Lu’u Lu’u 42

Advertisement

Bismillahir rahamanir rahim_

*42*

 

Wani mahaukacin yadi ne aka mishi babbar riga da yar ciki kalar bleue daya k’ona, bak’ak’en takalmi ya saka da hula bak’a kamar d’inkin da aka ma rigar, haka ma agogon hannunshi ta fata bak’a ce, yayi kyau matuk’a ya kuma gama had’uwa.

Haka ma Haman matsayinshi na babban amininshi ya shirya cikin farin yadi, shi ma tsaf ya fito abun shi gwanin sha’awa, yana mak’ala agogon hannunshi fara k’irar Gucci Umad kuma na fesa turare Rexona mai sanyayyan k’amshi ya kalli Haman kamar mai tuhumarshi yace “Haman, matata ka ke so ko?”

Da wani irin sauri Haman ya kalleshi yana rarako ido kamar zai had’iyeshi da su, tabbas da abinci yake ci da ya sark’e, ganin ya dakata daga d’aura agogon yasa Umad aje turaren hannunshi ya kama hannun Haman d’in ya fara d’aura masa agogon, d’aga idonshi yayi cike da miskilanci da kayar da gaba ya zuba a fuskar Haman da ya gama rud’ewa yace “Na san shirinku kai da yayarka, ta so ka auri matata saboda mijinta ya hak’ura da ita dan ita ma ta samu daraja a gunsa, k’ok’arinta mai kyau ne, saidai niyyar ce mummuna, hakan yasa na muku uzuri kai da ita d’in, komai ya wuce.”

Kanne masa ido d’aya yayi yace” Ka birgeni kai ma, saboda ni da kai duka manufar mu d’aya ce ta tunkarar Zafeera, wato *soyayyar d’an uwa*.”

Yana gama mak’ala masa ya bubbuga kafad’ar Haman d’in sannan yace” Mu je, lokaci ya yi.”

Da kallo ya bi Umad d’in sanda ya juya zai fita, jin bai biyoshi a baya ba yasa ya juyo yana kallonshi, murmushi ya sakar masa yace” Come on! Mu je mana.”

Da k’yar ya d’aga kansa ya jinjina alamar to, jiki a sab’ule ya fara takawa har saida ya kai kusa da Umad, sai kuma ya had’e fuska yana kallonshi yace” Amma dai fatana shi ne a ce babu soyayyarta a zuciyarka, Haman kishinta na ke fiye da yanda ka ke tunani.”

Advertisements

Ya d’aga k’afa zai fita Haman yayi saurin rik’o hannunshi yace “Umad, ba haka ba ne, ka fahimta mana, ni dama ban tab’a jin son ta a zuciyata ba, kawai ina yi ne saboda yar uwata.”

Wani murmushi ya sakar masa marar manufa sannan ya fice a d’akin ba tare da ya sake bi ta kan Haman d’in ba, d’akinshi ya shiga inda aka kwantar da mahaifinshi, kwance yake idonshi a rufe yana bacci har yanzu, tsaye yayi bayan ya rufe k’ofar yana kallon mahaifin na shi, a raunane ya girgiza kai yana tambayar kan shi “Wannan wace irin jarabawa ce?” *Lu’u lu’u*? Kowa ita ya ke son samu, kuma dan duniya kawai, babu mai son ta a yanda take sai dan d’aukakar da zai samu ta dalilinta, yanzu ga son zuciya ya d’ora kowa a muk’amin daya dace da shi, mahaifinshi wanda ya haifeshi yana kwance da ciwon son matar da ya ke aure, bugu da k’ari matar nan ta gama haramta ga mahaifinshi saboda abinda ya shiga tsakaninsu. Ina ma kafin ya musulunta ne lokacin bai samu ak’ida ba, da yana iya jarumatar sadaukarwa mahaifinshi ita, sai ya ga me zai faru bayan haka, amma yanzu ko mutuwa ya yi mahaifinshi ba zai tab’a aurenta ba.

A hankali y k’arasa kusa da shi ya zauna bakin gadon, rik’o hannunshi yayi na dama mai d’auke da zobuna na alfarma biyu ma su d’auke da dutsin gwal d’aya kuma lu’u lu’u, murza hannun ya shiga yi sanyaye kamar zai fashe da kuka y furta “Abba na.”

Yanda yake har yanzu haka yake ba wani canji, dan haka ya sake furta “Abba na…bud’e idonka ka ganni, ni ne Umad d’in ka.”

Duk da bai bud’e idonshi ba amma sai na’urar dake gefen gadon mai daidaita bugun zuciyarshi da numfashin shi ta d’an fara k’ara tin! Tin! Tin.

Da sauri ya kalli na’urar sannan ya sake kallon Wudar da k’wayar idonshi ke motsawa duk da idon rufe suke, alamar yana so ya bud’e idon, sake matsawa Umad yayi daf d shi a sanyaye ya sake cewa “Abba…”

Sannu a hankali sai kuwa ya bud’a idonshi tare da kiran sunan “Umad…”

Cikin wata murya mai gurguri dake nuna jikkatuwa ya yi maganar, da azama Umad ya sake maida hankalinshi akan mahaifinshi ya amsa da “Na’am, ina jin ka Abba na, bud’e ido ka gani ni ne.”

K’ara bud’a idon Wudar yayi ya sauke a kan Umad ya rik’e tafin hannunshi gam wanda ke cikin hannunshi, shi ma Umad taimaka masa ya yi ya sake had’e hannayen na su da kyau, cike da kulawa da buk’atuwa Wudar ya saka idonshi cikin na Umad yace” Zafeera…Zafeera Umad.”

Kamar saukar mari haka ya ji maganar da saida ta sa shi rufe idonshi, daidaita nutsuwarshi yayi a hankali ya bud’e idon ya kalleshi, a sanyaye a kuma ladabce yace” Baa, Ayam tana nan lafiya.”

Cike da damuwa ya nemi tashi zaune yana fad’in” Ka kai ni wajenta Umad, ina so mu yi magana da ita ka ji, ka kai ni wajenta.”

Mayar da shi yayi kwance yace” Shiiiii! Ka nutsu Abba na, za ta zo, Ayam za ta zo.”

Advertisements

Kallonshi yayi cike da gigin tsufa yace” Umad, da gaske wai ka aureta?”

Zuba masa ido yayi na d’an lokaci da tunanin amsar da zai ba shi, nauyayyen numfashi ya sauke har iskan bakinshi na fitowa kafin ya d’aga bakinshi da k’yar yace” E Abba, na aureta.”

Da sauri ya zabura ya tashi zaune yana fad’in” Umad kana da hankali? Baka san cewa ni nake so na aureta ba, yanzu matar ta w…”

Zunbur raba hannayensu tare da mik’ewa da sauri tsaye ya bashi baya, dafe k’ugu yayi yana feso huci daga bakinshi. Fahimta da ya yi kamar ya fara hassalashi kuma ya san waye shi yasa ya marairaice yace” D’ana, yanzu ba za ka saurare ni ba? Ba za ka zauna na fad’a maka damuwata ba?”

Juyowa yayi ya kalleshi ya ma rasa me zai ce masa, ba tare da ya ce komai ba kawai ya juya ya fita a d’akin duk da kuwa yana ci gaba da masa magana, saida ya rufe k’ofar ya kuma sauke wani wawan numfashi sannan ya ja tsaki ya kalli k’ofar d’akin, girgiza kai kawai yayi ya kama gabanshi.

*Filin taron*

A d’an k’ank’anin lokaci filin ya cika da manyan bak’in da dole zaka san bikin na manya ne, jama’a ne ta ko ina ka kalla, kama daga bak’in da aka gayyata, wasu a tsaye suke yayin da hadimai da kuma ma’aikatan da aka d’aukosu dan rabawa bak’i abun sha da abinci suke ta kai da kawowa, wasu kuma na b’angaren da kujerun zama suke suna zaune, duk wanda ka kalla yana cikin shiga ta alfarma, ko dai jinin sarauta ne ko kuma wani babban ma’aikacin gwamnati.

Juman da mahaifiyar Bukhatir da kuma Kossam ne suka fito da Ayam, tana tsakiyarsu cikin doguwar riga kalar ruwan gwal ta tattausan yadi, babban mayafi suka rufe mata kan ta da shi sannan suka saka mata k’ananun abun da suka rik’e mata shi, sannan aka saka mata wani k’aramin kambu a kan ta wanda ya dace da kalar kayanta, sosai fuskarta ta yi kyau ta fito shar shar da ita.

A tsanake suka rakata kan kujerar da aka tanada domin su suka zaunar da ita, daidai lokacin Umad shi ma ya shigo falon, Kossam ce ta masa alama da ya zo, a hankali kuma a gadarance ya shiga takowa saida ya zo ya tsaya, kamashi tayi ya zauna kan kujerar shi ma, kallonsu sukayi suka saki murmushi, Kossam wata yar k’walla ta share tare da fad’in “Kun yi matuk’ar kyau sosai, Allah kareku daga sharrin mutane.”

Da sauri Umad ya d’aga idonshi ya kalleta jin ta ambaci Allah a bakinta, wani murmushin ta kuma sakar masa ta lumshe ido alamar “Kar ka damu.”

Hannu Juman ta kai kan farantinbsilbar dake hannun adimarta ta d’auki farantin silbar mai d’auke da had’in madara da zuma ta kafawa Ayam a bakinta, yatsina fuska tayi ta d’ora bakinta ta d’an kurb’a sai kuma ta janye bakin, zaro mata ido tayi tace” Shanyewa za ki yi.”

Turo baki tayi ta sake kai bakin tana sha, saida ta shanye tas sannan ta d’auke mata kofin daga bakinta, mayar da kofin tayi ta aje kan farantin sannan ta d’auki wata dunk’ulalliyar madara wacce had’i ne na musamman ake ba wa amarya a wannan lokacin, shi ma a baki ta saka mata ta b’antara ta taune sannan ta cinye sauran ragowar, shi ma dai tana cinyewa yar k’aramar tasa ta d’auke mai d’auke da zuma a ciki farar saka ta saka k’aramin cokali ta dinga ba ta har sau uku sannan ta aje.

Gyara tsayuwarta tayi ta fuskancesu gaba d’aya, akan farantin ta d’auki wata k’aramar kwalbar turare ta mik’awa Umad tace “Sai ka fesa mata.”

Karb’a yayi ya bud’e murfin ya fesa mata a jiki, lumshe ido dukansu sukayi saboda tasirin turaren, sai dukansu suka daure ta hanyar bud’e idonsu kamar babu wani abu da ya faru.

Aje kwalbar ta yi sannan ta d’auki zoben azurfa ta mik’awa Ayam tace” Ki saka mishi a yatsar data miki.”

A sanyaye ta amsa tana kallonshi shi ma kuma kallonta yake, hannunshi na hagu ya mik’a mata wanda yake sanye da wani zoben a yatsar kusa da k’arama, kallon yatsun na shi tayi da kyau, a hankali ta kai yatsunta biyu ta cire mi shi wannan zoben sannan ta saka mishi na hannunta, kallonta yayi sosai murya kasa k’asa yace “Wannan fa mai daraja ne.”

Ba tare data boye muryarta ba ta amsa mishi a yaren Italy tace “Shi ma mai darajar ne.”

Tana gama fad’a ta kalli iyayensu da suma ke kallonsu suna murmushi duk da basu ji me ta ce ba ita, amma zoben na shi d ta saka a yatsarta babba ya k’ara basu sha’awa da dariya, wanda shi ma kuma hakan ya masa dad’i.

Da haka Juman ta dinga gabatar da al’adarta har ta ida sannan suka ba wa bak’i damar zaunawa a mazaunansu dan su ci abinci, sosai d’akin taron yayi shiru dayawa saboda kowa mai ji da kan sa ne, bayan k’arar cokula da takalmin hadimai dake yawon raba abinci da kowane teburi babu wata hayaniyar, sai magana k’asa k’asa kawai da hirar mutane ke tashi.

Ganin hankalin mutane baya kansu yasa Ayam yunk’urawa tare da fad’in “Ya Allah.” Ta mik’e, takawa tayi zata sauka daga matakalar d’aya yace “Ina za ki je?”

Juyowa tayi ta turo bakinta gaba tana jujjuyashi tace “To ai ban san an d’ora dokar hana d’aya daga cikinmu tashi a nan ba.”

Tana fad’a ta juya ta ci gaba da tafiyar ba tare da ta ji daga gareshi ba, da kallo ya bita yana murmushin gefen labb’a, tafin hannunshi yasa ya kama gemunshi dake ta k’yalli yana wasa da shi a ranshi ya ayyana” Rigima ko? To ai na bayar da hak’uri, kuma ma ai halalina ne.”

Wani murmushin ya kuma saki ya bi d’an k’ugunta da kallo, cije leb’en k’asa yayi ya d’an kawar da idonshi kad’an daga kanta yana tuno yar gajeruwar had’uwarsu da ita.

Sake maida idonshi yayi kan ta dan baya jin zai iya kawar da gani gareta na sakan biyu, saidai abinda ya gani yasa ya zaro ido har ya furta “Iyeeeh!”

Bai ankara da ya mik’e tsaye ba saida ya ji ya d’aga kafarsa ya taka k’asa, da sauri ya shiga takawa da gaggawa ya isa gareta, yana zuwa yay karaf ya karb’e kofin kwalbar mai shak’e da ice cream dan bak’in wanda take daf da kai wa bakinta da d’an cokalin k’arami.

Da sauri ta kalleshi suna had’a ido ta kyab’e fuska tace “Sha zan yi fa, kai ma ka d’auki na ka mana.”

Hannunta ya rik’e gam a cikin na shi ya d’ora kofin kan wani tebur sannan ya jata zuwa wani corridor da babu kowa sai masu wucewa.

Neman fizgewa take saida ya kai ta inda yake da buk’ata kad’ai ya dakata tare da mannata da bangon, saida ya mata runfa da k’irjinshi kamar zai fad’a mata sannan ya k’urawa fuskarta ido, hakan ya haifar da kusanci sosai a tsakaninsu ta yanda numfashinsu ke gauraya, k’asa ta sauke idonta tana wasa da hannayenta wanda bai ko bata damar had’esu wuri d’aya ba, cikin narkakkiyar murya a sanyaye yace “Kar ki sha sanyi kin ji…*Sajeeda*.”

D’aga idonta tayi ta kalleshi sai kuma tayi saurin sadda kanta k’asa, a hankali yasa yatsanshi ya tallabo hab’arta ya tilasta mata kallon fuskarshi, k’asa tayi da idonta sosai yanda sam bata kallonshi, daf da fuskarta ya sake matsawa yace” Me ye?”

A hankali ta girgiza kai cikin gargadar murya kamar zata b’alle da kuka tace” Ka…wai dai…na ji..ka kira…fassarar suna na ne da yarenku.”

Mamaki ne ya bayyana a fuskarshi yace” Kenan kinsan Ayam yana nufin Sajeeda ne?”

A hankali cikin dubara ta d’aga kai tare da fad’in” E.”

Gyara tsayuwarshi yayi sosai ya sake babbaketa ta yanda ba zata motsa ba yace” Kenan ni ma kinsan fassarar na wa sunan?”

Shiru tayi bata amsa mishi ba sai k’ok’arin kawar da kanta da take, sake cewa yayi” Uhum! Ina jinki.”

Kallon k’wayar idon shi tayi da sauri tace” *Faruk* mana, na sani ai.”

Murmusawa yayi tare da sake tallabo hab’arta yace” To e ye na hassalar? Ki bani amsa mana da girmamawa.”

Cikin fad’a ta ture hannunshi tace” Ni ka matsa zan wuce.”

Har zata rab’ashi ta wuce ya rik’o hannunta hakan yasa ta tsaya cak, juyawa tayi suka kalli juna, cike da sigar tsokana yace” Ba kya tsoron abinda zan miki idan aka ware mana d’aki ne?”

Da mamaki ta kalleshi tace” Ware mana d’aki kuma? Haka ka ke tunani?”

Gyara tsayuwarta tayi tace” Yallab’ai, ka ga dai ai ina jin kunyarka ko? Kuma ina ganin kimarka da darajarka, to me yasa ba ka ji kunyar abinda ka yi ba?”

Cike da danne dariyarshi duba da yanda take maganar yace” Amma ai na baki hak’uri ko? Kuma na ce zan dinga fara bayar da hak’urin kafin na yi yanzu.”

Hawayen data rik’e tun sanda ya matse mata wuri ne ta ji sun taho mata masu zafin gaske, nunashi tayi da yatsa tace” Dama can da nufi ka yi na farko? To ka sani ni ma n san ‘yancin kai na kuma zan k’waci.’yancina.”

Yatsar da take nunashi da ita ya jawo da k’arfi hakan yasa ta fad’o jikinshi bata shirya ba, matseta yayi a jikinshi sosai ya kuma had’ata da bangon nan, k’ure fuskarta yayi da kallo har ya had’a hancinsu wuri d’aya, cikin taushin murya numfashinsu na gauraya yace “…

 

*Nagode sosai yan uwa da uzurinku gare ni, Alhamdulillah mun gama sabga lafiya.*

 

*Alhamdulillah*

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like
Read More

TARTSATSI 80

Advertisement   *Page 80*   ********************   Tsawon lokaci Hafsa tana zaune acikin mota tana sak’e sak’en zuci,…
INAYAH
Read More

INAYAH 45

Advertisement 45_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Kofa ya dafa da kyau sbd ba zato yaji ta jikin nasa…. Yaune Karo na…
Read More

TARTSATSI 48

Advertisement page 48* ********************** Bayan sun k’are gaisawa ne da Abba sadauki ya fito haraba Hafsa da Salma…
Read More

TARTSATSI 30

Advertisement *Page 30* ******************* Sadauki ya kalleta dakyau yace “Ina saurarenki dafatar dai duk abunda zai fito bakinki…
INAYAH
Read More

INAYAH 55

Advertisement 55_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Daqyar ya iya bude Baki ahankali can qasan maqoshi yace” Nace ki Dena maganan Nan…..…