Advertisement
*19*
A ladabce dan san ya samu abinda ya ke so ya sunkuyar da kai yace “Sarki na, mhe zai hana ka zauna sai mu tattauna.”
A wulak’ance sarki Musail ya nuna kan shi yace “Da wa? Da ni? Ai har abada, ka manta rabuwarmu da kai ne?”
Murmushi Bikhatir yayi ya sake yin k’asa da kan shi yan tuna rabuwarsu ta k’arshe wacce basu sake had’uwar ba sai yau kuma yanzu, shekarun da suka gabata a baya gaba da gaba kuma ido cikin ido Bukhatir ya kalli sarki Musail yace _” Na yarda kayi nasara a kai na a kan ta, ban damu ba ko dan kana da mulki a hannunka ne kayi nasara a kai na, amma ka sani daga yanzu ni da kai gaba ce a tsakaninmu dan ka rabani da matar da nake da burin ta zama ta wa, shi kan shi wanda take so a matsayin abokin gaba na dinga kallonshi, kuma a kowace wucewar rana neman hanyar da zan kassarashi nake, na yi farin cikin mutuwarsa fiye da tunaninka, amma yanzu mutuwarka ita ce abar harina.”_
Sanyayyar murmushi ya kuma sako dan sai yanzu kalaman suka bashi dariya ma, sarki Musail ma murmushin yayi yace” Da alama ka tuna, dan haka ka gaggauta barin nan kafin na sa a cire maka kai, komata ka shigo.”
Dhurani ne ya sunkuya daf da kunnenshi yace” Ina ga fa zai fi mu saurare shi, haka kawai ba zai zo ba idan babi dalili mai k’arfi.”
Kallon shi yayi yace” Malami ina so ka sani duk wani abu da zai min barazana da rayuwata babu ni babu shi, ka fi kowa sanin haka.”
Kallonsu Bukhatir yayi yace” A gafarce ni ranka shi dad’e, maganar dake tafe da ni mai mahimmanci ce, magana ce akan gimbiya Zafeera, na san zaka so jin inda take? Tare da kuma wa take?”
Girgiza kai sarki yayi yace” Ta ya zan iya yarda da kai?”
Advertisements
Nuna masa k’ofa yayi yace” Gimbiya Zafreen, ai ta dawo cikin k’oshin lafiya, ko bata fad’a maka tare suke da yar uwarta a can ba a hannu na?”
Shiru sarki Musail yayi yana kallon fuskar Bukhatir, ya jima haka alamar yana ta tunani kafin ya jinjina kai ya taka a tsanake, wata k’ofa wacce wanda mai kallo zai yi tunanin ban d’aki ce ya bud’e ya nunawa Bukhatir yace” Akwai buk’atar muyi sirri?”
Da girmamawa yace” Me zai hana.”
Bin bayanshi yayi da ido sarki Musail ya ma Dhurani signar ya biyoshi, shi ma wucewa yayi a k’arshe suka bar Zeyfi tsaye dan sauran abokan tafiyar sjna farfajiyar gidan, ganin haka ita ma sai ta koma ta zauna tana gyara lullub’inta ta maida hankalinta ga kallo b’angare d’aya kuma tana tunanin ko me ya sa ya zo nan da ita kuma?
A ciki kuwa zazzaune sukayi suna ta kallon juna kafin sarki Musail yace “Ina jinka? Me yasa ka sace min yarana duka biyun?”
Murmusawa yayi ya sauke numfashi yace “Ba na sacesu bane dan na cutar da su.”
Da sauri sarki Musail yace “To me ka musu?”
Numfasawa yayi sosai ya d’an muskuta yace “A makarantar da su gimbiya suke akwai wasu makusanta na, daga bakinsu na samu labarin lallai ana bibiyarsu, da fari ban d’auki abun da mahimmanci ba saboda abunda ke tsakanin mu, amma a ranar da wata yar ajin su gimbiya Zafreen ta fad’a min ana shirin d’aukesu, sai na yi gaggawar tayar da hatsaniya dan na d’aukesu ba tare da hankalin kowa ya kai cewa su ne kawai aka rasa ba, sai dai kash ! Sarki Wudar yana da matuk’ar wayo da kuma mutane sosai, duk tsaron da nake ganin na ba wa gimbiyoyinmu saida ya d’auke mafi mahimmanci da tsadar.”
Nisawa sarki Musail yayi yana kallonshi yace “Kenan yanzu gimbiya Zafeera tana hannun Wudar?”
Jinjina kai yayi yace “Shakka babu.”
“Ta ina ya bi ya d’auketa a cikin gidan da kake ikrarin ka bata tsaro?”
Ya fad’a yana watsa mishi wani kallo, ba tare da alamar tsoro ko firgita ba yace “Na yi iya k’okari na wajen killacesu, saidai ko ma ta ya ya suka d’auketa a gidan nan na fi tunanin sa’ilin da sarki Wudar ya buk’aci mu keb’e ne ni da shi, to a lokacin mutanenshi suka d’auketa, ko kuma wannan d’an na shi.”
Advertisements
Jinjina kai sarki Musail yayi yace” Shikenan, zai gane yana tare da kadarata ma fi tsada da daraja a duniya.”
Da sauri Bukhatir ya kalleshi yace” Yawwa sarki na, ina so kayi iya k’ok’arinka wajen…”
Shiru yayi ya had’e maganarsa sakamakon kallon da sarki Musail d’in ya masa, sunkuyar da kan shi yayi yace” A gafarce ni.”
Wani malalacin murmushi sarki Musail yayi yace” Har yanzu ban ji zuciyata ta gama yarda da kai ba Bukhatir, kai ma nasan kana son ganin bayana, ka samu Zafeera kuma ka rabu da ita ta sauk’i haka, da wuya gaskiya.”
A ladabce yace” Ka yarda dani sarki na, babu hannu na a b’atanta, hasalima sanda sarki Wudar ya zo ya so yi min tayin gimbiya Zafeera da duk abinda ya mallaka, amma na nuna mana darajarta ta wuce haka.”
Wata yar dariya yayi yatsare shi da ido yace” Amma me ya kai shi gidanka a ranar data kasance tana gidanka?”
Kura masa ido yayi yace” Iyeh?”
Wani kallon firgitarwa Dhurani ya masa yace” Aka ce me ya kai shi gidanka a wannan lokacin? Wata k’ulalliya xe a tsakaninku ?”
Girgiza kai yayi yace” Kamar yanda na fad’a maka yana da mutane da dama da suke masa lek’en asiri, kar ka k’aryatani idan har na fad’a maka a masarautar nan ma yana da yan sa ido, dan ta hakane ya samu cikakken labarinta.”
Kallonshi yayi kamar zai hango gaskiya a fuskarshi sai kuma yace” Na yarda da abinda ka fad’a yanzun, amma Bukhatir…”
Ya fad’a yana mik’ewa tsaye ya d’ora da” Alamu sun nuna a matse kake da son ganin an samo gimbiya Zafeera, shin idan aka yi hakan me ye tukuicinka kai?”
Gaba d’aya gabansa ya yanke ya fad’i ya shiga tunanin abinda zai fad’a masa, amma yanda ya tsareshi da ido yasa dole ya sunkuyar da kai yace “Farin ciki ma ya wadace ni idan har d’iyar yar uwata ta fito a hannunshi cikin k’oshin lafiya.”
Dariya sarki Musail ya bushe da ita kamar wani mahaukaci ya dinga gaggab’awa, da k’yar ya tsagaita kuma kamar ba shi ba ya kalli Bukhatir fuska a hade yace “Shikenan, zamu gani.”
Juyawa yayi zai fita sai kuma ya tsaya ba tare daya juyo ba yace “Ba dan kar ka fita kana fad’in ban iya tarban bak’i ba, da ko ruwa ba zan ba ka ba Bukhatir dan nasan manufarka a kai na, amma karamci na ya isa insa a wadataku da abinci ko dan labarin daka siyar min.”
Da mamaki Bukhatir ya kalli k’eyarsa cike da takaicin wulak’ancinshi, wato ya ma d’auki abinda ya fad’a masa a matsayin labari har kuma ya siya? Sarki Musail ne ya katse masa shirunsa sanda ya juyo a hankali ya kalleshi yace” Ya suke? Suna cikin k’oshin lafiya?”
Wani kallo Bukhatir ya mishi yana ji kamar ya mik’e ya shak’eshi, wallahi da yana da sarauta a lokacin babu abinda zai hanashi d’urawa Musail ashar saidai duk su k’one a nan, iyayen Juman fa yake tambayarshi, shi bai san komai ba dangane da yanda aurensu ya kasanxe da Juman, amma dai tabbas ya fahimci akwai barazana a ciki wacce ita ce ke d’awainiya da iyayenta har yanzu, tunda ya d’auketa daga garesu shekara ashirin da bakwai har yau bata tab’a taka k’asar Egypt ba ko da sunan taro bare da niyyar ganin mahaifanta, hakazalika su ma basu tab’a yunk’urin kawo mata ziyara ba, tsufa ya cimmu su sosai amma damuwarta ita ce ta k’ata tsofar da su, dan wasu lokuta har k’aura sukeyi daga masarauta su ware kansu gefen gari su hana kowa zuwa inda suke.
Amma dan rashin mutumci shi ne yake tambayar wai suna lafiya? Da k’yar ya d’aga labb’anshi yace “Suna lafiya, sai dai ba sa cikin farin ciki.”
Tab’e baki Musail yayi yace “Hakane zai kasance dama, kuma kai ma nasan ba ka farin cikin, amma ka sake jaddada musu su sake yin nesa da ita, dan halin da take ciki yanzu idan suka ji zuciyoyinsu bugawa zasuyi su mutu a take.”
Yar harara Bukhatir ya wurga ma k’eyarsa sannan ya jinjina kai alamar to, ficewa yayi Dhurani na bin bayanshi shi kuma ya bi su da kallo da son sanin me kuma ke faruwa da Juman d’in? Tana ina ma? Me yake damunta? Shin tana farin ciki da auran waccen dabban ne ko kuma a’a?
Girgiza kai yayi cike da rashin jin dad’i ya d’auke kan shi daga k’ofar yana d’an jan tsaki, mik’ewa yayi ya fito ya dawo falon ya samu Zeyfi zaune tana kallo, haushi ya ji ta bashi da kallon fuskarta, gefenta ya zauna yana sake murtuke fuska, ita kuma cikin ladabi ta kalleshi tace “Lafiya ko? Me kuka tattauna haka? Naga kamar ranka b’ace?”
Ture hannunta yayi data dafa na shi hannun yace “Ba komai malama, zaki iya yi min shiru.”
A sanyaye tana had’e kukan dake taho mata a mak’osho tace “Me zai hana?”
D’ora kan ta tayi bisa kafad’arshi taake cukukuiye hannunshi tana siraro yar k’walla, cikin jin haushi ya kalleta dan har k’asan zuciyarshi yake jin tsanar yarinyar, baya sonta bai kuma tab’a son ta ba, ita kawai zab’in mahaifinsa ce ba yanda ya iya, amma shi kad’ai yasan irin dakon kayan da yake a game da ita, zama da wanda baka so babban k’unci ne da zai iya baibaye maka rayuwarka har abada, indai yana kusa da ita to baya farin ciki bare murmushi, ita kuma ga ta da na ci da jaraba a ganinshi, shiyasa in zaiyi wata bai nemeta idan ta kai kanta gareshi sai ya kirata da jarababbiya mayya.
Yanzu ma ya so tureta daga jikinshi, amma daya tuna sarki Musail ya ce zai wadatasu da abinci saiya k’yaleta, ammafa sai tsaki yake yana ta had’e fuska kamar kashi nea jikinshi, yayin da ita kuma take jin wata nutsuwa na sauka a zuciyarta na ganin bai turetaa jikinshi ba, sai ta ssamu kan ta da sake shige masa tana sauke ajiyar zuciya.
*Giobarh*
*Da yamma* sarki Wudar na zaune a lambun cikin masarautar tare da fadawa biyu dake nesa da shi yana jin dad’in yanayin, wazirinsa ne ya shigo bayan mai tsaron k’ofar ya masa izinin shiga, da sauri kamar zai tashi sama ya k’araso, zube gwiwoyinshi yayi k’asa yana mik’awa sarki Wudar takardar hannunshi yace “Shugaba na, gashi, akwai matsala fa babba.”
Rai b’ace ya kalleshi ya karb’i takardar yace “Waziri ba na fad’a hutu nake buk’ata ba kar wanda ya dameni?”
A kid’ime yace “Ka gafarce ni yallab’ai, wannan takardar ta fito ne daga sarki Musail, hankalina ne a tashe shiyasa.”
Da sauri ya shiga warware takardar ya k’ura ido dan karantawa, firgitattun kalamai ne kamar haka _”Daga yanzu zuwa wayewar garin gobe ina buk’atar ganin ‘yata gimbiya Zafeera dake hannunka, watsar da buk’atata kuma yana nufin yak’i kake nema da ni, kuma a shirye nake da fuskantarka dan ina da adadin dakarun da zasu iya k’wato min babbar kadarata.”_
A razane ya kalli wazirin yana jin zufa zata keto masa, jefar da takardar yayi ya tunkari hanyar fita, da sauri wazirin mmaa ya bi bayanshi yana mai son jin hukuncin da sarki Wudar d’in zai yanke, dan in har ya zab’i yak’i da sarki Musail to fa shi dai kam babu hannunsa, magana ta gaskiya ma zai tattara iyalinsa su bar k’asar har su gama sai ya dawo, dan ya sani ne ba zasu iya da sarki Musail ba, alfaharinshi kad’ai ya isa ya saka shi d’auko wasu rundunoni daga mak’wabtan masarautu dan su yak’esu su kuma yi kaca-kaca da su.
*Ayam* na d’akinta zaune duk ta matsu dare yayi ta ga abun bazatar nan ta ji an banko k’ofar an fad’o, da sauri ta mik’e tsaye tana gyara rigarta, da ladabi tace “Barka yallab’ai.”
Murmusawa yayi tare da saita nutsuuwarshi wuri d’aya sannan yace “Barka gimbiya Zafeera.”
Kallon idonshi tayi tace “Yallab’ai, zan fi jin dad’i idan ka kirani da Ayam.”
Murmushi yayi ya rik’o hannunta cikin na shi, fad’uwar da gabanta yayi ne yasa ta saurin saka idonta akan fuskarshi, kakkausan kallo ne ta masa dake nuni da me hakan ke nufi? D’an motsa hannunta tayi alamar tana so ta k’wace, amma sai ta ji kam ya rik’eta sosai, jan ta yayi zuwa bakin gadon suka zauna, sam ta k’i d’auke idonta a kan fuskarshi yayin da shi kuma ya kasa kallonta saboda kallon da take masa, idonshi na kallon cinyoyinta duk da cikin riga suke ya shiga fad’in “Gimbiyata, ina so ne na fad’a miki wani abu, sai dai ina jin tsoro.”
Mutsu-mutsu ta dinga yi da hannunta saida ta k’wace kafin ta d’an kawar da kan ta tace “Ina jinka yallab’ai, fad’a min ko menene.”
Gyara zamanshi yayi ta hanyar matse mata wuri, da sauri ta ja baya ta sake jefa masa kallon bansan iskanci tare da yatsina fuska tace “A’a yallab’ai, wai me ye hakane?”
Fuskarshi d’auke da murmushi yace “Kina ji ko? Ban san ko wani ya fad’a miki tarihinki ba…”
Da sauri ta jinjina kao tana sake matsawa baya tace “E e, an fad’a min, amma ban yarda ba, watak’ila kai zaka fad’a min gaskiya.”
Tsurawa fuskarta ido yayi yace “Kinsan komai game da ahalinki kenan?”
Girgiza kai tayi tace “Ta ya zan san komai a game da su? Bayan ko kamanninsu ban sani ba.”
A nutse ya sake kallonta yace “Kinsan bayanin b’atanki?”
A shashance tace “E, yallab’ai Umad ne ya fad’a min wai mahaifiyata ce ta bayar da ni dan ta kareni.”
Da alamar tambaya a fuskarshi yace “Umad? Dama kun yi magana da shi ne?”
Tuna kalaman Umad da tayi cewa saboda tsaro yake nesa nesa da ita yasa ta saurin fad’in “A’a ai d’azu ne da ka ce mu jira a waje, mun fara maganar sai kuma na nuna masa ban fahimci komai ba kawai.”
Jinkina kai yayi alamar gamsuwa yace “Kin tabbatar ya fad’a miki mahaifiyarki ta ceci rayuwarki daga masu son cutar dake ne?”
A gatsine tace “Haka ya fad’a, amma ni ina ganin me ye dalilin da zai sa a rabu da ni tun jinjira? Shin masu son cutar da ni d’in suna tare da ni ne a lokacin da take ganin rayuwa a cikinsu zai sa ni cikin had’ari?”
“Tabbas.” Ya fad’a yana kallonta, da mamaki ita ma ta kalleshi tace “Kamar ya?”
Fuskantarta yayi da kyau yace “Gimbiya Zafeera, a lokacin masu son kasheki dayawa ne, saidai wanda ya fi su had’ari kuma babban cikinsu shi ne, sarki Musail, wato *mahaifinki*.”
Irin kallon nan na galala ta masa kamar wacce bata hayyacinta, duk da labarin sabin iyayenta ba wai ta yarda ba ne, amma dai sai ta ji abinda ya alak’anta mahaifinta da shi ya mata ciwo yana kuma neman zautar da ita, zunbur ta mik’e tsaye tace” No! No! No… No…Hakan ba zai faru ba.”
Cikin d’aga murya tana nunashi da yatsa tace” Yallab’ai ku gaggauta dakatar da labarin k’anzan kuregen nan na ku, kuna neman ku haukata da wannan banzayen labaran, kun manta ni d’in yarinya ce? Shekaru na ba zasu d’auki wannan k’arairayin na ku ba, please yallab’ai ku daina na rok’eku.”
Had’e hannaye tayi alamar rok’o tace” Na rok’eka ka mayar da ni garinmu, ka taimaka ka kaini wajen iyayena ina son ganinsu.”
Mik’ewa yayi tsaye yana neman kamo hannayenta yace”…
*Alhamdulillah*
GIPHY App Key not set. Please check settings