Advertisement
*Free Page 3*
….nutsuwa ya sakama kansa ya qaqaro murmushi yana kallonta ya janyeta daga jikinsa ya kama hannuta suka nufi inda ta yasar da Abbayar ya sunkuya ya dauka haka kawai yakejin ciwon kallon da Jamal yake mata saka mata Abbayar yai suka dawo saman kujere. kusansa ta zauna tana murmushi zata kwanta jikinsa ya kiya ya kalleta da harshan turanci yace” kanwata ykk ina kika shiga har tsawon kwana biyu? hannusa ta rike ta fara magana da Hausarta babu wani kwarewa ” Ahukhuya banason Nigeria na gudu gidan abokina Maharaz ya boyeni kwana biyu yana bani kulawa yanzu ina cikin bacci Dan buro ubansa yazo yana matsani niko na saka masa kunama adiyan kaya na gudo gida ta fada tana wata irin dariya idanuwanta sun kade sunyi jajir alamar bata huceba kunyace ta kamasu ya kalli hannusa da ta rike tana murzawa tana dariya kamar zarara aransa yace ya Allah ka rabanin da wannan shawa Dan naga wannan
Ko munje ba daina tabani zatayi ba naga tabi’artace taba jikin mutum batare da ta kawo komai araiba sakinsa tayi ta Mike ta nufin gun Raiyan ta fada jikinta tana mata magana da larabci tana sakar mata kiss”ummina nayi missing dinki? ta rumgumeta gam tana kukan shagwaba ajiyar zuciya ta sabke tana buga bayanta Alamar lallashi fada ta Shiga mata da nasiya ta lallabata har tayi shiru dagowa tayi ta kalli manal ta harareta” ke Dan uwarki shine zaki wani zo gidanmu ai kinsan bananan salon ku tadawa ummina hankali? dariya manal tayi tana kallon jannat” habibty ummi taje ta dauko mu fah kallin jannat tayi ta mata magana da idanu ta mayar mata mik’ewa tayi daga jikinta ” kuzo muje ciki banyi sallah Azuhur ba tashi sukayi suka bita Mahabeer sosai yakejin sonta cikin ransa kai tsaye tin lokacin da ta rumgumeshi kallon ummi yai
ya fuskan ceta suna magana Jamal ko har yanzu wandonsa baibar motsiba ummi Raiyan tace” Mahabeer ba fah lako lako zakuyi mataba Dole sai kun zage kun zazare mata to bare kai da take ra’ayinka Akan Al’mahadee wato Dr Sardauna don haka ka sa mata idanu sosai don Allah kusa ta dawo cikakiyar mutum ina so naga zaeenaba ta nutsu tazama kamilar mace tayi nisa dani ko hankalina ya kwanta ko iyayena zasu yafemun tunda sun nuna itace basu kauna sunfi son abokan haihuwarta mazan biyu sun rabani dasu sunsaka ‘ya’yan cikina sun gujeni sun tsaneni ni da Zaeenaba saboda ta nuna kauna gareni wlh ina sonta bana son rabuwa da ita amma Dole zan hakura saboda hankalina zai fi kwanciya inaji tsoron ya saka akasheta ta fadi tana goge hawaye Dan tasan tabbas Zee taga kukanta akwai bala’i ajiyar zuciya ya sabke cike da tausayinta ” ummi Raiyan kiyi hakuri
Insha Allahu zata nutsu kuma zaku shirya da mahaifanki wlh Dole yaranki zasu nemeki koba bajima yanzu ma hankaline bai gama ratsasu ba shekara sha bakwai ne fah suke ciki to cikin su Zaeenaba tafisu wayo ita da take mace ajiyar zuciya ta sabke ” to da fatan zaka yimun koda wata daya kafin ku tafi? idanu ya zaro ummi wlh bakin kwana ukku zanyi mukoma aiki sunmun yawa bakiga shi Al’mahadee da bashida dama Dole nine nazo murmushi tayi ” to Allah ya kaiku lfy ya kuma hada fuskokinmu da Alkhairi? ” Ameen ummi suna cikin hira akayi kiran sallah la’asar suka Mike sukaje sukayo Alwalla suka tafi masallacin da yake manne kusa da gidan ummi ta Mike ta shiga tayi sallah zuciyarta babu
Dadi batason rabuwa da yar tata amma da ta tuna rashin jinta gashi batasan me zai faru a gaba ba Dan rashin jin. Yar tata sai ahankali gashi tana Addu’a ba dare ba rana amma baby wani sauyi Zee baby ko suna shiga ta tube kayan jikinta tana rawa da juyi sai ihu takeyi tana dariya daga ita sai shegiyar rigar nan manal tace” my habibty wlh iskanciki gaba yakeyi fah fasa rawar tayi wata shegiyar tsayuwa akarkace tana kallonta shekeke tana murmushi ” bari nayi bautar Allah na gama zanci durin uwarki la’ada waje yasin bathroom ta shige jannat ta kalli manal ” wlh duk kece kika koya mata Hausa da zage zage gashinan akanki take sabkesu wlh dazu naji kunyar abun da ta fadi gaban baki? dariya manal tayi” naji amma shaye shaye wa ya koya mata Dan kaniyar mai da famiki shurba daga cikin toilet ta lailayo zagi ta dirka musu ta ciko Dan bokiti da ruwa ta bude kofar ta watso musu ” sheguna ina jinku fah ta koma taci gaba da wankata ta dauro Alwalla ta fito tabude wardrobe dinta ta bude ta ciro Abbaya ta saka ta nade kanta da mayafin ta shimfida dadduma tayar da sallahr Azuhur, suko kayansu sukacire suka canza da nata suna mata Allah ya isa azuciya tana idarwa taji kiran la’asar ta tashi ta tayar suma Alwalla suka dauro sukayi sallah tana gamawa ta ci uwar kwalliya tasaka wata atamfa bakace mai ratsin fari dinki Riga da siket manal ce me musu dinki tare su ukku kullum to jannat ba’a barinta tana sawa agidansu saide idan ta fito gashinta ta sarce ta daureshi tayi masifar kyau kamar ka saceta sai dai dinkin ya fito da surata yan mazaunanta masu daukar hankali sai motsi suke tana kadasu gangan tana musu gwalo manal tace ” dallah can figigiyar banza nacemiki ki faso gari kizama yar duma duma A dama dake kullum ke kamar kinashan ruwan zafi ta fesa turare
ta kallesu ” wlh manal danayi jiki gwara daga haka nakara tsotsewa Dan uwarki ko ba jiki akwai kayan aiki ta juyo mata yan mazaunanta masu qira coca cola tana fito da harshe waje tana kadawa ihu suka saka ” ku tashi muje parlo ku gaishe da Dan uwana kuma wlh sai kun duka har k’asa fitowa sukayi suna dariya gun mahabeer suka nufa ta zauna kusansa suko suka duka suna masa sannu da zuwa cikin fara’a ya amsa yace” ko zaku bimu Nigeria ne kai suka girgiza suna dariya Zee ta jinginu da jikin Mahabeer ashagwab’e tace” Ahukhuya nima bana zuwa fah ta Kara shigewa jikinsa tana turo baki aransa Adu’a yakeyi Allah yakawo masa dauki son yarinyar yamasa mugun kamu ga wata muguwar shawarta da yakeji janyeta yayi yana murmushin karfin hali ” kanwata kiyi hakuri muje sati dayane zakiyi ki dawo ko ummi ya fada yana kallon ummi dariya tayi” eh sati daya zakiyi habibty ajiyar zuciya ta sabke” to naji amma da anyi sati zaka maidoni kuma ba gidansu wannan banzan gayan bane zan zauna ko ummi ta matso ta doketa abaya tun karfi take dukanta tana mata magana da larabci saida ta Saki Kara ta rukunkume Mahabeer tana kukan sangarta tare dukan yai yanaba ummi hakuri ransa babu dadi Dan yaji haushin bugun da take mata kamar yayi kuka yace” haba ummi Raiyan Zee yarinya ce fah lallabata zamuyi zata daina masa amma dukan yayi yawa sai ajimata ciwo ai idanu ummi Raiyan ta zuba masa cike da mamakinsa ” haba Mahabeer yanzu ahakane zaku ku gyarata kana daure mata gindi wlh shiyasa naso yazo da kansa tun kafin su isa can taci gidansu la’ada waje cikin shashekar kuka tace” Ahukhuya kagani kullum sai ummi ta dokeni saboda wannan mungun mutumin wlh idan mukaje Nigeria mutikar na Ganshi akasar idona
idanusa kafin na dawo Allah na dauki Alkawarin sai na Rama abinda akamun akansa ta fada tana Kara rumgumesa tana kukan takaicin duk lokacin da zata zageshi sai ummi ta doketa kuma duka ba na wasaba shiyasa takejin duk duniya ta tsaneshi sama da komai Hasbinallahu Wani’imar Wakim kawai yake maimaitawa gashi bayason kukanta daurewa yayi yana bubbuga bayanta ” yi hakuri kanwata nima bazan yardaba anaci miki mutumci yi shiru kinji ya leko fuskarta shiru tayi ta boye kanta kirjinsa samu yayi ya lallabata ya janyeta jikinsa Jamal da idanu yake binsu yanajin haushin yada idan tahau jikin Mahabeer yake janyeta baya bari ya rage zafi ba lallashinta ya shiga yi har ta Saki ranta suko su manal sunsha mamaki Dan sunsan Zee baby bata cika kuka ba a Al’amuranta kuka baya cikin tsarin rayuwarta ummi dai da idanu take binsu yau ta Mahabeer take ta Saki jikinta sai labari take bashi yako maida hankalinsa kanta sai dariya yakeyi Jannat na tayasu Dan Mahabeer ya burgeta bashida damuwa akwai fara’a
Saida akayi kiran sallah magrib suka Mike sukayi shirin zuwa masallaci suma su Zee baby suka tafi suyi sallah sai tsokanarta sukeyi wai taga Dan uwanta ta sheresu dariya tanusu batace dasu komaiba,
************
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
*Nigeria* karfe shida na yamma Wata jibgegiyar motace fara sal da ita saman babban titin malali cikin nutsuwa yake driving waya manne akunnesa sai murmushi yakeyi cikin amon muryasa mai dadin gaske naji yace” sweet baby kiyi hakuri wlh kukanki na daga mun hankali kiyi shiru ganina fah saman hanya zanzo na ganki shikenen ko OK Oya fito gani na karaso ina Sauri kar lokacin sallah magrib yayi ya fada yana tsinke kiran saboda ya Iso kofar gidan honr yai mai gadi ya bude masa ya danno hancin motar gidan yana parking ta fitowa masha Allah wata kyakyawa na gani baka ce sosai amma tanada kyau amma ba doguwa bace ba kuma bata fiye gajarta ba tanada hanci dede misali da idanuwa dede gwargwado tanada gashi ba laifi bakinta Dan karamine saidai tanada yar kiba kadan agaskiya dai batada makosa tanada kyau yar 23 year tanda faram faram batada daurin kai saide ta fiye sanyin hali batada hayaniya duk da a turai tayi karatun Nurse har tsawon shakara ukku isowa tayi ta bude motar ta shiga da sallama
tana murmushi shima murmushin ya sakar mata ” sweet baby uwar yan rigima ya gajiya bazaki bari ki hutaba kamar bamu hadu da safe ba ya cikin naki da fatan kinsha magungunan da na kawo miki kanta ta sada tana wasa da hannuta ” nifa kinga matsalata dake dagowa tayi Dan tasan halinsa yanzu zaiyi watsi da lamarinta ya tafiyasa Dan Sam bayason shariya ” my Dr yi hakuri ta fada tana kallonsa cikin dauriya Dan kwayar idanusa fusgar mutum sukeyi my Dr na kayi kyau sosai kamar na saceka ta fada cike da kunya ” OK Oya fadamun me kike so kika tisani da kuka sai nazo kuma gani kina wani sunne sunne ko cikinne ? kanta ta kwantar saman kafadarsa tana sabke ajiyar zuciya “sweet babyna menene bakida lfy ne ? ” my Dr na wlh idan nayi awa biyu ban gankaba banajin dadine amma yanzu banajin komai na warke ta fada cikin sanyinta murmushin gefen baki yai ya dagota kanta daga kafadarsa ya kura mata mayatattun idanunsa yanajin mugu mugun sonta da kaunarta na ratsashi Dan tarbiyyarta tayi masa tamkar ba aturai tayi karatu ba ” my mashakurah wlh nima ina sonki nifa na ganki nace kinmun so sai me ki ajiye hankalinki Dr Sardauna nakine ke daya insha Allah kinji sweet babyna idanuta ta lumshe ta daga masa kai kiss ya mata agoshi ” OK Oya shiga ciki kinji an fara kiran sallah kisha magani kinji? kai ta daga fitowa tayi tana daga masa hannu idanuta sun tara kwalla ya gani sairai idan yace ya lallasheta kuka zata saka masa shiyasa yaja motar ya fisgeta da karfi juyawa tayi ta tafi ta nufi cikin gida yana fitowa ya harba motar kan titi yana gudu sosai ya dauki hanyar kofar Marusa lowcos gudu yake shararawa sosai Dan ya samu sallah magarib, lokacin da yazo har an gama sallah honr yayi aka bude masa katoton get din gidan ya danna hancin motar gidan Ana harbar gidan yai parking ya fito gun mai gadi ya nufa agaguce yayi Alwalla ya nufi masallaci, bai fito daga masallaci ba saida akayi isha’i yana fitowa ya shiga bangaransu wow agaskiya ya hadu sosai d’akunane har biyar ukku daga farko biyu acikin wata yar kwana kwanar naga ya karya dakin karshene Nasa ya ciro key aljihunsa ya saka ya bude kofar wani ni’imataccen kamshi ya me fitowa tamkar yanzune akayi anfani da turarukan masha Allah nace saboda haduwar bedroom din wani royal bed makekensa d’akin ba tarkace amma zaka zata dakin amaryane ga wasu lumtsma lumtsuman kujeru na kayan jikinsa ya rage ya shiga toilet Yajima sosai ya fito daure da towel kirjinsa cike yake da gashi yana da fadin kirji sosai duk amunmurde yake tamkar yanacin karfe agaguce ya shirya ko mai bai shafaba yasa wando 3quater ya saka da Riga short ya fesa turare ya gyara sumar kansa tayi luf luf sai shegi take baka sudik wayoyinsa ya kwasa baki daya ya fito cikin kuzarinsa yake tafiya ko kofar bedroom dinsa bai rufeba ya nufi part dinsu ghaisha da sallama ya shigo parlon ghaisha na zaune Nawwara na jikinta yana shigowa ta Mike suna gaishesa yaran parlon hannu ya daga musu ghaisha tace” bokan turai baki ya turo kamar wani yaro zama kusanta ya kwantar da kansa saman cinyarta ashagwabe yace ” ghgaisha nah wlh duk nagaji” sannu Dr Sardauna ai Dole tin safe sai yanzu tausa ta fara masa” yauwa mamana Allah kuwa ciwon jiki nakeyi dariyace ta kamasu Hafeeza ce dariya ta kufce mata khalisat ta zaro idanu ta Mike sadaf ta gudu tun kafin ya dago aikuwa ya zabura zai tashi ghaisha ta rikeshi suna ganin haka suka matso suna bashi hakuri banda hafeeza da khalisat da suka Ari ta kare ghaisha tace”maza ku tashi kusan nayi ai yasan wa tayi dariyar mik’ewa sukayi suka bar parlon baki ya ciza ya kalli ghaisha” yanzu Dan Allah mamana kina kallo khalisat mai zubin nunar rana itada yar iskan yarinyanan sukamin
Advertisements
dariya kawai Dan nama mahaifiyata shagwaba dariyar ta danne ” haba Dr Sardauna khalisat baiwar Allah me take cewa acikin gidanan wlh banda ita akama dariya hafeeza ce ita zaka lakada amma banda khalisat baiwar Allah yarinyar da magana ma ba damunta tayi ba mareniyar Allah Aunty amarya ta fito daga kitchen tana dariya ” Wlh Aunty daurin gindinki dai ta samu Dr mun kabarsu zanyi maganinsu baki ya ciza Dan ya tsara launin azabar da zai musu bayan sun mance da anyi abun danshi baya horo kai tsaye ” Auntymu ki barsu zanyi maganinsu wayar sace ta dauki ringing screen d’in wayar ya kalla Ahmed ya gani mik’ewa yai yayi picking ya Kara a kunnesa ya fice daga parlon akofa suka ci Karo da Daddy murmushi ya masa “ah Dr kaida mutanan Saudia ” Daddy bari na dawo akwai hira ya tafi yana magana Daddyn kansa ya girgiza Dan yasan tambayarce bata masaba ya samu ya sulube masa Dr Sardauna mota naga ya shiga yamata key honr yayi aka bude masa get ya fice daga gidan aguje,
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
*Saudi Arabia* bayan sunyi sallahr isha aka fito da abunci Wanda ragone jibgegensa aka gasheshi da dafe dafen abunci irin irin nasu na larabawa Jamal sai baki yake washewa zaune suke akasa saman carpet sun baje baki dayansu suka hadu sunacin abuncin ummi Raiyan sai farin ciki takeyi ta tuno da mijinta da yaranta yan mazan Zee baby na kusan Mahabeer ta tisasa da rigima Dole sai shine yake bata abaki itama nata bashi su manal sai dariya sukeyi ummi dai kai ta girgiza Jamal shifa haushin Mahabeer yakeyi. dan de ba yanda zai yine suna kammalawa mai aiki tazo ta kwashe komai ta gyara gun sukaje suka wanko hannusu aka dawo Ana hira su jannat sai karfe goma suka tafi gida sun rakasu suna dawowa su ukku ita da Mahabeer da Jamal suka tardo majeed kofar gidan ya fito amota yashi gaban Zee baby cikeda rashin kunya ta rike k’ugunta tana girgiza zatayi magana Mahabeer ya riketa ya janyota cikin gida aikuwa kafin kofar ta rufe ya biyosu yana magiya ta sauraresa hararasa Mahabeer yake ransa abace cikin harshen turanci” kai malam kama gabanka tunda bata Sonka karabu mana da ita yau naga jaraba Dama haka kuke da kwawa ya dage sai masifa yake kirtama majeed shiko burinsa Zee baby ta kulasa dadi taji ta rungume Mahabeer tana dariya” yauwa Ahukuyah cimun durin uwarsa tunda ubansa yace baya kaunata na tsaneshi wollah bana sonsa yanzu dadi ya cika Mahabeer janyeta yai jikinsa ya kamo hannu majeed ya ingizashi waje jamal yace” wai kai ina ruwanka da shiga tsakanin masoya ” dallah malam yimun shiru yaja hannuta su shigo parlo sai cika da batswa yakeyi itako dadi takeji sai sangarta take zuba masa jamal na biye dasu ummi Raiyan tace ” Mahabeer wai dama tare kuke sakinsa tayi taje gun ummi ta rumgumeta ” ummi bari kiji rada ta mata akunne ” ah haba ikon Allah Mahabeer yanzu shirmenta zaka biyewa dariya yayi yana Sosa kansa hira sukaci gaba dayi sai karfe daya suka ma ummi sallama
Zasu kwanta Zee ta ririke Mahabeer bazai kwanta ya bari sai anyi sallahr asubah saida ummi ta riketa tace su tafi sukwanta kar yabiye mata ita ba bacci take ba dakinsu suka nufa ummi ta ja hannuta suka shiga bedroom d’in ummi tasa ta cire kayanta tayi wanka tasaka kayan bacci Riga da wando iya gwiwa ta lallbata suka kwanta tana rumgume da ita tana shafa mata gashinta kinyin barcin tayi tanaga ummi tayi bacci ta janye jikinta sadaf ta fito daga d’akin ta nufo parlo ja tayi ta tsaya ganin Mahabeer tsaya yana kai komo ya rasa me keyi masa dadi cikin farin cikin ganinsa ta nufi gunsa da gudu tana kiransa “Ahukhuya juyowa yayi suka hada idanu farin ciki ya ganin kan fuskarta amma ganin kayan jikinta ai bai bari ta karaso ba Dan yasan ba inda zata tsaya sai saman jikinsa ai kuwa ya zunduma da gudu ya nufi dakin da yafito yana shiga ya banko kofar ya murza key taji karan murza key din zubewa bakin kofar dakin tayi ta fashe masa da kuka tana kiransa Ahukhuya….✍🏻
Sai kunji next page insha Allah
GIPHY App Key not set. Please check settings