Advertisement
*26*
Suna kammalawa basu bi ta kan kwanukan ko gyara wurin ba suka koma kan gadon nan, tsakiyarshi suka haye suka tank’washe k’afafunsu hannayensu sark’e dana juna suna kallon juna, cikin nutsuwa da fara’a sarauniya Juman tace “Yanzu fad’a min, me kike son sani?”
Cikin nutsuwa tace “Mah, ina so nasan *wacece* ni?”
D’an murmushi tayi tace “Wacece ke kike tambaya Ayam?”
Jinjina kai tayi tace “E Mah, ina so na sani.”
Jinjina kai tayi ita ma ta nisa sannan tace “Ayam, ke ‘yata ce dana haifa a ciki na, kafin haihuwarki kuma malam Dhurani ya fad’a min ke mai baiwa ce da zaki zo bayan magabatan da suka shud’e masu irin baiwarki, na raini cikinki har na tsawon wata tara cike da kulawa da nuna miki k’auna, haka kuma mahaifinki na d’aya daga cikin wanda suka tayani kulawa da ke, haka muka ci gaba da rainonki har sanda cikinki ya isa haihuwa, saidai duk tattali da burin da muka ci na haihuwarki, haka ina ji ina gani sanda na haifeki ko wankan farko ba’a miki ba na mik’aki a hannun jakadiyata ta tafi dake.”
Da mamaki fal a fuskar Ayam tace”Me yasa Mah? Gashi dai a labarinki na fahimci Pah ma yana so na, amma kuma sai ake cewa wai yana son kasheni?”
Numfashi ta sauke a hankali tace “Ayam, lokacin da cikinki ya kai wata shida, wata ranar alhamis da ba zan tab’a mantawa ba jakadiyar sarki ta zo min da wata magana, lokacin da sarki mahaifinki yayi bak’i ta je sanar dashi, anan ta ji wata tattaunawarshi da malam Dhurani suna maganar cewa ke d’in da zaran an haifeki to su gaggauta kasheki, idan ya so sai su samu wata jaririyar su damk’a min a matsayin wacce na haifa, jin wannan labarin ya tayar min da hankali sosai, saidai ban k’aryata jakadiya ba saboda tsufanta da kuma wasu alamomin da suka dinga bayyana min a game da sarkin, wasu lokuta ya kan furta zancen zuci a gaba ya fad’i wata mummunar kalma a kanki, wasu lokuta kuma idan ya sha giyarsa cikin dare na nemi taimakonsa kan wani abu sai ya dinga fad’in *banzan cikina* yana surutai, hakan yasa na ci gaba da saka ido akan shi ina masa kallon biri yana min kallon ayaba.”
Nisawa tayi sannan ta d’ora da” Tunda na fara nak’udarki sarki Musail yake tsaye a kai na shi da malam Dhurani da wazirinsa Khatar, da k’yar ya fita ya bar likitar gidan nan da jakadiyarsa suka dinga taimaka min, k’arfe 11:59 na ji kukanki bayan k’akk’arfan nishin da nayi, wanda kukanki ya dira a kunnuwana tare da sautin bugawar agogo k’arfe 12:00 ta buga na sabuwar shekara, babban abinda ya firgita ni a lokacin shine yanda mahaifinki ya banko k’ofar d’akin yana son a dole a bashi ke ya rik’e, hakan ya k’ara tabbatar min da abinda nake zargi ya kuma tsorata ni sosai.”
Advertisements
Kallonta tayi ido cikin ido ta sake jinjina hannayen Ayam d’in dake hannayenta tace” Ayam, b’atanki ba shiryayyen abu bane kamar yanda kowa ke zato, a daidai wannan lokacin na rok’i jakadiyata Habbee data gudu dake zuwa wani wuri mai nisa, sannan na umarceta data nemi taimakon mijinta akan hakan, saida na kori jakadiyar sarki na c ta had’a min ruwa, lokacin likitar ma ta bar d’akin sannan na lallab’a Habbee, da k’yar ta amince dan abun bazata ya zo mata, bayan ta amince ne na samu damar mik’a mata ke bayan na sumbaceki, har zata bi ta wannan k’ofar da kike gani…”
Ta fad’a tare da nuna mata drower ta litattafai sannan ta d’ora da fad’in” K’ofar sirri ce a bayan nan d’in, wacce a d’akin sarki da iyalensa ake samunta saboda kaucewa farmakin magauta na bazata, to ta wannan hanyar Habbee ta fita dake a wannan daren bayan na d’aura miki wannan sark’ar wacce sarkin k’asar Khazira ne kawai ke d’aurawa wacce ya aura, sannan na bata kud’in da zasu kula da kansu har su kula da ke kanki ma, wannan ita ce Ayam d’in da kike son sanin wacece.”
A tare suka sauke numfashi inda Ayam idonta ke fitar da ruwa masu d’umi muryarta na rawa tace” Mah, kenan dai da gaske mahaifina yana neman rayuwata? To amma me yasa?”
Sakin hannunta d’aya tayi ta share mata hawayen da suka zubo tace” Kiyi hak’uri Ayam, haka ta ki k’addarar take, hak’ik’a a yanda komai ya fito mana mahaifinki yana son kasheni, kuma ba komai ya kawo hakan ba sai dan ci gaba da kasancewa a kujerar mulkinsa wacce babu komai a ciki sai tarin zalinci da tauye hakk’in jama’a.”
Marairaicewa tayi tace” To amma Mah ke ma kin yarda ina da wata baiwa wacce har mahaifina zai so kasheni saboda ita?”
Girgiza kai tayi tace “Ba zan ce komai ba a yanzu, saboda ban girma dake ba bare na fahimci me ce ce baiwarki, amma dai nasan akan haka mahaifinki ke neman rayuwarki.”
Kyab’e fuska tayi tace “To amma Mah, me yasa ba yar uwata bace aka haifa da baiwar nan? Tunda ita kuka fara haihuwa ko.”
Murmusawa tayi tace “Saboda ke ce ubangiji yake son gani a haka.”
A marairaice ta sake fad’in “Mah, su waye mutanen nan da suka fara fad’a min wacece ni?”
Da mamaki ita ma tace “Su wa kenan?”
Jim tayi alamar tana tunani sai kuma tace “Yawwa Bukhatir, sunansa Bukhatir a k’asar Egypt.”
Mamaki ne ya sake bayyana a fuskarta ta k’ank’ance idonta tace “Bukhatir ya had’u dake kenan?”
Advertisements
Jinjina kai tayi tace “E, wata safiya ce dana fito daga wanka saboda jin motsin da na ji, daga nan ban san me ya sake faruwa da ni ba tun buguna da akayi a kai sai bud’ar ido da nayi na ganni a gidansa.”
A hankali ta dinga gyad’a kanta alamar jinjina abun da kuma gamsuwa kafin tace” Tabbas zai iya aikata komai, fatana kawai Allah ya kareki daga sharrinsa.”
“Waye shi Mah?” Ta fad’a a sanyaye, d’an yak’e ta mata kafin tace “Ayam Bukhatir d’an uwana ne, mahaifina shi ne gaba da mahaifinsa, ni kad’ai ce ‘yar da suka haifa mace bayan shekarun da suka share a tare babu haihuwa, mahaifin Bukhatir mutumin kirki ne wanda mulkin yayansa baya gabansa, saidai Bukhatir tun yana k’arami yake sha’awar mulki, sanda suka haifeni sai ya yarda lallai idan na girma zan iya hawa kujerar mahaifina, saboda kuwa mu a wajenmu mace ma tana yin mulki sai idan bata buk’ata, bayan wani lokaci Bukhatir ya zo min da tayin soyayyarsa, amma ban karb’a ba saboda bai min ba, bana sha’awar mulki kuma bana son mai tsananin son mulki.”
Da mamaki Ayam tace” To Mah e yasa ya saceni ya kaini gidansa? Guduwa fa na yi bai sani ba, sanda na fahimci babu hankalin kowa a kai na na wa hadiman daya had’ani da su dabara na shige boot d’in motar bak’in da suka zo masa a lokacin.”
Girgiza kai tayi tace” A gaskiya ban sani ba, ban san dalilin da yasa ya saceki ba,saidai nasan lokacin da mahaifinki ya nemi aurena sun samu matsala har sukayi musayar yawu, watak’ila ko akan hakan yake son rama wani abu da aka masa.”
A hankali tace” To amma Mah, idan har kunyi soyayya irin haka da mahaifina, me yasa ya manta da komai ya jefaki a magark’ama saboda ni?”
Dariya Juman tayi har saida hak’oranta sirara masu kama dana Ayam d’in suka bayyana, girgiza kai tayi tace” Ayam kenan, yarinya ce ke har yanzu.”
Da mamaki tace” Kamar ya Mah, ni fa na girma.”
Ta fad’a tana kumburo baki, dariya ta sake yi tace” Ayam ba haka abun yake ba, a shekara ta 1985 sarakunan gargajiya sunyi taro na musamman dan sake hab’aka zumunci da kawar da bambamce bambamce a tsakanin k’asashen, sarkin Egypt wato mahaifina, da sarkin Khazira wato mahaifinki, da kuma sauran sarakuna daga ciki har da sarki Wudar na Giobarh, duka sun hallara a wannan babban taron wanda mahaifina shi ne mai alhakin sauke bak’in, ma’ana a k’asarmu aka gudanar da taron, kwana uku aka d’auka ana wasanni kala daban daban, a na ci a na sha cikin farin ciki da annashuwa, b’angare d’aya kuma sarakuna na gudanar da abinda ya kawosu.”
Numfasawa tayi ta d’an gyara k’afarta data tank’washe sannan ta ci gaba da fad’in” A kwana ukun da akayi na kamu da soyayyar wani d’an baiwa, kinsan me yasa na kirashi da d’an baiwa? Saboda shine zakin daya fara sace zuciyata, da kallo d’aya ya birgeni ya kuma shiga zuciyata, lokacin da nake jin dad’in satar kallonsa ina tunanin hanyar da zan fad’a masa abinda ke zuciyata kafin su bar k’asar, sai ya turo da k’aramin k’aninsa mai shekara shida a duniya ya fad’a min wai shi ma yan so na.”
Damk’e hannun Ayam tayi sosai tana jijjigawa cike da farin ciki tace” Kin kuwa san irin farin cikin da na kwana ina yi a ranar? Na ji kamar duniya aka bani da komai dake cikinta, saidai kash! Ban tab’a tunanin wannan bak’in taro ne a gareni ba saida Musail ya shigo rayuwata, ki gafarceni idan kin ji ba dad’i Ayam saboda soyayyar d’a da uba, amma dai tabbas ban ji dad’i ba.”
A sanyaye Ayam tace” Me ya faru Mah?”
Girgiza mata kai tayi tace” A’a Ayam, bana so daga had’uwarmu na zauna na yi ta fad’a miki mugayen halayen mutanen dake zagaye da ke.”
Rik’o hannunta tayi tace” Please Mah, ki daure ki fad’a min komai, na fad’a miki mutanen da ban sani ba suna kawo min farmaki ta hanyar rikita min k’wak’walwa, ina so na san komai daga gareki, hakan shi ne zai cire min kokonto na akan kowa da komai.”
Girgiza kai tayi tana sako da hawaye a idonta tace” Ba zan iya fad’a miki wannan ba Ayam, ki gafarce ni.”
Jinjina kai tayi alamar gamsuwa tace” To shikenan na ji, amma ki fad’a min waye wanda kika so a zuciyarki? Sannan ki fad’a min me ya hana aurenku?”
Murmushi tayi tace” Ayam ai idan na fad’a miki abinda ya hana aurenmu an gudu ba’a tsira ba kenan, dan abinda ya hana auren na mu shi ne abinda bana son fad’a miki.”
Jinjina kai ta sake yi tace” To na ji, waye shi?”
Saida ta saki sanyayyan murmushi tace” Sunansa *Urab*, babban d’an sarki Wudar.”
Zazzaro ido tayi tace” Sarki Wudar Mah?”
Jinjina kai tayi tace” E, d’an sarki Wudar.”
Da mamaki a fuskarta tace” Hakan na nufin yaya ne ga yallab’ai Umad? Dama ‘ya’yan sarki biyu ne?”
Gyad’a mata kai tayi tace” E, su biyu, Umad d’in ai shine k’aramin k’aninsa da nake fad’a miki.”
Juyar da kanta tayi gefe a ladabce tace” Kenan yallab’ai Umad sosai ya sanni ba sanin shanun talla ba? Kenan tabbas saboda ni ya je makarantar nan? Kuma mahaifinsa ya san wacece ni, amma kuma duk da haka yake cewa yana son…”
Shirun da tayi yasa Juman saurin fad’in” Yake son me? Kin had’u dasu dukansu? Ta ya ya?”
Girgiza kai tayi dan bata san me hakan zai janyo ba kafin tace” Ba komai Mah, na zauna tare da su na kwana biyu.”
Tsaf ta kwashe abinda ya faru ta fad’a mata, sai daga bisani kuma ta kalleta a tsanake tace” Mah, to ina shi yayan yallab’ai d’in yake? Ko gidansu dana zauna ban ji ko da labarinshi ba.”
Kallonta tayi sosai ita ma a tsanake tace” Ya rasu shekara ashirin da hud’u da suka gabata.”
Dafe k’irji tayi tamkar mahaifinta aka ce ya mutu tace” Me?”
Jinjina mata kai tayi alamar e, girgiza kai tayi kamar zatayi kuka tace “Amma ta ya Mah?”
Girgiza mata kai tayi tace “Kinga yanzu dai manta da wannan, bana so ki sa kanki a damuwa, yanzu bani labari game dake?”
“Kamar me kenan Mah?” Ta fad’a kamar mai rad’a, jan hancinta tayi tace “Kamar k’awayenki, samarinki, karatunki, matsayin addininki a gareki.”
Bushewa tayi da dariya tace “Mah, a b’angaren karatu na dai kam zan iya miki albishir da ce wa tun dana fara daga ajin farko zuwa inda nake yanzu, indai za’ayi jarabawa to ni ke zuwa farko, k’ok’ari na ma yasa har idon gwamnati ya zo kai na suka dinga d’aukar nauyina.”
Rausayawa tayi ta ci gaba da fad’in” Kawaye kuma ni kam ban da tsayayya, duk k’awayen makaranta ne, da zaran mun rabu to shikenan ni da su sai ko kan hanya idan an had’u.”
Cikin jin kunya tace” samari kuma…ban tab’a yi ba Mah, ko na wasa.”
Jin tayi shiru yasa Juman fad’in” To addininki fa? Me ye matsayinsa a gunki?”
Waina idonta tayi tace”…
*In shaa Allah sai litinin kuma*
*Alhamdulillah*
GIPHY App Key not set. Please check settings