Advertisement
*29*
Kamar jiranshi ake ya koma b’angaren shi Adah ya mik’o masa wayarshi yace “Yallab’ai ana kiranka a waya.”
Kallonshi yayi kafin ya sa hannu ya karb’a ya duba lambar da babu suna, k’arasawa yayi cikin falon ya nemi guri ya zauna tare da aje wayar gefenshi har ta tsinke, a tsanake Adah ya kalleshi yace “Ranka shi dad’e, na ga har kiran ya tsinke baka d’aga ba?”
Yatsin fuska yayi yace “Bak’uwar lamba ce.”
Cikin ladabi Adah yace “Hakane ranka shi dad’e, amma akwai yiwuwar wani mai mahimmanci ne, duba da lambarka ce ta manyan mutanenka.”
Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce wani abu sai kiran ya gajeren sak’o ya shigo wayar, kallon Adah yayi yace “Duba ka gae aka ce.”
D’auka yayi ya duba kamar yanda ya ce, da sauri ya kalleshi yace “Yallab’ai, *Abraham Joshua* ne fa, komishinan kud’i da kake shirin yanda zaku tattauna da shi.”
Da sauri ya zura hannu ya karbi wayar yana k’ok’arin maida kiran yana fad’in “Ka tabbata? Abraham Joshua?”
Kiran da ya sake shigowa yasa sarki Musail kallon wayar, jim yayi bai d’aga ba na yan dak’ik’u, daga bisani kuma sai ya d’aga, Adah na gefe yana kallonshi jin yanda suke gaisawa kamar sun san juna dama, bayan gaisuwar ne Abraham ya d’ora da “Ranka shi dad’e sarki na, dama wata muhimmiyar magana ce ta sa na kiraka.”
Advertisements
A tsanake shi ma ya amsa da “Muhimmiyar magana kuma? To ina jinka, Allah yasa dai lafiya?”
Da fara’a yace “Ah lafiya lau, dama d’an waje na ne ya ke fad’a min ya ga d’aya daga cikin ‘ya’yanka kuma ya na so.”
Shiru yayi daga haka na dak’ik’u sannan ya d’ora da “To na amince masa ya nemi aurenta a wajenka, saidai ya cika sauri dayawa, da na fad’a masa zamu je tare nan da kwana biyu bayan na dawo daga tafiya, sai ya nuna bai yarda da hakan ba, ‘ya’yan manya a kowane lokaci farautarsu a ke, dan haka ya ce shi zai fara zuwa a yau, ni sai na zo daga bayan.”
Numfasawa yayi sosai sannan yace” Fatan dai ba muyi gaggawa ba ranka shi dad’e?”
K’urawa Adah ido yayi yana kallo tare da shiga kogin tunani, hark’allar da yake son k’ullawa da kwamishinan kud’in ta isa ta sa ya amince masa, dan haka ya d’an murmusa yace” Ok, wannan ai ba matsala ba ne, ya zo kawai, nan ma kamar gidan su ne.”
Numfashi ya sauke kusan sau uku kafin yace” Amma…wace a cikin gimbiyoyin na wa?”
A hankali yace” E to…ina jin dai kamar k’aramar.”
Jim sarki Musail yayi sai kuma ya tab’e baki a ranshi yake fad’in” Idan ta zama gawa kafin nan sai a maida auren kan gimbiya Zafreen.”
A zahiri kuma murmushi yayi ya amsa da ba komai kawai sai sun zo, har da tagomashin fad’in” Zan tura dreba ya je ya d’aukoshi.”
Da sauri Abraham yace” Yallab’ai sai dai ba shi kad’ai ya taho ba, tare yake da mai tsaron lafiyarsa.”
Jinjina kai Musail yayi yace” Wannan ba damuwa bane, ko su na wa zasu zo akwai masaukinsu.”
Suna Ida wayar ya kalli Adah yace” Ka kula da komai Adah, ka tura dreba ya d’aukosu a filin jirgi, sannan ka sa a shirya musu tarba ta musamman, dan neman aure zasu zo.”
Advertisements
Da sauri Adah ya kalleshi cikin ladabi yace” Ranka shi dad’e a gafarce ni, amma neman auren wa daga cikinsu?”
Ba tare daya kalleshi ba yace” Zafeera.”
Da mamaki yace” Zafeera kuma? Ranka shi dad’e wacce muke shirin turata wata duniyar, me ye hikimar yin hakan?”
Wani lallausan murmushi yayi yace ” Ka zuba ido kawai ka sha kallo.”
Rusunawa yayi ya jinjina kai tare da fad’in” Na barka lafiya sarkina.”
*Suna* zaune d’akin Juman hadimai biyu suka shigo da farantan abinci, Ayam dake duba zoben da Juman ta nuna mata na azurfa wanda ta ce Urab ya bata shi, ajeshi tayi kan k’aramin teburin, suna zuwa su ma suka aje kwanukan akan teburin, a tsanake Juman ta kallesu tace “Me aka dafa yau?”
Cikin ladabi d’ayar ta shiga bud’e mata kwanukan dan ta gani da idonta, murfin kwanan ta aje a k’asan zoben, hakan yasa Ayam data gani tace “Mik’o min zoben nan?”
D’aukowa hadimar tayi ta mik’o mata, karb’a tayi saidai sub’utar hannu yasa zoben sub’ucewa ya fad’a cikin farfesun kifin da ke kusa, da sauri Ayam ta furta “Oh Allah.”
Da sauri hadimar ta d’auki cokali tana fad’in “Oh! Sannu gimbiya, bai fallatsar miki ba?”
Girgiza kai tayi tace “A’a, ki gaggauta ki ciro shi.”
Cokalin ta sa ta d’auko zoben nan na azurfa, abun mamaki ya canja kala yayi bak’i sid’ik, sam Ayam bata fahimci me sauyin zoben ke nufi ba, amma Juman da ta san komai tuni ta mik’e tsaye tana dafe da k’irjinta tace “Inna lillahi wa’inna ilaihi raju’un.”
Kallonta Ayam tayi tace “Mah, me ya faru? An ciro shi ai.”
Hankali tashe tace “Ayam baki gani bane? Guba ce a abincin nan.”
Zabura tayi ita ma ta mik’e tsaye tace “Guba kuma? Ta ya mah?”
Nuna mata zoben tayi da hannun hadimar har ya fara rawa tsabar kad’uwa tace “Dubi zoben mana ki gani, ya canza kala.”
Kallon zoben tayi sannan ta kalli hadiman tace “Ta ya haka ta faru? Wani ne ke sonkashe min uwata?”
Girgiza kai sukayi a tare alamar a’a suna neman fashewa da kuka, cikin tsawa Juman tace “Yanzu da ku za’a had’a baki a nemi kashe min ‘yata? Me ta muku? Wa ya saka ku? Me aka baku da ni ba zan iya baku ba?”
Kallonta Ayam tayi a nutse tace “Mah, kwantar da hankalinki.”
Kallon hadiman tayi tace “Ku d’auke abincin ku fita da shi, ku fad’a musu Allah ya fi su.”
Cikin rud’u Juman ta fashe da kuka tace “A’a Ayam, dole mu san…”
Matsawa tayi kusanta ta rumgumeta tace “Shiiii! Ya isa Mah, ki nutsu kin ji, ki bar min komai a hannu na.”
Jinjina kai tayi tana sauke numfashi ta bi hadiman da kallo da su har ga Allah basu san ta ya haka ta faru ba.
D’agowa tayi daga jikin Ayam tace “Bari na je da kai na na samo mana ko da kayan marmari ne, daga yanzu ba zamu sake yarda da kowa ba.”
Jinjina kai tayi alamar to, zaune tayi bakin gadon inda Juman ta fita a d’akin dan samo musu abin ci.
*Giobarh*
Tana kwance kan doguwar kujera da wayarta tana amsawa, cike da kissa take farfar da ido tana fad’in” Haka ni ma na yi kewarka waziri na, yanzu ka fad’a min yaushe zamu had’u?”
Daga wajen wanda ta kira waziri ya amsa da” Ina so mu had’u Joy, sai dai dole mu dinga taka tsantsan, kinsan fa abubuwa sun fara canjawa, musamman yanzu da shegiyar yarinyar nan ta bayyana garemu.”
Yar dariya tayi tace” Da alama tsoronta ya gama tasiri a zuciyarka, ai ban sanka da tsoro da sarewa ba, k’aramar yarinya ce fa? Ubanta ma ya ya iya da mu bare kuma ita?”
Jinjina kai yayi daga inda yake yace” Hakane, amma kinsan ita daban ce, a gaskiya bana iya d’aga idanu na a gaban yarinyar nan, kwarjininta ya fi na ubanta Musail, kamar…wata zakanya haka nake ji idan na ganta.”
Tsaki tayi ta tashi zaune tana fad’in” Ya isa haka malam, ya kake so ka nuna min ka fara sarewa da lamarin, kana so kace kenan mu hak’ura da burinmu?”
A sanyaye yace” Ko bamu hak’ura ba Joy do’e dai mu bi a hankali.”
A hassale tace” Ba zamu bi d’in ba, zamu tafi da gudu dan cika burinmu, ta jima ba tayi abinda za tayi ba, kar ka manta shekara ashirin da shida mun aikata abinda har yanzu babu uban daya ganemu bare ya d’aga canzan, kuma idan akwai wanda za’a zarga a ciki sarki Musail ne.”
Numfasawa yayi yace” Na san da wannan, matsalata da ke garaje, Joy hanyar da muka bi muka aiwatar da waccen tsarin, idan kika bi a hankali wannan ma haka zamuyi.”
Ajiyar zuciya ta sauke tace “Shikenan na ji, yanzu ya zamuyi da kai?”
A hankali ya amsa mata da “A game da me fa? Halan kud’i kike so?”
Yatsina fuska tayi tace “E mana, kai ma kasan ai zan buk’aci kud’i, tunda Wudar ya juya min baya saboda banzar yarinyar nan.”
Numfashi ya sauke yace “Shinkenan na ji, zan turo miki anjima, dan nasan wajenku yanzu dare ne.”
A sangarce ta amsa da “Hakane, shikenan sai na ji ka.”
Aje wayar tayi a gefe ta koma ta kwanta ta lumshe ido tana tunanin abubuwan da suka aikata masu yawan gaske ita da waziri Khatar d’in, wanda ba komai ya jawo haka ba sai soyayya, asali a makaranta suka fara soyayya a babbar jami’ar Khazira, a k’arshe sai iyayenshi suka zab’a mishi mata yayi aure, dan dama shi da ita soyayyar shan minti ce aka buga, duk da auren da yayi su kan ziyarci juna su kuma sha soyayyarsu, tsawon lokaci kuma bayan irin kitimurmurar da suka k’ulla ne na son cikar burinsu sai ta koma Giobarh wajen yayarta tana kula da ita.
Yanda ta ji an d’ora hannu a k’irjinta yasa ta zabura ta tashi zaune tan kiran “Kai! Waye…”
Sarki Wudar ne tsaye gabanta cikin saussauk’ar shigarshi ta kayan bacci, hular dake kan shi kuma ta tabbatar mata akwai abinda yake so gareta shiyasa ya shigo ta b’arauniyar hanya zuwa wajenta, had’e fuska tayi ta kauda kai daga gareshi ba tace komai ba.
Murmushi yayi tare da zaa gefenta ya jawota jikinshi yana sumbatar kumatunta yace “Oh my madam, me ya faru ne haka ake had’e min fuska kuma?”
Tureshi tayi da k’arfi cikin masifa tace “Me ma ya faru kake tambaya ta? To ban sani ba, ka ga tashi ka fita daga d’akin nan.”
Sake jawota yayi cikin dubara ya zura hannunshi kan mamanta dake babu bras a cikin rigar bacci, farin gemunshi ya fara shafa mata a kafad’a, inda bakinshi ke kan kunnenta yana rad’a mata” Haba sarauniyata, me yasa za ki fad’i haka? Ni ne fa, sarkinki.”
K’ok’arin kubcewar da tayi yasa shi sake k’amk’ameta a jikinshi, mayar da hannunshi yayi kan mararta ya shafa, tauri da kuma d’umin da take ji a wurin da neman mai tallafa mata a lokacin yasa ta lumshe ido ta sauke numfashi.
Cikin dakusashiyar murya ta furta “Me yasa ka dinga wulak’antani a kan ta?”
A hankli ya shiga sauke numfashi a cikin kunnenta ya rufe ido shi ma, a zuciyarshi ya amsa mata da “Saboda ta fiki komai a wajena, da ita zan kai matakin da babu wanda ya zata a duniya.”
A zahiri kuma cikin taushin murya yace “Kiyi hak’uri kin ji, ai yanzu bata nan.”
Cikin fad’a tace “Amma ai na ji labarin kun yi alk’awarin aure da ita, ko ka d’auka ban san me ake ba ne a gidan?”
Jim yayi da tunanin a sanda sukayi maganar nan wa ya ji? Sai kawai ya share dan yasan kad’an daga aikin gidan masarauta kenan, cikin gurnani na abinda ke damunshi wanda shi ya kawoshi nan ya sake zura hannu yana shafa mamanta yace” Rabu da kowa kinji, ki kwantar da hankali yanzu, kinsan fa ba ke kad’ai ba ce ko?”
D’ago kanshi yayi yace” Yanzu tashi mu je ciki ki ga wani abu.”
Matsawa tayi daga gefenshi tace” Ka ga malam, ni ba yarinya ba ce da zaka min wani banzan wayo kamar wata yar talla, na san me ya kawoka wajena kuma ban da buk’ata ni.”
D’auke kai tayi daga gareshi tace” Sai ka je can figaggiyar Zafeera ta ke ko wa? Ta sauke maka abinda yake damunka.”
Mik’ewa tayi tsaye d’auki wayarta sannan ta kalleshi ta sake fad’in” Ko kuma ka je nakasashiyar matarka ta biya maka buk’atar, amma ni ma daga yanzu na san ciwon kai na.”
Tana gama fad’a ta juya da sauri ta shige d’akin baccinta ta rufe da makulli, da kallo ya bita har ta rufe k’ofar, tab’e baki yayi ya mik’e yana d’an girgiza kan shi, to in banda abun Joyran ma ta ya sarki zaki fad’a masa haka? Gidan nan da ke cike da bayi da hadimai.
D’akinshi ya koma inda ya samu d’aya daga cikin masu tsaron k’ofar shi ya kirashi zuwa ciki, bayan sun zauna ya nutsu ne yake fad’a masa “A cikin hadiman gidan nan wacece ka yarda da tsaftarta da kuma rik’on sirrin ta?”
Sadde kai ya sake yi cikin girmamawa yace “Wajen tsafta kam ba za’a rasa ba ranka shi dad’e, a ge da rik’on sirri dai ne bamu da tabbas, amma zamu iya d’orata a hanya mu da kanmu.”
Jinjina kai sarki Wudar yayi yace “Wa ya fad’a maka amana koyawa mutum ita ake? Ai da ita ake haihuwar mutum.”
K’ara sadda kai bafaden yayi a zuciyarshi yace “Amma ni a zaman da na yi da abokina na fahimci addininshi ne ya koya masa zama hakan, ko ba’a haifeka da ita ba indai kana wannan addinin, to ya zama wajibinka ka koyawa kanka ita, rashin samun amana kuma a wajen mutum mai wannan addinin, to tabbas ka tabbata gurb’atacce a cikinsu.”
A zahiri kuma cewa yayi” Hakane ranka shi dad’e, amma girmanka ya isa ya samar da mai amana da rik’on sirri.”
Jinjina kai yayi amma bai xe komai ba, kusan minti biyu a haka kafin yace” Ka je ka zo min da ita nan.”
Da sauri ya mik’e yace” An gama sarki na.”
Fita yayi da sauri dan cika umarninshi, sarki Wudar kuma mik’ewa yayi ya koma d’akinshi dan zaman jiran wacce za’a kawo masa.
A k’alla minti ashirin ya d’auka kafin suka dawo tare da wata budurwa, har k’ofar d’akin ya k’wank’wasa ya basu izinin shiga, shiga sukayi a tare ind ya d’ora ido akan matashiyar, bata da laifi kam kyakyawa yar duma duma, jikinta ma babu alamar k’azanta ko datti, saidai alamu sun nuna a tsorace take, dan gaba d’ay cikin d’ar d’ar take ta k’ame ta k’i sakin jikinta.
Kallon bafaden yayi ya masa alama da zai iya tafiya, jinjina kai yayi ya tashi zai fita yace “Na barku lafiya.”
Yana kaiwa bakin k’ofar ya bud’e Umad kuma na tsaye bakin k’ofar, d sauri ya sake zubewa k’asa yana fad’in “D’an sarki jikan sarki, barka da warhaka shugaba na, barka, barka.”
Wani kallo Umad ya masa hakan yasa ya rab’ashi ya wuce sum sum sum, cikin takon isa ya shigo d’akin yana kallon mahaifin na shi da kuma yarinyar nan.
Wangale baki sarki Wudar yayi ya fara kame kame ya rasa abin fad’a, har saida Umad d’in ya tsaya gabanshi ya kalli yarinyar yace “Je ki.”
Da sauri jikinta na rawa ta kama hanya ta fice a d’akin, ganin haka yasa Wudar matsawa kusanshi ya dafa kafad’arshi yace “D’ana, ka gane ko? Wannan d’in ai…ita..”
A nutse ya k’urawa fuskarshi ido yana kallo yace ”
*Alhamdulillah*
GIPHY App Key not set. Please check settings