Lu’u Lu’u 30

Advertisement

*30*

 

A nutse ya k’urawa fuskarshi ido yana kallo yace “Ita d’in ‘yar wasu ce, kuma addininta bai lamunce mata aikata abinda ka so aikatawa da ita yanzu ba, dan ba siyota kayi a kasuwar bayi ba, amma zaka iya neman aurenta hannun iyayenta, dan a gaskiya bana buk’atar wani k’anin wanda aka samu ba ta hanyar aure ba.”

Waro ido yayi yana kallon Umad d’in dake sake k’are masa kallo, a ladabce ya sanyaye yace” Ni zan tafi, lokacin tashin jirginmu ya kusa, sai na dawo.”

Juyawa yayi zai tafi sai kuma ya dakata, ganin kallon da yake masa ne yasa shi fad’in” Mahaifina ka kwantar da hankalinka, babu wanda zai ji maganar nan daga bakina, na san me yake faruwa tsawon lokaci, hakan yasa ban cika son zaman gidan nan, kuma ban ga laifinka duba da halin da mahaifiyata take ciki, takaici d’aya ne kawai yanda ka kasa samun halak d’inka kake bibiyar haram, haram d’in ma wacce ta k’azanta.”

A ladabce ya girgiza masa kai yana sadda kanshi yace” Dan Allah Babana kar ka tilasta mata ta zubar da cikin nan, dan kuskure ne akan kuskure.”

Juyawa yayi a ladabce ya fice a d’akin ba tare da Wudar ya ce komai ba, dan sosai maganganun suka dakeshi, saboda bai tab’a tsammani ba kuma abun ya zo masa a bazata, hakan ya hanashi tambayar ina Umad d’in ma zai je? Dan kunya ta gama lullub’eshi baya jin zai sake d’aga ido ya kalleshi.

 

*Khazira*

 

Advertisements

Ka rantse da Allah mahaifinta kuma sarki Musail bai gargad’eta kan sallah nan ba, domin kuwa la’asar ma a farfajiyar suka yi ta kamar yanda suka yi sallah zuhur.

Suna cikin sallahr nan motar su Umad ta shigo gidan, saidai madadin k’ayatuwar gidan ta d’auki hankalinsu, sai ya zamana sallah ce ta d’auki hankalinsu duba da abu ne da ake yi a b’oye.

Saida suka fito daga motar wani bafade ya d’auko jakarsu k’waya d’aya tak ya nufi ciki da ita, girgiza kai Umad yayi dan yasan wannan kam na daga cikin aikin Ayam.

Bin bayan bafaden sukayi kamar yanda sarki Musail d’in ya umarta a saukesu a babban falo na babban b’angare dan su fara cin abinci, sannan a nan ne zai had’u da Ayam d’in.

Suna kammalawa suka nufi shig ciki sai Juman ta kalleta tace “Ke je ina zuwa.”

Da alamar tambaya tace “Ina zuwa Mah?”

A sanyaye tace “Zan ga mahaifinki ne.”

Jinjina kai tayi ta shige ciki, tana shiga falon suka had’a ido da wata jakadiya, sam bata kula da tsiyarta ba ta taka matakalar ta shiga hayewa sama da sauri.

Sam bata gansu a zaunen nan ba, amma shi tun shigowarta yake kallonta, saidai yanzu kuma da take hawa matakalar sai ya ji gabanshi ya tsiri fad’uwa haka kawai, yanda take hawa da gudu gudu haka zuciyarshi ke harbawa tana dokawa, jikinshi ke bashi kamar da wani abu, hankalinshi ya kasa kwanciya duk da bai ga wani abun zargi ba.

Yanda jinin jikinshi ke tsinkewa yana wani d’add’aurewa yasa shi d’an mik’ewa tsaye, kalonshi Haman yayi yace “Ya dai? Ina zaka je kuma?”

Girgiza kai kawai yayi tare da d’an takawa yana ci gaba da kallonta har ta haye na d’aya ta shiga taka na biyun wanda daga shi zai sadata da d’akin Juman, bata ankara ba, kamar a mafarki, ba zato ba tammani kawai ta ji k’afarta tayi wani k’iiiiiiii, takalminta da a plate ne masu d’amara, tiles d’in kuma irin mai shegen walk’iyar nan ne da sulb’i, hakan yasa duk isa da izzar Zafreen kan ga bata cika anfani da takalmi masu tsini ba, idan ka ga ta sakasu sai ta sauko k’asa.

Abun ne ya had’u yayi yawa, hakan yasa ta kasa rik’e kanta yanda bata da wata dabara daya wuce ta rintse idonta ta anbaci “Ahhhhhhh.”

Advertisements

A k’asan zuciyarta kuma Inna lillahi wa’inna ilaihi raju’un take furtawa, saidai firgicin ya hanata fito da shi, dan ba kad’an ba silb’in nan ya ja ta.

Bata yi k’asa a gwiwa ba wajen fara mirginowa daga kan matakalar, da wani irin sauri ya ma matakalar hawa biyu a na uku ya had’e da ita tana neman k’arasa durkowo, cak yasa hannayenshi da wata irin zummar cimmawa ya d’auketa cak a jikinshi.

Tabbatarwa da tayi ba’a k’asa take ba, sannan ta ji a jikin mutum take bayan wuntsilawar data fara yi, ga kuma k’amshin daya daki hancinta wanda a jikin mutum d’aya ta san shi, da kuma yanda shi ma ya wani k’amk’ameta sai kawai ita ma tayi luf a jikinshi ta sake rik’eshi sosai, idonta kuma har yanzu suna rintse, inda ta shiga sauke numfashi tana fad’in “Oh Allah, Oh Allah na, Alhamdulillah.”

K’am k’am ya ci gaba da mak’ale mata kamar wata wacce za’a k’wace masa, shi ma idonshi a lik’e suke inda gabb’an jikinshi ke karb’an sak’onnin da zuciyarshi ke wadatuwa da su, sai ya ke jin kamar wata masoyiyar daya jima bai had’u da ita ba ne, sai ya ji kamar namijin da aka tura yak’i ne ya dawo da ranshi ya kuma samu iyalinshi lafiya, wata irin kewar wacce yake rumgume da ita ya ji tana lullub’eshi, bugu da k’ari ga wani yanayi da wani shauk’i da ya d’ebeshi kamar ya daure ya sumbaceta.

Yanda siririyar muryarta ta karad’e gidan sanda tayi wannan ihun yasa duk wanda ke b’angaren saida ya ji kuma ya fito har da Zafreen dake kwance a d’akinta tana danna waya.

Haka ma duk da ihun a kad’an ya shiga dodon kunnenta, amma abunka ga mahaifiya sai Juman ta juya tare da furta “Ayam.”
Da gudu ta fice a fadar ba tare data fad’i me take son fad’a ba, sarki Musail daya shiga kid’imar abinda ta fad’a masa na batun gubar da aka zuba musu shi ma da wani irin sauri ya sauko daga kujerarshi ya bi bayanta kamar zai ruga shi ma, hakan uasa fadawan duk suka rufa masa baya Khatar da Dhurani suna mai fatan a ce ta mutu daga ihun nan da suka ji.

Shigowarsu a hargitse yasa su saurin dawowa hayyacinsu, raba jikinsu sukayi da sauri suka kalli juna kamar an firgitasu, Ayam ce hakan ya firgita ta har tace “Kai ne? Yallab’ai?”

Da sauri Juman ta matso kusanta tana duba jikinta tace “Me ya sameki Ayam? Ihunki na ji?”

Da sauri sarki Musail yayi kanta yana d’aga hannunshi alamar zai dafa kanta yace “Me ya sameki? Kina lafiya ko?”

D’aga kai tayi alamar e sannan tace “Lafiya ta lau Pah.”

Juman ce ta sake fad’in “Me ya faru to? Wani ne ya miki wani abu?”

Girgiza kai tayi alamar a’a tana satar kallon Umad, hakan ne ya b’ata ran sarki Musail yace “Ana magana kuna ji kunyi shiru, a cikinku babu wanda zai fad’a mana me ya faru ne?”

D’aya daga cikin hadiman dake kawo abinci ne tace “Ranka sho dad’e muna kawowa bak’i abinci, shi ne muka ji ijunta daga sama, kafin mu farga silb’i ya jata ta fad’o daga…”

Hankalinshi a matuk’ar tashe yace “Daga saman nan?” Ya fad’a yana nuna saman, a sanyaye hadimar ta jinjina kai, sake kallon Ayam yayi ya fara takawa zai tunkareta, kamar kuma an tsikareshi saiya dakata tare da basarwa, a wani gadarance ya kalli Umad dake kallonshi yana son tabbatar da abinda idonshi ke hango masa a game da sarki Musail d’in.

Cikin k’asaita ba tare daya d’auke ido daga gareshi ba yace “Waye kai?”

Fuskarshi babu alamar rusunawa, idonshi tsaf suke kallon cikin na sarki Musail wanda ba kowa ke haka ba, fuskarshi babu alamar ladabi ko zai girmamashi, a gadarance ya furta “Umad.”

K’ank’ance ido sarki Musail yayi yace “Ba sunanka na tambaya ba, waye kai na ce?”

Da sauri Haman dake gefe a tsaye tun sanda Ayam ke burususuwa tana fad’owa ya mik’e ya matso, cikin ladabi da girmamawa sam ya ma manta da tsarin da suke a kai yace “Yallab’ai, shi ne ai abo…mai tsaron lafiya ta.”

D’auke kai yayi ya kalli Haman d’in yana yatsina fuska, kallo ya k’are mishi sai ya ga indai ba wani abu ba kuma, a zahiri dai kam sam Umad bai yi kama da wanda zai zama abinda Haman d’in ke fad’a ba, duba da wasu b’oyayyu da kuma bayyanannun yanayi dake tattare da Umad.

Da sauri sauri Zafreen ta fito daga d’akinta hannunta rik’e da waya, tana zuwa ta tsaya cak tana kallonsu tace “Pah, me yake faruwa a nan?”

Kafin ya bata amsa kuma ta kai kallonta kan Umad, da wani irin zumud’i ta nufeshi bata tsaya komai ba ta fad’a jikinshi ta kwanta tayi luf da dariya a fuskarta tana fad’in “Yallab’ai, kai ne a nan ma?”

D’agowa tayi daga jikinshi ta kalli fuskarshi yanda yayi sororo da al’ajabin dama arharta har ta kai haka? Cikin farin ciki tace “Yallab’ai ni ka biyo ko? Na sani da ma kai ma kana so na.”

Zura hannunta tayi cikin na shi hannun ta mak’ale masa kamar za’a rabasu, Juman kallonta take da mamakin irin yanda ta ballagazar da kanta haka, kamar ba wannan mai izzar da d’agawa ba? Gashi babu kunyar kowa haka take tsaye da kayan jikinta, farin wando na jeans iya cinyoyinta da riga kalar pink mai siraran hannaye, duk da kyanta ya bayyana da kyakyawar surarta, amma dai babu kimarta a idon masu kallonta haka kuma darajarta.

Tunda ta fad’a jikinshi Ayam ta ji fad’uwar gaba tare da jin wani haushi ya taso mata da takaici, har saida ta kasa b’oyewa ta ja d’an k’aramin tsaki ta d’auke kai daga kallonsu tana yatsina fuska, haka kawai abun ya b’ata mata rai har tana jin da zata samu damar keb’ewa da shi a yanzu data tuhumeshi akan me da ta rumgume shi bai tureta ba? Bata sake kallonsu ba saida ta ji Musail yace “Ina kika san shi?”

Cikin zumud’i da rashin kunya tace “Pah ai a makarantar da na je a nan yake koyawa.”

Wani kallo Dhurani ya masa yace “Idan kuma malami ne kai, ta ya ka zama mai bashi tsaro?”

Wani kallo ya wurgawa Dhurani da alamar b’acin rai yace “Aikin gwamnati na ke, duk wanda ya tari gabana zan yi.”

K’ura masa ido Juman tayi ta kasa d’aukewa har saida murmushi ya sub’uce mata, sak kallon yayanshi take masa Urab, hakan yasa har ya fahimta ya d’an karkata idonshi ya kalleta, cike da kunya da girmamawa ya rusuna idonshi tare da kanshi a ladabce yace “Barka sarauniyata.”

Sake murtuke fuska sarki Musail yayi ganin sai matarshi ya sakar ma fuska amma shi ya maidashi kamar wani sakarai ma, jinjina kai yayi a b’oye sannan ya kalli Haman yace “Sannu da zuwa.”

Rusunawa yayi ace “Barka yallab’ai.”

Muryar Juman ce ta dawo dasu da ta kalli Umad tace “Sannu ko?”

Jinjina kai yayi a ladabce yace “Sannu ranki shi dad’e.”

Yatsina fuska sarki Musail yayi yace “Mu je mu ci abinci.”

A sanyaye Ayam ta mak’ale kafad’a tace “Ni dai na k’oshi.”

Juman ma sama da k’asa ta kalleshi tace “Ni ma haka.”

Hannun Ayam ta kama zasu bar wuri ta kalli Umad tace “A ci lafiya.”

Hanyar masaukin Ayam suka nufa inda sarki Musail ya bisu da kallo, a ciki yayi k’wafa alamar zku sani sannan ya nufi wajen cin abincin ba wai dan yana buk’ata ba sai dan bak’inshi.

Rankayawa sukayi kan teburin Umad na ta k’ok’arin b’amb’are hannunshi cikin na Zafreen amma ta rik’e gam, har saida suka isa duk suka zazzauna, tsaye ya so yi dan sake k’ara fahimtar komai na gida da takon kowa, amma sai Zafreen ta zaunar da shi da k’arfi har saida Musail ya kalleta yace “Ke!”

Sai kuma ya d’auke kai yana girgiza kan shi, haka aka zuzzuba abincin kowa ya fara ci.

Cokalansu kad’ai ke k’ara a wurin, cikin siririyar murya Zafreen ta kalli sarki Musail tace “Pah, kasan na jima ina fad’a maka ban samu wanda ya dace dani ba a garin nan?”

Zuba mata ido yayi shi dai bai ce komai ba, d’orawa tayi da “To yanzu na samu, wannan ne.”

Ta k’arashe tana nuna Umad da ka rantse baya jin yaren ta, duk da dai d’in gaskiya bai cika jin yaren slovaque ba, amma dai yana ji jefi jefi saboda yanayin aikinshi da shige shige da kuma sa kai.

Haman a dake ji jefi jefi da Khatar da kuma Adah duk kallonta sukayi dan Dhurani tafiyarshi yayi bai tsaya ba, sarki Musail ma kallonta yake yi kamar ya wanka mata mari, haushin hakan yasa bai ce k’ala ba sai Haman daya kalla a nutse yace “Me ye sunanka?”

A ladabce ya amsa da “Ranka shi dad’e sunana Haman.”

Jinjina kai yayi irin na dattawa yace “Haman Abraham Joshua kenan?”

Gyad’a kai yayi alamar e, lumshe ido yayi alamar gamsuwa, a tsanake ya sake furta “Me ye aikinka? Kuma a ina ka fara sanin Zafeera? Me kuma ya sa kake son aurenta?”

Cikin d’ar d’ar Haman yace “Yallab’ai na kammala karatu na, inda nake da burin mahaifina ya sama min aiki a babbar ma’aikata, Zafeera kuma mun fara had’uwa ne a Giobarh, saidai ban mata magana ba a saida na fara sanin wacece ita, ina kuma so ne na aureta dan ina sonta.”

Wani hamshak’in murmushi sarki Musail ya saki yace” Bayan son da kake mata, sai kuma wane dalili?”

A hankali ya karkata ya saci kallon Umad da shi ma ke kallonsu ko abincin baya ci, sai kuma ya kalli sarki Musail yace” Saboda yar babban gida ce, ita ce ta dace ni.”

Sauk’akk’en murmushi ya saki ya d’an fara tsakurar abincin yana fad’in” Mu ci abinci yanzu, nan da awa biyu zan had’aku da ita dan ku tattauna, idan kun fahimci junanku mahaifinka na zuwa nan ranar d’aura muku aure za’a saka.”

Wani k’ayataccen murmushi Umad ya saki a ranshi ya ayyana” Lallai ma, ku gama duk shirin ku, na wa ne zai yi aiki a k’arshe.”

Haka suka ci gaba da cin abincin da tattaunawa tsakanin Haman d’in da sarki Musail, bayan su babu wanda ya saka musu baki banda Zafreen dake ta k’ok’arin d’aukar hankalin Umad d’in tana ta washe masa baki.

 

*Alhamdulillah*

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like
Read More

TARTSATSI 42

Advertisement *Page 42* **************** Hafsa tana zaune sai faman sak’awa da kwancewa takeyi, in ta kamo hanya nan…
INAYAH
Read More

INAYAH 5

Advertisement 5 Daqyar ta iya furta “Hadiza Allah zai zama gatanki, Allah zai raya Miki ‘yarki cikin Aminci…
INAYAH
Read More

INAYAH 11

Advertisement 11_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Washe gari ba wani dogon walwala ta tashi Saima guraren 9 ta tashi Dan tun…