafi cikin zuciyarki daga yau zamuyi hannu Riga dake figigiya kawai ficiciya dake sai fitsara da fitina kusanta ya matso ya zauna ya janye rigarsa idanu ya zaro ganin gilashinsa ya cireshi rigarta da rabin kirjinta ke waje ya hannu ya gyara mata bakinsa yakai kusan kunneta ya kirata” zee baby Oya bude idanunki zan nuna miki banbancin fari da baki dayake bata nauyin bacci idan ba shaye shaye tayi ba idanunta ta bude ahankali jin ni’imataccen kamshinsa kusanta yasa ta dago idanu hudu sukayi dashi zabura tayi da sauri ta zauna gira ya daga mata yana murmushi ” barka da warhaka tantiriya tambayoyi zanyi miki guda ukku daya bayan daya ki amsamun kafin ki amshi hukunci da zai zauna miki azuciya ya hanaki sukuni cikin tsiwa tace ” to matsa na, sabkar maka daga kujeraka kokarin sauka take ya sanya tattausan hannuwansa duka biyu ya maidata ya zaunar buge masa hannu tayi mari ya zabga mata ya tsareta da shanyayun idanusa fuskarsa babu wasa” dan ubanki ni sa’ankine zaki rika bugemun hannu me zanji awanan busashan jikin naki Oya dago idanunki ki kalleni ya fada yana kai hannusa wuyanta yana shafawa ya riko hannuta guda yana murzawa cikin wani irin salo yar naji gashin jikina na mik’ewa wasu kwayoyi nake gani cikin fitunanun idanunsa ban gama dawowa daga tunani ba naji amon murasaki mai fitar da amon dadi yanace min” inaso ki amsamun tambaya ta farko kafin tabiyu da ta uku suzo daga nan sai hukunci da zai tarwatsa kwanyarki yaki fita azuciyarki meye dalilinki na fasamun wayoyi da ciciramun kayan jiki da farfasamun turarukana da maiyuka yada yake mun tambayoyin cikin nutsuwa tamkar mai mai mun rada yana shafar wuyana da fuskata da yake ga hannuna da yake murzawa naji jikina ya fara saki ga kasala ta sabko mun sanyi ya fara ratsani mafaka nake nema kamshinsa ya adabeni ga ya tsare ni da rikitatun idanunsa yace karna kuskura na dauke idanuna daga kallonsa abinda yafi rudar da ni Kenan sai lumshe idanu nake nayi kasa da kaina tsawa ya buga mun da karfin gaske saida hantar cikina ta kada na dago na kalleshi” dan ubanki Oya bani Amsa duk da naji tsoransa mutika ga yanayin da na shiga amma na dake na dauke idanunta daga kallonsa muryata ta fara canzawa nace” Dr Sardauna bari kaji dalili………..

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like
KALLABI
Read More

KALLABI 20

Advertisement BABI NA ASHIRIN Da wani irin tashin hankali yake kwana yake tashi, bawai dan bai da karfin…
INAYAH
Read More

INAYAH 50

Advertisement 50_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Ringing biyu wayar tayi anty Hafsat ta dauka tana cewa” Dr Inayah majeed Yar gatan…
Read More

TARTSATSI 73

Advertisement *Page 73*     *********************   Sadauki yana kashe wayar, ya kalleta yana dariya yace:   “Waike…
Read More

TARTSATSI 17

Advertisement *Page 17*     ********************     Ana cikin haka, saiga Abba ya dawo, Hafsa ta yi…