Advertisement
*31*
Wajen Ayam kuma d’aki suke ita da Juman inda ta tambayeta a tsanake “Mah, a game da lamarin ruwan garin nan, yau nayi magana da wasu daga cikin talakawa sun fad’a min komai, ya zanyi na taimakesu akan haka?”
A tsanake ita ma tace “Ayam ai maganar ruwan nan kasuwanci ya shiga cikinshi, duk da gwamnati na iya yin ta, bana jin zaki iya wani abu tunda baki da abu biyu.”
Da alamar tambaya ta kalleta tace “Kamar ya Mah?”
Numfashi ta sauke tace “Na d’aya baki da kud’i, na biyu baki da iko.”
Da mamaki tace “Idan ina da su kenan zan iya taimakon al’umma?”
Jinjina kai tayi tace “Tabbas, idan kina da kud’i zaki iya taimaka musu, idan kina da iko zaki mallaki dayawa daga cikin masu fad’a a ji.”
Shiru tayi tare da fad’awa kogin tunani, sai ta ga bata da wad’annan abubuwan, da sauri ta rik’o hannun Juman tace “Mah, ke fa? Ai kina da iko saboda ke ce sarauniyar k’asar nan, kuma nasan kina da kud’i ma.”
Murmushi tayi ta girgiza kai tace “Bana da ko d’aya yanzu Ayam, sanda mahaifinki ya jefani kurkuku ya datse min asusun bankina, gaba d’aya masarautar nan yanzu ba zan iya saka baki a abinda ya shafeta ba.”
Advertisements
Da mamaki a fuskarta tace “Saboda me Mah? Na d’auka yanzu ai kin fito.”
Sake fad’ad’a murmushi tayi tace “Ayam kenan, kafin ya fito da ni saida aka fad’a min na wucen gadi ne.”
Cike da alhini a fuskarta tace “Mah…na kasa yarda Pah duk yake wad’annan abubuwan, har yanzu bana jin wani iri a jikina idan na ganshi.”
Lak’ace hancinta tayi tace “Saboda yana mahaifinki ne mana, soyayyar dake tsakaninku ba zata bari tsoro yayi tasiri a kan ki ba.”
Ajiyar zuciya ta sauke bata sake cewa komai ba, haka ita ma Juman ba tayi magana ba, saidai dukansu da abinda suke tattaunawa a zuk’atansu.
*08:30* Na dare ta fito cikin wasu had’add’un kaya na masarauta wanda suke jan k’asa har da babban mayafin da aka d’ora mata a kai amma ya sauka a baya, karo na farko a rayuwarta da aka shafa mata jan baki kalar leb’enta pink, bayan yau kam bata tab’a sakawa ba, tana dai shafa man leb’e amma ba jan baki ba.
Sanyayyan k’amshinta ne ya fara sanar da su tana zuwa, suna juyawa a tare da sauri Haman ya mik’e tsaye dan sak sarauniyar Khazira idonsa suka gane masa, hakan yasa shi saurin mik’ewa da girmmawa yana neman gaisheta.
A b’oye Umad ya ja rigarsa ya d’an motsa labb’ansa yanda ba kowa zai gane ba yace “Kula fa, kar ka kwafsa.”
D’an gyara tsayuwarshi yayi ya saisaita kanshi ya dakata daga hard’ewar da yake shirin yi ya rusuna mata, da k’ayataccen murmushi ta k’araso a nutse zauna tare da nuna masa zai iya zama, zaune sukayi a tare inda ta d’an k’yallara idonta ta kalli Umad.
D’auke kai tayi ta kalli hadiman da suka rakota, a nutse kamar wata sarauniya ta furta “Zaku iya tafiya.”
Saida suka rusuna kafin suka nufi hanyar fita, saida ta ji sun rufe k’ofar sannan ta kalli Umad dake tsaye bayan Haman k’ik’am, sauke k’arar data d’ora kan d’aya tayi ta gyara zamnta cikin yanayinta data saba tace “Me ye haka yallab’ai? Duk wannan shirin na miye? Me ye wani neman aure na da kuma mai tsaro?”
Haman kam mik’ewa yayi ya koma kusa da Umad yace “Zai miki bayani, duk shirin sa ne wannan.”
Advertisements
Kamar a rashin sani ta mik’e tsaye tare da wurgawa Umad wata harara, takawa tayi har zuwa inda suke tsaye, da yatsa ta shiga masa k’wak’waran kashedin “Ka ga yallab’ai bana so, bana son wannan bibiyar da kake min, idan har gaske ne rayuwata na cikin had’ari, to ka barni na mutu bai dameka, amma ka sani idan har wani abu ya samu mahaifina a zuwan nan na ku, wallahi Allah sai ka gane kurenka.”
Jujjuya d’an k’aramin bakinta tayi ta juya ta barsu tsaye baki sake da mamaki, bugo k’ofar da tayi bayan fitarta ne yasa Umad sakin wani lallausan murmushi yana girgiza, wai shi ta kalla duk da matsayinshi a gareta, da kuma matsayin da Allah ya masa kasancewarsa mai jiran gado, bata duba kasantuwarshi na malaminta ba ta kalleshi ta nunashi da yatsa sannan ta ce wai *zai gane kurensa*.
Shafa sumar kanshi yayi ya zauna kan kujera yana furta “Zakanya, ni ne zan gane kure na?”
Jinjina kai yayi yace “Zan gani.”
Da sauri Haman ma ya zauna yana fad’in “Ka ga Umad dan Allah ka fad’a min me ye shirin ka? Ni wannan shirun da ka min ina bin uamrninka bana son shi wallahi.”
Kallonshi yayi fuska a had’e yace “Zan fad’a maka, ka k’ara hak’uri kawai.”
Jinjina kai yayi yace “Shikenan zan jira.”
Tana komawa d’aki ta samu Juman ta shiga fad’a tana fad’in “Mah ni wannan kayan sun isheni, cirewa zanyi.”
Dariya tayi tace “Zaki fara sabawa da zaran kin zama sarauniya.”
Kallonta tayi kamar zatayi kuka tace “Haba Mah, ki daina fad’a mana.”
Jinjina mata kai tayi tace “Na ga wannan ranar Ayam, na ga haka a mafarkina, saidai nasan ba lallai mafarki ya zama gaske ba.”
K’ala ba tace ba saida ta cire kayan nan ta d’auki wata sassauk’ar riga a cikin wanda aka kawo mata ta bacci ta saka, warware gajeran gashinta tayi wanda har yanzu yake tohowa ta sakeshi dan ya sha iska, kan gadon ta kwanta ta kalli Juman tace” Mah, yau na farko a rayuwata ina so na kwana tare da ke kaina a kan k’irjinki.”
Dariya tayi tace” Baki da matsala gimbiyata, ni ma zan so hka duba da yau zan yi bacci a nutse hankalina kwance.”
Da mamaki tace” Saboda me Mah?”
Cikin rad’a da fara’a a fuskarta tace” Saboda Umad na gidan nan, ganinshi ya bani k’arfin gwiwa, duba da shekarun dana fara had’uwa da shi da kuma yanzu.”
Girgiza kai tayi ta buga hannunta akan cinya alamar” Haba mana Mah.”
K’yalk’yalewa tayi da dariya tace” Da gaske nake fad’a miki.”
Turo baki tayi tace” Ni da yanzu mana fad’a masa ya daina bibiyata, ni sam ban wani yarda da shi ba.”
Kallon tuhuma ta mata tace” To da kike jin haka a game da shi, me ya hana ki fad’awa mahaifinki?”
Jim tayi sai kuma ta d’aga kafad’a alamar bata sani ba, matsawa Juman tayi kusanta ta ja dogon hancinta tace” Ko dai ko dai? Ko dai akwai abinda k’aramar yarinyata ke b’oye min ne?”
Rik’e hannun Juman d’in tayi data ja mata hanci da shi tana k’yalk’yala dariya tace” Mahhhh…hancina fa, ni ba wani abu da nake b’oye miki, d’azu ma ba’a gabanki na saka kaya ba?”
Janye hannunta tayi daga hancinta sai kuma ta shiga mata cakulkuli tana fad’in” Ban yarda ja’irar yarinya, fad’a min me kike ji a kan shi? Da alama idan baki zama sarauniyar Khazira ba zaki zama sarauniyar Giobarh.”
Cikin farin ciki suka dinga wasarsu har Juman ita ma ta canja kayanta suka kwanta, daga kwance ma duk abubuwan da zasu anfaneta a cikin addininta ta dinga sanar da ita, k’aramar wayar da Ayam har ta manta ta ta ce sak’o ya shigo, d’auka Juman tayi ta mik’o mata tace “Wayarki.”
Karb’a tayi tana duba wayar dan har ta manta wace kala ce ma, bud’e murfin tayi ta duba sak’o gajere kamar haka _”Ki ji magana ta, bayan d’akinki da na mahaifiyarki ki kwana a ko ina ki ke so, idan kuma kina son kasancewa cikin tsaro, to ki kwana a k’ark’ashin kulawar Umad.”_
Tashi tayi zaune tana sake karanta sak’on, me hakan ke nufi kuma? Wa ye ya turo mata sak’o haka? Gashi dai lambar ma a rufe take, tsaki tayi kawai ta rufe wayar ta aje gefe ta koma ta kwanta.
Cike da kulawa Juman ta kalleta tace” Lafiya? Me ya faru?”
Ba yabo ba fallasa ta amsa da” Ba komai.”
D’ora mata tayi daga inda suka tsaya ta ci gaba da fad’in” A duk wani hadisi daya tabbata kuma ya zo daga iyalai ko sahaban manzo (S. W. A) babu wanda ya nuna Annabi Muhammad yayi wankan tsarki wanda ba cikakke ba, ma’ana wankan da bashi da alwala, amma magaba sun inganta wanka da baya da alwala ma, wasu daga ciki sun ce ko da a cikin kogin ruwa ka tsumbula da niyyar wankan janaba to yayi, haka ma idan a buta ne ka d’aga ka kwarara a kan ka shi ma yayi…”
Numfashin da Ayam ke saukewa ne yasa ta satar kallonta, ai kam idonta a rufe alamar bacci, da alama kuma ta fara jin dad’inshi saboda yanda ta turo baki hannunta akan cikin Juman, murmusawa tayi ta d’an muskuta kwanciyarta sannan ta gyara hannunta ta fara shafa gashin Ayam d’in.
Irin dad’in da take ji marar misaltuwa na ratsata sanadiyar kasancewa tare da ‘yarta, hakan yasa murmushi ke shinfid’e akan fuskarta idonta a lumshe tana d’an rera wak’a a can k’asan zuciyarta ta farin ciki da godiya ga Allah, sannu sannu ita ma har baccin ya d’auketa mai dad’in gaske data jima ba tayi irinsa ba.
Yanda ya ji shiru daga d’akin yasa shi shigowa cikin sand’a, ganin dukansu bacci suke yasa ya ci gaba da takawa saida ya zagaya inda Ayam ke kwance, a hankali savoda baya so su farka ya sunkuya tare da d’an d’ora hannayenshi a kan gadon ya tokaresu, matsawa ya dinga yi saida ya kai kanshi kusa da na ta, cike da shauk’i da so da k’auna ya d’ora labb’anshi ya sumbaci kanta, a hankali ya d’ora hannunshi akan gashinta ya shafa wasu k’walla na cika masa ido.
Motsawar da Ayam ta d’an yi ce tasa ya zabura ya mik’e tsaye ya rarraba ido cikin rashin gaskiya, kamar zata bud’a ido sai kuma ta sake yin ram da cikin Juman ta ci gaba da shek’a baccinta.
A hankali ya zagaya ta b’angaren Juman yasa hannu ya daddab’ata, a tarz suka bud’a ido suka kalleshi kafin su raba jikinsu dana juna, cikin had’e fuska sarki Musail yace “Ke me kike a nan? Ba ga d’akinki can ba?”
Turo baki tayi gaba tace “Pahh, nan nake so na kwana, kai ma ka zo ka kwanta a nan.”
Murmusawa yayi yace “Zafeera, ki je d’akinki ki kwanta kinji, na zo ganin mahaifiyarki ne tunda na ga ita bata san ta je inda nake ba.”
Cikin magagin baccin daya kasa sakinta ta kalli Juman sannan ta rarrafa ta sauka daga kan gadon, ganin kamar tana had’a hanya yasa shi saurin kama hannunta ya rumgumota a jikinshi, saitin kunnenta ya rad’a mata” Ki tabbatar baki je d’akinki ba a daren nan.”
D’aga kanta tayi t kalleshi da mamaki da kuma fad’aw tunani, amma kafin ta ankara ta turata k’ofar d’akin ya rufe ya barta tsaye da zulumi.
Ganin gidan shiru ga fitilu duk an kashe yasa ta saurin d’aga k’afa ta nemi haurawa sama, dakatawa tayi sai kawai ta bi ta wata kusurwar duk da bata san ina zata kai ta ba, cikin tsoro tsoro take tafiya tana sand’a, duk k’ofar data wuce saita kalla da mamakin yawan d’akunan dake cikin gidan, jin ana bud’e wata k’ofar daga bayanta da makulli yasa ta saurin ruguwa cikin sand’a, d’akin dake k’arshen kusurwar kawai ta bud’a ta kuma yi sa’a a bud’e yake, dan tsoronta bata san wa ye zai fito ba, kuma sak’on nan da kuma abinda mahaifinta ya fad’a mata ya tsorata ta sosai, ga ka duhun cikin gidan wanda sai d’an siririn hasken jar fitila kawai.
Tana shiga d’akin ta mayar da k’ofar da sauri ta rufe tare da juyawa ta dafe k’irji dan ta sauke numfarfashi, sai dai bala’in data gani ne ya yi barazanar tafiya da numfashinta, kakkafewa idonta sukayi inda ta ja numfashi amma bata samu damar saukeshi ba, ga hannunta akan k’irji ta tsaya k’am kamar gawa.
Fitowarshi kenan daga wanka ya gama goge jikinshi, wandonshi ya d’auka 3 quater zai saka, hakan yasa shi zame towel d’in dake d’aure a k’ugunshi, amma da ya ji an shigo d’akin kamar ba lafiya ba sai ya dakata ya juya da k’arfi rai b’ace da tunanin wane marar tunanin ne, ganinta yasa komai na shi ya tsaya ya rasa abun yi, musamman daya fahimci kamar ta fita hayyacinta sakamakon mugun ganin da ta yi. 馃槍
A saib’ance ya sunkuya ya d’auki towel d’in ya d’aura yana jan tsaki da fad’in “Ko ma menene ke kika ja.”
Wani tsakin ya kuma saki tunawa haka ma waccen ranar ta bankad’o mata kai d’aki, saidai anyi sa’a ranar yana cikin ban d’aki ne.
Sake juyawa yayi ya kalleta ya ga tana nan yanda take, girgiza kai yayi ya fara takawa zuwa gareta, yana tsayawa gabanta ya k’yasta mata hannu yace “Ya dai? Kin ga wani abu ne?”
K’arfin halin irin na ta yasa ta d’aga baki za tayi magana, sai ta ji babu abinda zai iya fitowa sai kurmanci, hakan yasa ta daddagewa ta d’aga bakinta ta kwamtsa k’ara, da wani irin sauri ya sa hannu ya rufe mata baki tare da jawota jikinshi ya had’e gam, tana jin haka sai kuma numfashinta ya b’ace b’at ta sume a jikinta, hakan yasa jikinta ya saki kamar wata matatta.
_Domin samun *lu’u lu’u* da kuma *Badak’ala*, ki biya naira d’ari biyu kacal ko kuma 400f cfa, dan samun na ki tuntub’i wannan lambar 94-98-56-52._
*Alhamdulillah*
GIPHY App Key not set. Please check settings