Advertisement
Bismillahir rahamanir rahim_
*41*
Babban teburin falon b’angaren sarauniya Juman aka zauna cin abinci, wanda sarauniyar ta sa aka gayyaci kowa zuwa nan, bayan cokula babu abinda ka ke jin k’ararshi, saidai kallon juna da ake kawai da ido, wani kallon mai ma’anoni da fassara, wani kallon kuma na katari ne kawai ido su sark’e da juna.
Gyaran murya sarki Musail yayi ya aje cokalin hannunshi mai yatsu sannan ya had’e tafukan hannayen ya kalli sarki Abdallah da ke kujerar dake fuskantar ta Musail, duk da suna da d’an nisa haka ya d’aga muryarshi amma a tausashe yace “Ranka shi dad’e, ina ga tunda gaba d’ayanmu mun taru, me zai hana na fad’i abinda ya ke raina?”
Cike da karammawa ya lumshe ido shi ma ya aje cokalin hannunshi yace “Me kuwa zai hana, bismillah fad’i.”
Ayam ya kalla dake kujerar daf da shi wacce take kallonshi tana tsakurar abincin saboda kallon da Umad ke mata wanda ke kurar dake fuskantar ta, murmushi ya sakar mata yace “Da ma ina so ne na mik’a mulkin Khazira ga me abun, ma’ana Ayam.”
Waro ido tayi tace “Kyu (Me)?”
Da mamaki suka kalleta na sabon yaren da tayi inda Umad ya rumgume hannaye a ranshi ya furta “Wata sabuwa.”
Da sauri ta kalli inda sarki Abdallah yake tace “Grand Pah, ka ji me Pah ya ke fad’i? Gaskiya ni a’a.”
Advertisements
A sanyaye Juman ta kalli sarki Musail tace “Abban Ayam, ina ganin me zai hana idan ma mulkin zaka bayar ka ba wa mai buk’ata Zafreen, tunda ita ma ai ‘yarka ce kuma babba.”
Kallonta yayi a tausashe yace “A gaskiya bana so na sake aikata wani kuskuren, Zafreen hali na gareta babu abinda ta rage, talakawan Khazira sun sha wahala a a hannuna, bana so na sake saka su uku.”
Marairaicewa Ayam tayi tace “Gaskiya ne Mah, ni kinga bana son wannan hayaniyar, idan so samu na ne na samu wani keb’antaccen daji mai d’auke da nau’in kowace dabba, na zauna tare da su na rayu da su cikin farin ciki.”
Wata basarakiyar dariya sarki Abdallah da Musail sukayi, haka ma sauran mutanen saida suka dara, inda Bukhatir ya narke ido yana kallon Ayam kamar ya sumbaci bakinta sanda take maganar, Juman ma cikin dariya ta kalleta tace” Ke burinki kenan a duniya? Rayuwa da dabbobi?”
A hankali ta jinjina kai alamar e, maida kallonta tayi niyyar yi ga plate, sai kawai a tsautsayi suka had’a ido da Umad dake kallonta yana sakin b’oyayyan murmushi, suna had’a ido ta d’auke kai ta d’auki cokalinta, ajiyar zuciya ya sauke ya kalli sarki Abdallah yana d’aukar na shi cokalin shi ma a ladabce yace “Yallab’ai, ai ita d’in sarauniyar jeji ce, ina ga dalilinta kenan na shiga karatun gandun daji, kuma da alama wannan foresti猫re d’in za ta zama sarauniyar dabbobi.”
Da fara’a sarki Abdallah yace “Da gaske Umad?”
Jinjina masa kai yayi yace “Baka gani ba sanda suke hira da zaki, abun kamar al’amara.”
Waro ido tayi ta bud’e baki tace “Kai kai kai, ni d’in? Yaushe?”
Kallon Juman tayi da ke k’yalk’yala dariya tace “Hakane ko Mah?”
A nutse Musail yace “Ayam, maganar gaskiya nake fad’a miki, ki shirya zama sarauniyar Khazira.”
Turo baki tayi gaba tace “Pah, a gaskiya ban shirya ma hakan ba, sannan ka ga ina so na kammala karatu na, burina shine na zama major, sannan ni ban san komai a harkar siyasa ko sarauta ba, i can’t take this risk Father.”
Sarki Abdallah ne ya kalleta yace “Pourquoi pas ma cher?”
Advertisements
Yatsina fuska tayi tace “Haka kawai ba zan iya ba.”
Kallon sarki Musail yayi ya d’an masa hira da ido irin ta su ta manya, jinjina kai yayi irin na fahimta sannan ya ci gaba da cin abincinshi.
Suna tsaka da cin abincin wani bafade ya shigo tare da sunkuyawa alamar girmamawa yace” Sarki na, bak’i daga Giobarh sun iso.”
Zaro ido Umad yayi ya kalli bafaden yace” Giobarh?”
Da mamaki Musail ya kalli bafaden shi ma yace” Giobarh? Su wa ye haka?”
A ladabce yace” Sarki Wudar ne da kuma sarauniyarsa.”
D’an zaro ido Musail yayi yace” Manyan bak’i haka? M yake shirin faruwa kuma?”
Kallon bafaden yayi yace” Shikenan, ka musu iso.”
Sunkuyawa yayi sannan ya juya ya fita, Musail kuma mik’ewa yayi yana kallon Umad da yake kallon k’ofa yace” Ina fata ba maganar d’aukar fansa ba ne?”
Kallon Musail d’in yayi sai kuma ya mik’e tsaye shi ma yace” Ba wannan yallab’ai.”
Hadimai ne suka fara shigowa mata d’auke da manyan kwando na roba mai kyau tamkar wanda aka sak’a da kaba, an musu kwalliya lullub’e da yadi mai k’yalli.
Layawa sukayi su goma duk rik’e da kayayyaki a hannunsu, a nutse sarauniya Kossam da sarki Wudar suka shigo, kayansu kusan kala d’aya ne har kalarsu ne, kalar shud’in ta musu kyau ga ratsin fari da k’yalli k’yalli, inda duka rigunan na su ke jan k’asa musamman ma gyalen Kossam.
Duk mik’ewa mutanen teburin sukayi suka tunkaresu a nutse, cike da girmama juna da karramawa suka dinga gaisawa, suma a ladabce suka sunkuya suna gaishe da sarki Abdallah wanda suka ganeshi sosai duk da dai shekaru sun ja sosai.
Ayam dake bayan Musail tana hangen Kossam, sai yanzu ne take tuna lallai fuskar matar nan ce a hoton data gani d’akin Umad zuwanshi makarantarsu, dan yanzu fuskarta ta fi fitowa da kyau saboda an sha gyaran jiki da na kai, duk da ba kwalliya a fuskarta amma dai hoda da man leb’en data shafa kalar leb’en na ta sun sa ta k’ara kyau.
Ta shagala da kallonta sosai ta ji murya kamar daga sama an ce “Zo nan ‘yata, gujajjiya daga mahaifiyarta.”
Dariya mutanen d’akin sukayi sai ita data zabura ta sake kallon matar, hannun Kossam d’in ta kalla data mik’o mata, a hankali ta mik’a mata hannun sannan ta taka zuwa gareta, kallon juna sukayi sai kuma Ayam ta sunkuyar da kanta k’asa cike da kunya tace “Mah…”
Hancinta Kossam ta ja tace “Shine dan kinga bana iya magana a lokacin kika gudu kika barni.”
D’aga kai tayi ta kalli k’wayar idonta, cikin dubara Kossam ta janye na ta idon saboda gagara da tayi wajen kallon idon Ayam d’in, d’an giggilma idon tayi tana kallon gefe gefe, lura da haka yasa Ayam sauke idonta k’asa tace” Ki yi hak’uri Mah…gani yanzu.”
Kallon fuskarta tayi da murmushi a fuskarta tace” Ba zaki sake guduwa ba?”
Girgiza kai tayi tace” A’a Mah, can ma na gudu ne saboda ina so zan ga iyayena.”
Kyab’e fuska Kossam tayi tace” Dan haka zaki sake min nisa? Nasan haka zai faru, shiyasa na zo da shirina dan na wa tubkar hanci.”
D’an d’aga ido tayi ta kalleta sai kuma ta sunkuyar da kai, a nutse ta tallabo hab’arta ta zubawa fuskarta ido, cikin sanyayyar murya tace” Zafeera, za ki zama ‘yata ta hanyar auren d’ana Umad?”
K’uri ta zuba mata ido tare da jin dokawar k’irjinta, kasa cewa komai tayi sannu sannu har ta samu ta sunkuyar da kanta k’asa, yanda falon yayi shiru Juman kuma ta d’aga labb’anta za ta yi magana sarki Abdallah ya mata alama da ido tayi shiru, hakan yasa d’akin ya d’auki shiru na wasu mintoci, kamar an tsikani Ayam ta d’aga kanta tana murmushi tace “Mah, na yi farin ciki da kika samu lafiya, zan iya zama ‘yarki mana…ko ma na ce na za…ma.”
Ta k’arashe tana kallon inda Umad ke tsaye wanda ya zuba mata ido yana kallo, da fara’a sarauniya Kossam tace “Da gaske za ki zama ‘yata? Sirikata?”
Da ido ta mata alamar e, hakan yasa Kossam fad’ad’a murmushinta ta kalli hadiman dake bayansu, mik’a musu hannu tayi d’aya daga cikinsu ta bata kwandon hannunta, tallabo kwandon tayi daga k’asa sannan ta juyo ta kalli Ayam, Musail da Juman dake bayan Ayam su ma ta kalla tace “Ina neman izininku da ku ba wa d’ana Umad auren ‘yarku Zafeera?”
Musail da Juman kallon juna sukayi, a k’ayace Musail ya saki murmushi Juman kuma ta b’oye dariyarta, sarki Abdallah ma haka tare da kusan wanda ke wajen.
Da mamaki suke kallonsu ta ya suke musu dariya daga wannan maganar, da sauri Umad ya matso kusan Kossam cikin rad’a d yarensu na Gallois yace mata “Mahh…kiyi shiru mana, ki zo zamuyi magana a wane.”
Kallonshi tayi ta kyab’e fuska kamar zatayi kuka tace “Me na yi da suke min dariya? Sai ka ce na nema maka auren matarka?”
Bai san sanda ya tintsere da dariya shi kan shi, abar da ya jima bai yi ba sai gashi yana k’yak’yatawa sosai duk da k’ok’arinshi na son rik’eta, cije leb’en k’asa tayi ta sake yin takwaf takwaf da fuska, da sauri ta mik’awa Ayam kwandon dake hannunta ta d’aga hannaye za ta daki Umad, da gudu cike da nishad’i ya lab’e bayan Wudar ya ruk’umk’umeshi yana fad’in “Pah ka gani fa, yanzu hakane ya dace mu yi farin cikin samun lafiyar Mah?”
Ita kam k’ok’arin sai ta dakeshi take tana cewa “Ja’iri kawai, ta ya kai ma za ka dinga min dariya daga magana, me na fad’a ba daidai ba? Zaka zo nan ko sai na…”
Cikin sa’a ta rik’o wuyan rigarshi ta jawoshi gabanta, fad’awa yayi jikinta yana ci gaba da k’yalk’yala dariya yace “Yi hak’uri Mah, zan fad’a miki wani abu to.”
Duk da Juman na jin kunyarta dan k’iris ya rage su zama surukanta, amma gashi ‘yarta ta zama surukarsu, cikin ladabi tunda suna sama da ita tace “Yar uwa, ki rabu da shi haka mana, dole ne fa a miki dariya saboda abinda kika zo d shi.”
Dakatawa tayi ta kallet tace “To me ya sa za’ a min dariyar?”
Cikin danne dariya saboda yanda tayi maganar tace “To ai matarsa ce kike nema masa aurenta, kinga kuwa dole mu yi dariya.”
Zaro ido tayi ta kalli Ayam ta kalli Juman, sannu sannu sai ta dinga juyawa tana kallon mutanen wurin dake ta sakin murmushi ban da Bukhatir kawai.
Da mamaki tace “Amma….” Bata fad’a ba ta dakata saboda wata damk’a da Wudar ya ma hannunta da k’arfin gaske, da sauri ta juya ta kalleshi.
Gaba d’aya fuskarshi da yanayinshi ya nuna ya shiga wani hali ne na tashin hankali da kid’ima, yanda ya kakkafe idonshi kan fuskar Juman da ta yi maganar, ga kuma d’aya hannunshi dake kan saitin zuciyarshi baki bud’e kamar zai yi magana amma kuma maganar ta mak’ale.
Gyara tsayuwarta tayi cikin rad’a ta dafa d’aya hannunshi daya rik’e na ta tace “Sarki na, lafiya? Me ya ke damunka ne?”
D’aga baki ya sake yi da kyau yana so sai yayi magana, amma sai ya fara sauke wani irin numfashi kamar yana fizgoshi ne da k’arfi saboda barazanar barinshi da yake, idonshi da ya kafe kan Juman ne suka d’an motsa da k’arfi sai kuma suka rufe ruf, gagggaf jikinshi ya d’auki rawa haka yasa k’afafunshi ma suka kasa d’aukarsa, luuuuu ya tafi zai fad’i Umad yayi caraf ya tallabeshi.
Saidai dake gaba d’aya ya saki jikinshi sai Umad d’in ya d’an motsa kamar zai fad’i shi ma, da azama Haman ya kama mi shi suka rik’eshi da kyau, hankali tashe suka rufa a kanshi wasu na firfita d’aya a cikin k’annan Bukhatir ta kawo ruwa aka shafa masa, shiru bai dawo hannaycinsa ba kuma Umad ya saurari harbawar jijiyar wuyarshi, kawai dai rud’u ne da tashin hankali ya ziyarce shi lokaci d’aya.
Musail ne yace “Ku kaishi d’aki ku kwantar, bari a kira likitan cikin gida sai ya dubashi.”
Cire masa kambun kanshi Kossam tayi sannan su Umad suka ja shi zuwa d’akin Umad d’in da ya sauka. Inda Musail ya kira babban likitan ya kuma ce yana zuwa yanzu.
Kossam dake tsaye juyowa tayi kan Juman da mamakin da har yanzu bai barta ba tace “Yar uwa, garin ya haka ta faru? Yarinyar da nake mafarkin ta zama sirikata, sai ku ku tabbatar min da mafarkin.”
Kama hannunta Juman tayi tace “Muje ciki sai na fad’a miki komai.”
Zasu wuce Juman ta sake juyowa ta kalli hadiman gidan tace “Dan Allah ku samawa kowa masaukin da ya dace da shi, sannan kayan nan babbar tsaraba ce daga surukanmu, dan haka ku adana su waje mai kyau, anjima zan zo na duba.”
Ciki suka shige hadiman kuma suka shiga yin abinda ta umarcesu, Ayam kuma mik’awa wata hadimar kwandon hannunta tayi sannan ta kama hannun sarauniya Bilkees suka nufi hanyar d’akinta, juyowa tayi ta kalli k’annan Bukhatir tace” Ku zo mu je.”
Bin bayansu sukayi su ma suka yada zango a d’akinta.
*Wudar* ma cikin gaggawa likita ya zo ya duba shi, jininshi ne yayi mugun hawa sosai hakan yasa aka masa allurar bacci mai nauyin gaske, Umad da Haman barinshi sukayi a d’akin, inda Umad ke cike da mamakin abinda ya jawo wa mahaifinshi shiga wannan halin, shin soyayyar da ya ke wa Ayam ce ta kai wannan matakin? Ko kuma dai ya shirya wani gagarumin abu ne ga auren d’an daya rage masa? hakan yasa jin yayi auren ya jefashi a wannan halin? Ko kuma dai alhakin mahaifiyarsa ne Allah zai fara cire mata hakk’inta dalilin Ayam?
*A gurguje*
A al’adar k’asashen dama idan har an amince da neman izinin auren, to a cikin kayayyakin da iyayen miji ke kawowa har da kayan gyaran jiki, dan haka Juman bata tsaya b’ata lokaci ba wajen duba kayan nan ta d’auki duk abun buk’ata wanda ya shafi dukhan, dilka, madara, zuma, kurkum, haska amarya, man ja mai kyau. Hankali kwance a nutse suka sakata tsakiya ana ta darjewa a nutse, jakadiyar Juman da ita kanta Juman d’in, ga kuma Kossam da ta aje surukantaka a gefe tana shafawa Ayam d’in dilka da kan ta, ga kuma sarauniya Bilkees dake zaune tana taimaka musu da wasu abubuwa.
Awa d’aya suka d’auka kafik daga bisani tayi wanda da zallar sabulu na zuma da madara, tana fitowa Bilkees ta bata madarar da aka dama da kauri da sanyi kad’an ta shanye tas, mai ta shafa wanda shi ma duk cikin kayan da aka sako ne sannan ta saka sassauk’an riga ta gabatar da sallah la’asar, bayan ida sallarta ne Kossam ke tambayarta abinda ta yi, nan Juman da Bilkees suka fayyace mata komai game da addinin har saida ta ji sha’awar shi ga ita ma.
Ko da duhu ya fara shigowa masarautar Khazira ta d’auki harami ta kuma canza kala, dan kuwa ma’aikata daga kampani na musamman a wajen tsara wajen taro aka d’auko suka k’awata gidan, walwali mai d’aukar ido da kayan ado da alatu ta ko ina aka zagaye gidan kamar ba shi safiyar yau yayi gobara ba, shiga da fita kawai hadimai ke yi suna ta harkoki na k’ayata wajen bak’i da abubuwan ci da shi, haka ma babban tureburin da amarya da ango za su zauna.
A d’aki kuma masu kwalliya na musamman aka kawo wanda kafin su shiga saida aka cajesu da akwatin kwalliyarsu, mai gyaran kai tana aikinta cike da k’warewa, haka mai wankin k’afafu da yanke farce, sannan aka mata gyaran farce na hannu aka shafa mata verni kalar fari da ba’a cika shaida an saka ba.
Duk da har yanzu gashinta bai yi tsayi ba, amma da aka mishi wani irin gyara mai murd’ewa sai wanda zai ganta a lokacin ya d’auka tsayin gashin ne yasa aka mummurd’eshi hakanan, gashi an bar mata shi a yanda yake kalarshi ta asali maroon da tsili tsilin yellow yellow. Saida aka d’auki minti talatin ana gyara mata girarta da girar idonta, yanda ake so su tsaya cak ba tare da sun rabe da juna ba sannan su mik’e kuma su lank’wasa, daga haka aka ci gaba da mata saukakk’an kwalliya wacce ita kanta ta zuba ido take so ta ga yanda fuskarta za ta yi da kwalliya abar da bata tab’a yi ba.
*Alhamdulillah.*
GIPHY App Key not set. Please check settings