Lu’u Lu’u 25

Advertisement

*25*

 

Waziri Khatar na d’agawa sarki Musail yace “Ka bayar da umarni a fito da Juman, a fito da ita yanzu yanzu.”

Hankali tashe Khatar yace “Yallab’ai ka tabbatar? Wani abu ne ya faru?”

Cikin fad’a yace “Idan ban tabbatar ba na kiraka, na ce ka fito da ita yanzun nan.”

Da sauri ya amsa da “To yallab’ai, yanzu kuwa.”

Aje wayar yayi yana sake rarako idonshi yana tuna abinda ya faru tsakaninshi da Ayam, girgiza kai yayi yace “Kai ina! Hakan ma ba zai faru ba, ba zan tab’a yarda da wannan ba.”

Tana komawa d’akinta ta samu hadiman nan suna jera mata kaya da aka siyo mata daidai ita, falo ta zauna zuciyarta cunkushe saboda rashin jin dad’in abinda ya faru tsakaninta da mahaifinta, ta jima zaune ita kad’ai tana tunanin nan kafin hadiman su fito suka durk’usa gabanta d’aya tace “Gimbiya an gama shirya kayan, ko da wani abu da kike da buk’ata?”

Girgiza kai tayi tace “Ba komai, nagode, zaku iya tafiya.”

Kallon juna sukayi da mamakin jin ta musu godiya, wanda da Zafreen ce saidai ta bisu da tsaki ta musu alama da hannu su fita, mik’ewa sukayi suna fad’in sun barta lafiya kafin suka nufi fita.

Advertisements

Kallonsu tayi suna daf da ficewa tace” Ya maganar wacce ta rasu? Anyi jana’izarta?”

A ladabce ta k’arshen tace mata” Yallab’ai sarki ya sa a kai gawarta ga iyayenta.”

Da d’an mamaki tace” Ina kenan?”

D’aya a ciki ne tace” Nan baya kad’an, mafi aksari iyayenmu sunyi aiki a nan kafin su daina mu kuma mu ka d’ora, to mai akwai babban filin da aka gina musu suke rayuwa anan.”

Da alamar tambaya tace” Kenan a gidan nan babu wanda ya je jana’izarta?”

A hankali wata ta girgiza kai tace” Gaskiya sarki bai bamu wannan izinin ba.”

Jinjina kai tayi tace” Shikenan, d’aya a cikinku sai ta rakani na je.”

Zaro ido sukayi suka kalli junansu, wacce ta rakata d’azun ce tace” Ranki shi dad’e ki rufa mana asiri.”

Fuskarta ba alamar wasa tace” Asirinku a rufe yake, zaman lafiyarku d’aya shi ne muje d’aya a cikinku ta rakani.”

D’aya a ciki kamar zatayi kuka tace” Ranki shi dad’e idan har ya zama dole ki tafi dole mu dukanmu zamu rakaki, sarki ya umarcemu mu kasance tare da ke a ko ina.”

Mik’ewa tayi tsaye tace” To ai sai mu tafi.”

Wacce suka tafi tare ce ta sake fad’in” Duk da haka akwai dogarai da aka ware dan rakiyarki.”

Advertisements

Murmushi tayi ta girgiza kai tace” Ko ma menene dai mu tafi.”

Ita ma kan ta murmishin tayi kafin suka shiga take mata baya har suka fita falo.

A falon suka had’e da Zafreen ta fito ita ma da masu take mata baya alamar fita zatayi, a wulak’ance ta bisu da kallo kafin ta tambayi hadiman da cewa “Ku kuma ina zaku tafi?”

Cikin ladabi d’ayar tace “Zamu raka gimbiya ne babban gida.”

Yatsina fuska tayi tace “What? Babban gida kuma? Me zatayi a can?”

Girgiza kai Ayam tayi tana murmushi tace “Aunty gimbiya ni na ce su rakani, zan je ta’aziyar d’aya daga cikin hadiman da aka rasa da sfiyar nan.”

Wani malalacin murmushi tayi tace “Ke kuma kalar zubar mana da mutumcin da zakiyi kenan? Me ya had’aki da talakawan nan? Me zaki je ki musu har inda suke rayuwa?”

Girgiza kai Ayam tayi tana mamakinta tace “Ko na fad’a miki ba zaki fahimta ba, amma a tak’aice su ma mutane kamar mu, dan bamu fi su da komai ba.”

Tana gama fad’a ta nufi hanyar fita ba tare data sake ji daga Zafreen d’in ba wacce ta bita da kallon mamakin furucinta da kuma jin haushi.

Yanda ta buk’ata haka ya faru, ta isa babban gidan wanda ke da babban filin tsakar gida sai d’akuna a jejere ba adadi, mutuwar da akayi kuma ita tasa kowa na gidan ke waje wasu zaune wasu tsaye suna kallon gawar da aka shinfid’e iyayen yarinyar suna kanta suna kuka da fad’in shikenan sun rasata.

Kusa da su Ayam ta zauna ita ma ta share ‘yar k’wallarta kafin ta shiga jera musu ban hak’uri da fad’in yanda abun ya faru, sosai hakan ya faranta ran iyayen da ma duk wanda suke cikin gidan, dan ko shekara talatin ka b’ata kana ma sarki bauta yau ka mutu ko jaje ba zai yi wa wanda abun ya shafa ba.

Saida aka d’auki gawar dan kai ta gidan kad’ai Ayam ta bar wurin tare da abokatafiyar, suna shiga masarautar daf da k’ofar shiga falon wata hadimar ta ha’de dasu, a ladabce ta sunkuya tace “Ran gimbiya ya dad’e, mai martaba ne ya ce ki zo sarauniya ta iso.”

Da sauri ta kalleta tace “Ta iso? Tana ina? Muje.”

Da sauri ta shiga ciki suka rufi bayanta, rasa hanyar da zata nufa tayi hakan yasa hadimar nan fad’in “Nan ne gimbiya.”

Da sauri kamar zata tashi sama ta bita suka shiga haura matakalar da gudu gudu, saida suka kai k’ofar d’akin sai kuma ta tsaya turus, bud’ewa aka yi hadimar ta kalleta tace “Shiga ranki shi dad’e.”

Kallon k’ofar tayi dake bud’e kad’an, a hankali ta fara d’aga k’afarta tana shiga ciki idonta tsaye wuri d’aya, jin an rufo k’ofar daga baya yasa ta saurin juyawa hakan ya tabbatar mata lallai an rufe k’ofar, sake juyowa tayi gabanta tana mai baza idonta tana son ganin ta inda zata fito.

Sauti tashin muryoyi taji daga wata mashigar,a hankali ta fara takawa zuwa ciki wanda labule ne ya musu shamaki, tana zuwa ta d’aga labulen sai kuwa mutanen suka bayyana, hadimai ne uku da jakadiyarta sai sarauniya Juman tsakiyar su suna caje mata kai bayan tayi wanka tsabar wahalat data shawo a gidan kurkukun nan.

Jin shigowar mutum yasa su ma suka juya, suna ganin Ayam suka kama jikinsu suna mata barka da zuwa, mik’ewa Juman tayi a sanyaye ta juyo gaba d’aya ta zuba mata ido, ido cikin ido suka kalli juna yayin da a tarz sak’on ya isa ga zuciyoyinsu cewa lallai alak’ar mai k’arfi ce wacce ta isa su kira junansu da mai haihuwa da wacce aka haifa.

Ayam data kasa motsawa Juman ce ta shiga d’agowa a hankali tana tunkarota tana k’ara gyara k’aramin towel d’in dake kafad’arta duk gashinta ya kwanta a kai, saida ta tsaya gabanta suka kallon juna, cikin sanyayyar murya Juman tace “Kamar jaririyar ‘yata dana kalla sau d’aya tak a rayuwa?”

Kamar ambaliyar ruwa haka hawaye suka fito daga kurmin idon Ayam suna sauka a kumatunta, cikin muryar kuka ita ma a tausashe tace “Ba zan iya tuna kamannin fuskar ba, dan ban tab’a ganinta ko a mafarki na ba, saidai duk da haka hakk’in haihuwa ne ya jawoni zuwa nan dan tabbatarwa da kai na mahaifiyata na neman taimako na.”

Sark’ar wuyanta ta jawo ta nuna mata tace “Da gaske ke ce kika saka min wannan a wuyana tun ina k’arama?”

Jinjina mata kai tayi ita ma tana kukan tace “Tabbas ni na d’aura miki ita da hannu na a lokacin dana haifeki.”

A hankali tace “To amma me yasa?”

D’an murmushi ta k’ak’aro tace “Saboda ta zama tsaro a gareki, sannan shaidar da zan iya ganeki ko a cikin dubu, sannan hujjar da zan iya nuna miki cewa ni na haifeki.”

Fashewa tayi da kuka mai ban tausayi ta saki sark’ar daga hannunta tace “Me yasa kika rabani da ke a lokacin da na fi buk’atarki? Me yasa kika zab’i kiyi nesa da ni a sanda zamanmu a tare shi ya fi komai mahimmanci?”

Da sauri Juman ta saki towel d’in take rik’ewa hakan ya bayyanar da wuyanta dan d’aurin k’irji ne jikinta na farin towel babba, rumgumeta tayi tsam a jikinta suka fashz da wani sabon kukan, cikin magiya take fad’in” Kiyi hak’uri ‘yata, ban yi haka dan bana sonki ba, da banyi abinda nayi ba da yanzu ba kya raye, idan kuma kin rayu to da kin sha wahalar da ni kuma ba zan juri ganin kina shan ta ba, shiyasa nayi nesa dake dan ki rayu cikin aminci, sannan ki zama mai kyawun d’abi’a da ba irin na mahaifinki da ‘yar uwarki ba.”

K’am k’am Ayam ta rik’eta tana sauke ajiyar zuciya da fad’in” Na fahimta Mah, na fahimceki Mah na.”

D’agota tayi daga jikinta ta kalli fuskarta ta hanyar d’aga hab’arta tace” Kin yafe min kenan?”

Langab’e kai tayi tace” Ban rik’eki ba Mah, ina sonki sosai.”

Ta fad’a tana sake komawa jikinta, ita ma matseta ta sake yi tana murmushi, daga bayansu jakadiyar sarauniya Juman ce tace” Ranki shi dad’e na fito miki da kayan da kika buk’ata.”

Cikin shagwab’a da sangarta Ayam ta bud’a ido ta kalli jakadiyar tace” Babu mai rabani da Mah ta, anjima ta saka.”

Dariya jakadiyar tayi haka ma Juman data d’agota daga jikinta tace” Sai yaushe kenan? Nayi ta zama a haka?”

Rik’o hannayenta Ayam tayi tana mamatsawa musamman ruwan zafi’ da tayi wanka da su yasa duk fatarta tayi taushi saboda rashin samun lafiyayyar shinfid’a a kurkukun nan, cikin shagwab’a tace” Mah, zaki zauna tare da ni ko? Akwai abubuwa dayawa da nake son tambayarki, ina rok’onki ki zauna tare da ni kuma ki amsa min, dan babu mai fad’a min gaskiya har yanzu.”

Jawo hannunta tayi ta zaunar da ita bakin gado sannan ita ma ta zauna, kallon jakadiyar tayi tace “Ku je jakadiya, zan nemeki anjima, yanzu lokacin ‘yata ne.”

Rusunawa sukayi tace “To sarauniyata, mun barku lafiya.”

Dukansu suka fita kafin sarauniya Juman ta maida hankalinta kan Ayam tana murmushi tace “Ya kika rayu ba tare da ni ba?”

A take tace “Cikin aminci, k’auna da soyayya.”

Jinjina kai tayi tace “Kin tabbatar kin rayu babu barazanar talauci?”

Girgiza kai tayi tace “Babu Mah, sun ciyar dani da dad’i da ba dad’i, sun d’auki nauyin karatu na har zuwa sanda gwamnati ta d’auke musu nauyin, sun tufatar da ni iya iyawarsu.”

Jinjina kai ta sake yi tana k’asaitaccen murmushi kafin tace “Game da lafiyarki fa? Babu abinda ke damunki?”

Girgiza kai tayi kafin tace “Babu Mah, idan da akwai ciwon dake damuna bai wuce yawan mafarkai ba tun ina k’arama, shi ma yanzu kuma na fahimci wa nake gani a mafarki na.”

Cikin zolaya ta lak’aci hancinta tace “Wa kike gani haka? Ko dai sirikin na wa ne?”

Dariya tayi tana rufe fuskarta da tafin hannu tace “Lahhh! Mah ki daina.”

Dariya tayi ita ma kafin tace “To fad’a min wa kike gani?”

Bud’e fuskarta tayi ta d’ago tace “Ke ce Mah, ke nake gani kullum kina neman taimako na, bansan me hakan ke nufi ba?”

Numfasawa tayi ta rik’e hannunta gam suka kalli juna, a sanyaye tace “Ayam…”

Da mamaki ta kalleta da sauri kuma tace “Ya akayi kika san sunan dana tashi ina amsawa? Tunda na baro Larhjadin yallab’ai Umad ne kad’ai ke kirana da sunan.”

Dariya tayi har saida hak’oranta suka bayyana sannan tace “Saboda ni na fad’awa Habbee ta rad’a miki sunan *Ayam*, sunan dake birgeni kenan tun da jimawa, na so sakawa yar uwarki Zafreen, amma sai mahaifinku ya zab’a mata sunan Zafreen.”

Dafa kafad’arta tayi tace “Mafarkin da kika kasance kina yi ni na fara yin shi na tsawon lokaci, amma ina haihuwarki komai ya wuce.”

K’asa tayi da kan ta tana sakin murmushi tace “Umad? Umad?”

Sai kuma ta kalli Ayam tace “Ta ya kika san Umad? D’a ga sarki Wudar.”

Da mamaki ta kalleta tace “Ya akayi kika san shi Mah?”

Sosai tayi murmushi kafin ta kalleta tace “Yanzu dai ki bari na saka kaya, daga baya zamuyi magana bayan na ci abinci.”

Kyab’e fuska tayi ta ware hannayenta ta rumgumo Juman d’in tare da fad’in “Mah bana so kiyi nesa da ni ko na sakan d’aya, please ki zauna tare da ni.”

D’ago hab’arta tayi tace “Wai tsaya ban tambayeki ba, ta ya kika iya yaren slovaque? Su Habbee ne suka koya miki?”

Girgiza kai tayi a harshen larabcin parsi tace “Ko d’aya Mah, kawai dai na iya ne saboda ni yar garin nan ce asali.”

Da mamaki ta waro idonta tace “Hada yaren k’asar haihuwata ma kin iya?”

A harshen faransanci tace “Oui m猫re (e mahaifiya ta).”

D’aga hannaye tayi ta dafe kanta tace “Tsaya tsaya! Wai me ye haka? Ta ya kike yaren nan a bakinki?”

Zaune tayi da kyau tace “Ki je ki kammala duk uzurinki, sai muyi magana daga yanzu har wata safiyar.”

Kallon tuhuma sa kuma tsoro ta mata tace “Kin tabbatar?”

Jinjina mata kai tayi tace “Na tabbata.”

Mik’ewa tayi ta nufi wajen kayan da aka fito mata da su ta shiga k’ok’arin sakawa, Ayam duk na zaune tana kallo ta shirya a tsanake babu mai cewa komai, saidai jefi jefi sukan kalli junansu suyi murmushi, kowa na jin zuciyarsa na masa wani iri game da d’an uwansa.

Har ta gama shiryawa ta nufi wajen zaman mutum biyu gaban teburin da aka jere mata abinci mai rai da lafiya, kallon Ayam tayi ta mata alama da hannu ta taso, mik’ewa tayi ta nufeta ta zauna kusa da ita, zuba abincin tayi sannan ta kalleta tace “Mu ci.”

Da fara’a ta tsoma hannunta ba cokali ba ta d’ebo loma ta nufi bakin Juman, da fara’a ita ma ta bud’e bakin ta saka mata, ita ma d’iba tayi ta saka mata hakan yasa su sakin murmushi.

Cikin farin ciki da jin dad’i da annashuwa suka dinga ciyar da junansu amma ba hira suke ba sai k’orafin da suke wa junansu na sun k’oshi, amma a haka Juman zata sake jefa mata loma a baki, sai ita ma tace sai ta rama haka har suka cinye wanda suka zuba a farantinsu.

 

*Alhamdulillah*

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like
KALLABI
Read More

KALLABI 59

Advertisement BABI NA HAMSIN DA TARA “Sakarai dalla matsa min, kasan waye shi? Idan ya dawo masarautar nan…
A BAKIN WAWA 3
Read More

A BAKIN WAWA 16

Advertisement 16 Gefen takardun ya zauna sannan ya kalleta yace’ Mahmud or Muhammad, Bata bashi amsa ba taci…
Read More

TARTSATSI 74

Advertisement   *Page 74*   Yana nan azaune yana tunanin miye hakan kuma, wari Salma ina bazaiyiyu ba,…

KALLABI 56

Advertisement BABI NA HAMSIN DA SHIDA Cikin wani irin azababben zafin nama yake yakar su, kamar ba bako…