Lu’u Lu’u 24

Advertisement

 

*24*

 

 

 

 

Tsoro matuk’a ya kamata ganin abinda y faru daga zuwanta, da an samu akasi kenan da ita ce zata mutu? Shin wane irin had’ari ne wannan a daidai wannan lokacin? Shin me yasa sai… Kafin ta sake tambayar kan ta ta ji sarki Musail ya shigo a rud’e yana nuna tashin hankalin k’arya, rumgumota yayi jikinshi yana duddubata yana fad’in “Gimbiya Zafeera kina lafiya? Ba abinda ya sameki dai ko?”

 

A raunane tace “A’a pah babu komai, saidai ita…matar ta mutu.”

 

Advertisements

Ta fad’a tana fashewa da kuka, shafa bayanta yayi ya sauke ajiyar zuciya yana feso iskan rashin jin dad’i, likitar agajin gaggawa dake cikin gidan ne suka fito da gawar a gadon arasa lafiya suka fita da ita, hakan uasa Ayam sake fashewa da kuka, shi kuma sai daddab’ata yake alamar tayi shiru.

 

Suna fita da gawar Zafreen na shigowa da saurinta ta kalli sarki Musail tace “Pah lafiya? Me ya faru?”

 

Girgiza kai yayi yace “Wani had’ari ne ya faru, sai dai abun ya zo da sauk’i tunda wata baiwa ce ta mutu ba ‘yata ba.”

 

Kallonshi Ayam tayi haka ma Zafreen Ayam ta kalla tana mai had’e fuska, cikin nuna kulawa Ayam tace “Pah ita ma fa mutum ce, kenan da ya zakuyi idan ni ce?”

 

D’an tsaki yayi daya nuna maganar ta haushi ta bashi yace “Karki damu da wannan, ki je kiyi wanka ki shirya.”

 

Sakinta yayi ya juya zai fita tayi saurin fad’in “Pah, idan so samu ne ina so na ga Mah d’ita yanzu, a zan iya wankan nan ba a yanzu dan na tsorata.”

 

Advertisements

Wani kallo ya mata tare da sakin murmushi yace “Tsoro? Ke d’in zab’abb’iyar Khazira?”

 

Fashewa yayi da dariya wanda hakan ya zama jikinshi sakamakon yawan ta’ammali da giya, kallonshi ta dinga yi sai ta ji tsoronshi na samun muhalli a zuciyarta yana zaunawa, saida ya ga dama dan kanshi ya tsagaita ya nunata da yatsa yace” Ke ce zaki bayar da tsoro abisa tsarin, amma ba dai ke kiji tsoro ba.”

 

Shafa kuncinta yayi yace” Ki samu ko huta, zaki ga Mah d’inki anjima.”

 

Da kallo ta bishi har ya fice a d’akin, a wulak’ance Zafreen ta k’yasta mata yatsunta tace” Malama ji nan.”

 

A hankali ta kalleta da idonta da suka d’auki launin ja mai duhu kad’an, matsawa tayi daf da ita a gadarance tace” Kina farin ciki ne saboda kin zo babbar masarautar Khazira? Hummmmm! To kar ma ki fara yarinya, dan farin cikinki nan gaba kad’an zai koma ciki.”

 

Ba tare da hayaniya ba Ayam ta sake kallonta tace” Me kike nufi?”

 

Murmushin gefen labb’a tayi tace” Ina nufin ni ce babbar ‘ya a msarautar nan, hakan na nufin ni ce magajiyar duka fada da kuma kujerar mulkin, dan haka ki gaggauta barin nan sannan ki manta kina da ahali a nan d’in, idan kuma ba haka ba nadama ce zata biyo baya.”

 

K’asaitaccen murmushi Ayam ta sauke ta rumgume hannayenta a k’irji ta gyara tsayuwarta tace” Da alama ke kuma abinda ya sha miki kai kenan, to ki sani ni ban ma san da wannan masarautar ba sai kwana biyu zuwa uku da suka wuce, infact har yanzu ban ji na gama yarda da cewa ku d’in ahalina bane, har yanzu zuciyata raya min take tatsuniya ake rad’a min a kunnuwana, sarauniya Juman ce kad’ai na ke son had’uwa da ita ta kuma tabbatar min, idan har ta tabbatar min da bakinta shi ne zan yarda da sauki burutsunku.”

 

D’auke hannayenta tayi daga k’irji tace” Shawara d’aya yar uwa, ki rage soyayyar nan da kike wa mulki, dan idan har kika sameshi alamu sun nuna giyarshi zata fi haukataki.”

 

Sama da k’asa ta harareta tare da jan dogon tsaki ta fita a d’akin tana fad’in” Matsalarki ce kuma wannan.”

 

Da kallo kawai ta bita a zuciyarta tana fad’in” Ke ma zata zama ta ki nan gaba kad’an.” Fita tayi a d’akin ita ma ta koma falo ta zauna jiran tsammani.

 

 

Ta jima zaune ita ba kallo ba ita ba bacci ba har saida aka k’wank’wasa k’ofar d’akin, da sauri dan dama ta k’agu da zaman tace” Shigo.”

 

Bud’ewa akayi aka shigo, cikin ladabi hadimar ta sunkuya tace” Ranki shi dad’e, sarkina ne ya umarceni da na rakaki zuwa sama dan ganawa da mutanen gari.”

 

Da mamaki tace” Sama kuma?”

 

Yar fara’a tayi tace” A saman bene nake nufi.”

 

Mik’ewa tayi tana fad’in” Oho.”

 

Fita sukayi suka bi ta matakala, suna kan tafiya a hawa na uku suka had’u da d’aya daga cikin dogaran gidan, rab’ewa sukayi dan hanyar ba wata mai fad’i bace, kamar Ayam ji tayi ya damk’a mata abu a cikin hannunta, abun mamakin kuma bai kalleta bai sai rusunawa da yayi saboda sanin matsayinta ya gaisheta kai tsaye kuma ya wuce abin shi.

 

Ganin hadimar tayi gaba bata kula bda komai ba yasa Ayam bud’a tafin hannunta, k’aramar waya ce mai kyau fara sol da ita mai murfi k’irar Samsung, da mamaki take kallon wayar ta sake juyawa ta kalli mutumin har ya sauka, “Waye shi?” Shi ne abinda ta tambayi kanta ta bi bayan hadimar nan kawai tana sake jimk’e wayar a hannu.

 

A saman fili ne da shi ma aka k’axatashi dan shan iska, wata k’ofa ta bud’e ta d’auka wani wurin zasu shiga, sai gani tayi kawai ashe titi ne zaka iya hange, kamar jira suke dama sai kawai ta ji ihun da saida ta zabura ta rike hannun hadimar nan, d’aruruwan mutane da suka taru dan ita, da mai kyakyawar niyya da mai akasin haka dukansu, gashi sai ihu suke suna d’aga mata hannu alamar jin dad’in ganinta.

 

Cikin girmamawa hadimar tace “Duk dan ke suke nan ranki shi dad’e, shekaru wasun su suka kwashe suna fatan bayyanarki, dayawa sun ci buri akan dawowarki da sa ran sabon tsarin da zaki kawo musu, daga cikin talakawan nan akwai wad’anda suke sadakar abincinsu dan abun bauta ya kareki a duk inda kike sannan ya dawo musu dake lafiya.”

 

Da mamaki Ayam ta kalleta tace” Mutanen da sukayi sadakar abinci saboda ni, kuma shi ne za’a bani izinin ganinsu daga nesa?”

 

Gyara tsayuwa tayi ta had’e fuska wanda ita kanta bata cika sanin tana kama jikin nan ba tace” Muje ki kaini ta inda zan gansu ga da ga.”

 

Kallonta hadimar tayi da niyyar yi mata gardama, sai kuma ta sake rusunawa jikinta na b’ari tace” Ranki shi dad’e izinin da mai martaba ya bani kenan, idan na sab’a masa zai iya hukunta ni.”

 

Saida ta gama saurarenta tas tace” Ki kaini na ce.”

 

Jinjina kai tayi jiki na kyarma ta rufe wannan k’ofar ta juya bayanta, ita a Ayam juyawa tayi sai ta ga ta bud’e wata k’ofar, rab’ewa tayi tace” Muje tanan ranki shi dad’e.”

 

Wucewa Ayam ta fara yi suka sauka a matakalar, suna kai wa k’asa ta sake bud’e wata k’ofar, suna bi ta siririn corridor sai ga su ga al’ummar nan, caaaa sukayi kanta kowa k’ok’arin rumgumarta yake, sa’a d’aya dogarai dake wurin suka dinga taresu suna maidasu baya.

 

Hannaye ta dinga d’aga musu fuskarta d’auke da murmushi wasu kuma har hannun na ta suke rik’ewa, cikin hakane wani tsoho sosai daya tsufa ya shafi tafin hannunta sai kuma ya sumbaci hannun na shi, fashewa yayi da dariya yana murna da fad’in “Na gode abun bauta, ko yanzu ka d’auki rai na ban da bakin ciki dan jikina da na ta ya had’u.”

 

Da mamaki jin furucinshi ta kalleshi, sai ta fahimci dayawa dake tab’ata abinda suke yi kenan, a rikice kuma a mugun rud’e ta kallesu ta ja baya cikin murya mai fitar da amon tashin hankali tace” Me kuke yi ne haka? Ya haka kuma?”

 

 

Girgiza kai tayi cike da damuwa hawaye na gangaro mata cikin kasalalliyar murya tace “Kun sani jin kunya ganin yanda kuke min abu kamar wata waliyiya, me nake aikatawa daya sha bambam da ku? Me na muku? Wacece ni? Me yasa bakuyi tunanin ni ma mutum ce kamar ku ba? Me ya hanaku fahimtar ni ma ina da irin buk’atocinku na rayuwa, kama daga cin abinci a lokacin buk’atarsa, shan ruwa yayin buk’atarsu, wanka da bacci duka ni ma iya ni, hakazalika idan abincin da na ci ya kai wani mataki na kan buk’aci shiga ban d’aki dan na fesar da marar kyau da kuma anfani a jikina.”

 

Sanyayyar ajiyar zuciya ta sauke tasa hannu ta share hawayenta ta ci gaba da fad’in” Ni ba kowa bace, ya kamata a dakatar da wannan farfagadan da wasu suke son su mulkeku da shi, duk da bansan me ce ce asalin baiwar wad’anda suka gabace ni ba, amma dai nasan an zuzuta abun, dan haka daga yau bana son sake ganin kuna min irin wannan da sunan girmama baiwata ko dan ni zab’abb’iya ce, ni ma mace da namiji suka haifeni sannan aka raine ni kamar yanda aka reneku.”

 

D’ag musu hannu tayi zata juya ta koma wani namiji ya d’aga muryarsa yace” Hakan na nufin ke ba zab’abb’iya ba ce kenan?”

 

Juyowa tayi sai kawai ta sauke ido akan shi, cike da fad’uwar gaba ba tare da tunanin zata iya hangoshi a cikin mutanen nan ba yayi saurin sunkuyar da kan shi k’asa, murmushi ta saki tace” E hakane, ni ba zab’abb’iya ba ce, tunda ni dai ban ga wani abu a jikina ko a cikin rayuwata ba daya sha bambam da na ku.”

 

Wannan tsohon daya tab’a hannunta ne yace” To amma gimbiya ya maganar canjin da zaki kawo mana? Dan na b’ata shekaru da dama ina ciyar da abinci dan kawai ki bayyana ko ‘ya’ya zasu samu rayuwa mai kyau fiye da ta wa, duk da ba k’arfin ciyarwar gareni ba.”

 

Da mamaki ta kalli tsohon ta gyara tsayuwa tace” Baba yayanka nawa?”

 

Kai tsaye ya bata amsa da” Bakwai, maza hud’u mata uku, amma duka matan na gidan aurensu.”

 

Kafeshi tayi da ido tace” Dukansu sunyi karatu?”

 

A ladabce yace” K’aramar ‘yata ita ce aka haifa shekara biyu bayan haihuwarki, daga lokacin da aka haifeki dukda kinyi b’atan dabo, hakan bai sa na cire rai da samun canji ba, daga lokacin na daina biyan kud’in karatunsu na ce su zauna gida suna kama min sana’ata, dan canji ya kusa zuwa da zasu samu rayuwa mai kyau.”

 

Had’e fuska tayi ta girgiza kai tana ji kamar ta wanka masa mari, saida ta feso zafin dake balbali a zuciyarta kafin ta sake jimk’e wayar nan dake hannunta ta kalli tsohon tace” A hakane kuma kake nema musu canjin rayuwa? Shin ko kasan da ace zan tattara takardun wad’anda sukayi makaranta ne sannan na basu aiki, kasan da ‘yayanka babu wanda zai shiga ciki?”

 

Cikin jin haushi da fad’a ta kalli dukan mutanen tace” Ire irenshi na wa ke akwai a nan? Wace irin rayuwar jahilci da mutuwar zuciya kukayi a baya? Saboda kawai an ce an haifi zab’abb’iya, shin cikinku akwai wanda zai iya nuna min wani canji guda d’aya tak wanda cikin wanda suka gabaceni suka kawo muku wanda ya tallafi rayuwarku da ta yayanku?”

 

Kallon tsohon tayi ta d’ora da fad’in” Me aka tab’a canza muku kafin zuwana ni?”

 

Wulwula ido yayi sai kuma ya girgiza kai yace” E to, zab’abb’e daya gabata wanda daga gareshi muka samu labarin zuwanki, a lokacin muna da k’arancin ruwa, kuma mun kawo kukanmu so ba adadi a wajen sarkinmu, to a lokacin shi ne ya mana rinjiyoyin ruwa wanda a yanzu malaman fada suka mayar da su panpunan zamani.”

 

Jinjina kai tayi tace” Na ji kun samu ruwa kyauta, bayan shi fa?”

 

Wata dattijuwa dake gefe ne tace” Wa ya fad’a miki gimbiyarmu? Ai bayan rasuwarshi da wasu shekaru sai iyalenshi suka fara karb’ar kud’in jama’a idan zasu d’ebi ruwa, yanzu haka yara ne birjik a duk gurin birtsatsen nan suna karb’ar kud’i ana d’iban ruwa.”

 

Wani murmushi tayi tana girgiza kanta kafin tace” Anfani kawai suke da ku suna cika aljihunansu, amma daga yanzu ba zaku sake biyan kud’in ruwa ba, ni zan yi magana da sarkinku wato mahaifina, ku kwantar da hankul…”

 

Ihun da suka saka da k’arfinsu da tapi na murnar abinda ta fad’a yasa ta dafe kunnuwanta da ta ji ihun har cikin dodon kunnuwanta, addu’a suka dinga mata da fatan alkairi da kirari sanda ta juya tare da rakiyar hadimar nan dogarai kuma suna rik’e mutanen saida suka ga shigewarta an rufe k’ofar kad’ai hayaniyar ta lafa wasu suka fara barin wurin ma.

 

Suna cikin taka matakalar wayar dake hannunta tayi vibration, da sauri ta duba ta ga lamba ce babu suna, tab’e baki tayi ta bud’e ta kara a kunne, muryar sarki Wudar ce ta ji cikin shauk’i yace “Gimbiyata, fatan kin sauka lafiya?”

 

Da mamakin jin muryarshi d tunanin kenan shi ya turo mata da wayar? Ganin hadimar nan ta juyo tana kallonta yasa ta mata alama da hannu tace “Ki je kawai ina zuwa.”

 

Saida ta ga ta juya ta tafi ta sauke ajiyar zuciya tace “Yallab’ai barka.”

 

Cike da jin k’uruciya da rashin kunya sarki Wudar yace “Ba yallab’ai ba, ki kirani da mijinki.”

 

Rintse ido tayi ta yatsina fuska kamar ta ga ba-haya tace “Yallab’ai?”

 

Amsa mata yayi da “E mana, ba kin min alk’awarin aure ba, alk’awari kuma a wurinmu tamkar d’aura auren ne.”

 

S’an safe gaban goshinta tayi tace “Yallab’ai kana lafiya? Ya d’anka?”

 

Wani abu ya ji a zuciyarshi saboda tambayar d’anshi da tayi, amma sai ya share yace “Ina lafiya, ke fa?”

 

Jinjina kai tayi tace “Ina lafiya, nagode.”

 

D’oraw yayi da “Kin tabbatar kina lafiya? Babu wani abu daya faru?”

 

Amsawa tayi da “E yallab’ai.”

 

Jinjina kai yayi yace “Shikenan, yanzu ya maganar alk’awarinmu?”

 

A tak’aice cikin jin ya fara hawa mata kai tace “Zamuyi magana, zan sake kira anjima.”

 

D’if ta yanke kiran tana jan tsaki a zuciyarta tace “Kaga jaraba, me zanyi da kai ni kuma tsofai tsofai da kai.”

 

K’arasawa tayi ta shige ita ma ta samu hadimar bakin k’ofa tana jiranta, tana zuwa ta kalleta tace “Ki kaini wajen sarki.”

 

Da sauri ta kalketa jin wai ki kaini wajen sarki, rusunawa kawai tayi ta nufi hanyar da zata sadasu da shi d’in gabanta na fad’uwa dan bata san me zai mata ba idan har baya buk’atar ganin kowa ta kuma rakata gareshi d’in.

 

Saida suka jira a bakin k’ofar wani dogari ya musu iso, jim kad’an ya dawo ya ba wa Ayam d’in umarnin shiga abisa yarjewar sarkin, tana zura k’afarta akan wani mahaukacin tattausan carpet ta lumshe ido, wani irin sanyi ne ya ratsata tare da ni’imtaccen k’amshi ga wani irin shup shup da d’akin yayi, tana k’arasa shiga ta wara ido tana kallon ko ina, a take idonta suka hasko mata hoton mutanen da ta gani yanzu, wanda dayawa daga ciki kana kallonsu zaka san talauci ya musu katutu, amma dubi irin daular dake cikin gidan sarautar nan, ka rantse da Allah arzikin duk duniya aka tara a cikin gidan.

 

Jin bata ce komai ba sai kalle kalle take yasa sarki Musail gyara zamanshi yace “Ina jinki gimbiya.”

 

Da sauri ta dawo da hankalinta kan shi tana motsa bakinta a hankali tace “Amm..Pah, dama ina so ne zamuyi magana.”

 

D’ora k’afa d’aya kan d’aya yayi ya d’auki kofin glas d’in gefenshi da abun sha a ciki kalar ja ya kurba sannan yace “Ina jinki, zauna.”

 

Inda ya nuna mata ta zauna ta kalla sannan ta kalli kofin daya aje gefenshi, kai tsaye dai bata ce barasa bace, amma dai ta d’an ji tana shakku duba da kwalbar data gani zungureriya a ajiye, a hankali ta k’arasa ga kujerun na alfarma royal da kula k’irar Italy, zaunawa tayi kamar akan k’aya sannan ta kalleshi, ganin ya sakar mata murmushi ya sa ita ma ta saki murmushin.

 

Da fara’a ya sake fad’in “Fad’i mana gimbiya ta, ina jinki.”

 

A nutse cike da kunya ta fara alama da hannunta tana fad’in “Pah dama magana ce akan mutanen da suka zo gani na, sun zo da buk…”

 

D’aga mata hannu yayi yace “Gimbiya Zafeera, su ba mutane ne kamar kowane ba, talakawa zaki ce idan kina so na gane, ki dinga banbantawa.”

 

Baki sake ta kalleshi sai kuma ta jinjina kai tace “To Pah, dama shi ne suka fad’a min ruwa ma da suke sha su talakawa siya suke, bayan kuma d’aya daga cikin magabata ne suka samar musu da su dan su sha kyauta, amma yanzu wasu ne suka mayar da hakan kasuwanci.”

 

Irin kallon daya tsareta da shi yasa ta sunkuyar da kai, a dak’ile yace” Yanzu da kike fad’in duk wannan, me kike so na yi a kai?”

 

Cikin rawa da jikinta ya fara na tsoronshi da kwarjini yasa ta d’an muskuta tace” E to…ina ganin…idan..”

 

Sake d’aga mata hannu yayi yace” Dakat Zafeera, wa ya kitso miki duk wannan tsirfar da kika zo yanzu kike kora min? Yaushe kika zo nan d’in da har kika fara fahimtar matsalolin mutanen garin nan? Me kika sani? Me kike tunanin zakiyi?”

 

Yunk’urawa yayi ya mik’e tsaye tare da nunata yace “Kina ji ko, ba neman matsala bace ta kawoki nan, kin zo had’uwa dani ahalinki ne ba had’uwa da k’orafe k’orafen jama’ar gari ba.”

 

Komawa yayi ya zauna tare da nuna mata k’ofa yace “Zaki iya tafiya.”

 

Kamar zata fashe da kuka ta ske kallonshi tace “Pahh…ka ce zan had’u da Mah, kuma na ga har yanzu…”

 

Cikin jin haushi da tsawa yace “Kai! Wai me yasa kike da shan kai ne? Dama haka kike? Haka banzayen bayin nan suka raineki ko? Ki wuce ki bani wuri idan nasa an fito da ita zan sa a kiraki.”

 

Mik’ewa tayi tsaye ta kalleshi, ita bat1 gusa ba ita bata sauke idonta ba, k’ura masa ido tayi tana kallo kamar mai son tsaorata shi.

 

Wani d’ar d’ar ya fara ji zuciyarshi na yi har da harbawar da baisan dalili ba, sai ga sarki Musail a gaban ‘yarsa yana ta sissine kai, yana so dole ya kalleta ido cikin ido ya daka mata tsawa ta bashi waje, saboda ya nuna mata iko da izzarshi, amma kuma wani tasiri dake cikin idonta da suka ninka na shi kwarjini yasa dole yake kakkawar da na shi kamar mai jin kunyarta, gaba d’aya sai ya duburburce ya rasae zaiyi.

 

Ayam ma data fahimci haka sai ta ji ba dad’i ganin yanda mahaifinta ke mata, gyara tsayuwarta tayi tare da d’auke idonta daga kan shi, sanyaya murya tayi a nutse cikin ladabi tace “Ina so a fito min da sarauniya Juman, na zo ne dama saboda ita kuma idan na tabbatar da abinda nake son tabbatarwa zan bar nan da ita, ba sarautarku ta kawoni nan ba, saidai akwai abu d’aya da bana yarda da shi shi ne, *rashin adalci*.”

 

Juyawa tayi a tsanake ta dinga takunta har ta fita a falon na shi, yanda ya idonshi suka kakkafe ya bita da kallo kamar ya ga gawa, rufo k’ofar da akayi ne ya dawo da shi hayyacinshi, a zabure ya lalubo wayarshi dake kan d’aya k’aramin teburin gefenshi ya danna wasu lambobin, ana d’agawa sarki Musail yace “…

 

 

 

 

*Alhamdulillah*

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like
Read More

TARTSATSI 24

Advertisement *Page 24* ********************** Salma bacci yayi bacci sai faman mafalkin sadauki take, kwatsam sai tayi wani Mafalki…
Read More

TARTSATSI 62

Advertisement *Page 62*     *****************   Sadauki yayimasu sallama har zai fita ya dawo ya ciro invitation…
INAYAH
Read More

INAYAH 40

Advertisement _40_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Babban tashin hankalinsa shine a yanayinda babyn Nan take ciki bazai iya bada ita ga…
INAYAH
Read More

INAYAH 22

Advertisement _22_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Lokaci ya tafi sosai dan tuni maganar aurenta da Faruk ta Gama kammaluwa aka saka…