Advertisement
*👉🏻39*
….Nisha itakam batasan ma zee nayi ba jikinta ta fada tana dariya ta rumgumeta nutsuwata na tatataro na kakalo murmushi dan wani mugun haushi Nisha nakeji da na Sardauna na rasa dalili Dole na rumgumeta tunda banida hujja” my dear ya gida nima nayi missing d’inki ummi tace” Aisha Baby kadai kika gani ko? kunya ta kama Nisha tasaki zee ta miki taje ta rumgume ummi Raiyan” ummi ina yini kanta ta shafa”lfy ya gida da fatan kina lfy? ” Alhmdllh Sardauna gun ghaisha ya ISO ya zauna yana murmushi ya dora kansa kafadarta “momyna kinsan me? ” ah ah sai kafada daddy yayi dariya” wlh Faisal anyi marar kunya ai sai ka fada mata zee ko jin zazakar muryar Sardauna mai fitar da amon dadi kusa da ita da dadadan kamshinsa gaba ki daya ta rasa nutsuwarta wani irin shaukine ya kamata gashin jikinta sai mik’ewa yake tanajin wani iri jikin ghaisha ta koma ta rumgumeta tana sabke ajiyar zuciya ta kalli Sardauna saboda sunyi kusanci dayawa amma koda wasa bai kalleta ba idanunta ta lumshe ta boye kanta jikin ghaisha Sardauna yace” momyna wlh kin kusa yin jiki fah dukansa
ghaisha tayi tana dariya Daddy yace” kya dara wlh nima haka yacemin za ta kara dukansa ya Mike dan dama kusancinsa da zee yayi yawa so yake yabar gurin mik’ewa yayi ya nufi gun ummi Raiyan ya zauna yana gaisheta ya bata labari Nisha nada ciki kunya tasa Nisha mik’ewa tazo ta gaishe da Daddy ta zauna kusan ghaisha ta gaisheta rumgumota ghaisha tayi” masha Allah Aisha Allah ya inganta kanta ta sada zee baby ta rasa abinda yake mata dadi Dole ta zauna ta saki ranta ta rumgumo Nisha” my dear kice zamu bararaje zanyi d’a ko diya Nisha shiru sai lokacin Sardauna ya kalli zee yada take cikin farin ciki yaga tayi masa mugun kyau da sauri ya kauda kansa dan Allah kade yasan me yakeji Nisha tama zee rada” my dear please akwai soyeyar kaza? dariya zee tayi “babu amma gidan Daddah nagani dazu da yamma muje kici ta mike ta kama hannu Nisha ghaisha tace ina zaku? ” ummi nama zataci soyaye nagani gidan Daddah tajata suka fice ghaisha nakiran zee tazo ta yafa gyale itada Takeda ciyayi akai tana fita haka kin zowa tayi tana dariya suka fice
ummi murmushi tayi dan ba karamun dadi takeji ba idan taga ana kaunar zee ghaisha tace Sardauna kaci wani Abu kuwa? murmushi yai” ghaisha banajin cin komai coffee kawai zansha idan nakoma gida” OK zuwa gobe zansa nanuwa mai aiki ta samo ma Aisha yar aiki insha Allah” yauwa momyna godiya Muke” kici gidanku mahabeer ne ya shigo da sallama adakile Daddy ya amsa Sardauna ya Mike ya taresa yana murmushi ya rumgumesa” bro Albishirinka cikin sanyin jiki yace” goro rada yama mahbeer Daddy ya tab’e baki “Faisal Allah yama albarka ina alfahari dakai ako ina murmushi mahbeer yayi ya kamo hannu Sardauna suka zauna mahabeer ya kalli Sardauna ya rike hannusa” Dr namu dan Allah kasa baki su Daddy su yafemun subani matata wlh ina sonta sun rabamu sunsa namata saki daya idanu Sardauna ya zaro ya kalli Daddy” haba my daddy dan Allah ya kukayi haka suna son junansu ku rabasu ghaisha tace “dallah can rufemun baki kasan abunda yayi ne ya fada maka wlh babu kai babu ita sakin mahabeer Sardauna yayi ya Mike yaje gun Daddy ya rumgumeshi “Daddy kuyi hakuri ku yafe masa dan Allah abi komai asannu ku maida musu auransu ajiyar zuciya ya sabke” naji jeka mayi tunani amma idan kun hadu ya fada maka laifinsa kallon mahbeer Sardauna yayi yanaso yaji Karin bayani mahbeer yame nuni sayi magana gobe kafada ya daga Alamar Allah kaimu
Mahbeer gun ummi Raiyan ya nufa ya zauna” ummina dan Allah kiyi hakuri wlh ina son matata ba laifina bane murmushi tayi”haba mahbeer wlh karka damu baby kanwarka ce kainefa kaje kakawo abunka kayi hakuri Daddy da ya huce za’a maida muku auranku godiya yayi mata sosai Najib da hafeeza tun dazu basu gano bakin sai yanzu suka gane inda zancan ya dosa ya kalli hafeeza suna danne dariyarsu amma saida ta fito nawwara tace” kai kai kai da yaya mahbeer kuke ko? Najib yace”Daddy tunda yaya bayaso ni abani mana wani mugun kallo Sardauna ya watsama Najib Wanda yasa hafeeza takusa sakin fitsari aguje tayi hanyar bedroom yace”wallahi zakuci ubanku waye kukewa dariya ai tuni ta banko kofar cikin wani taku ya nufi Najib “dan ubanka matar yayan nakace kake cewa abaka auranta ya fada idanunsa sun kade sunyi Ja Najib ganin idan fa Sardauna ya damkesa ilatashi zaiyi yasa ya Mike da Sauri yayi gun ghaisha tsawa ta daka masa” Dan gidanku karkazo mun nan Mara’s kunya Daddy ne ya katse Sardauna “Faisal zo nan yi hakuri ai gaskiya ya fada wlh sai na aurawa Najib ita yo meye aciki mik’ewa mahbeer yayi ransa amugun b’ace yabar gidan Sardauna wani irin duhu yake gani ransa ya baci sosai da furucin Daddy duk da yasan ya haramta zee har abadan bazai ta son matar yayansa ba bayan hakama sauran wani Dan kar gano irin Bacin ran da yake ciki ya nufi kicin ya hado coffee yanajin tsanar zee da mahbeer na mamaye zuciyarsa idan ya tuna sun malaki juna parlon ya dawo ya
zauna yasha coffee d’insa kusa da ghaisha tana shafa kansa” auta meye kuma naga duk ka canza shagwabe mata yayi”ni babu komai fah momy murmushi ta Saki tana shafa kansa Daddy yace” kujini da yaro wai shinan fushine yayi ya tafi ghaisha da Daddy suke hirasu banza Sardauna yayi dasu kiss yama ghaisha ya Mike ya nufi daddy yamasa kiss” my daddy good night zamu tafi gida ummi good night dariya tayi” night Dr Daddy yace” Dr anzama dady ko shiru yayi yana Sosa kai ya fice ya nufi part d’in Daddah, bangaran zee baby da Nisha kuwa suna rike da hannu junansu har part d’in Daddah suka iskota da mairan karfe suna hira zee ta fada jikin Daddah tana dariya” tsohuwa munzo cin kaza Nisha kusan tsoho ta zauna tana tsokanarsa”ke Aisha ja’ira amarya ko Dan kwanon tuwa baki kawomun ba ko? dariya tayi zee ta taso” baxata kawoba nakama zamuci ta fada tana shiga kitchen ta daukowa Nisha cinyar kaza guda biyu asoye jajur ta zuba a plate ta kawo mata daddah tabi zee da kallo” iye sannu zainaba masu kwadai anyaku Aisha bakiyi cikiba zee tasa dariya”wallahi daddata shine ma? tsoho yace” oh zamani Nisha taja hannu zee suka koma gefe can nesa da su daddah suka zauna Nisha tace” nagode my dear wlh yawuna har tsinkewa yakeyi sweetheart har ya dasamun suna mai kaza ta fada tanacin naman zee namata dariya Nisha tace” my dear wlh My Dr ya iya soyayya yana kasheni da salonsa nagama haukacewa Akan sa ina mugu mugun sonsa ina ji dashi shidin jarumine wlh dazu bakika kaunar da yanuna munba nida babynsa wlh Yaya Faisal yayi arayuwa zee baby yawun bakintane ya k’ame baki daya hankalinta yayi mugun tashi gudun karta ganota ta Mike tana murmushi “my dear bari na dauko wayata nima na nuna miki pic dinmu da yaya mahbeer dariya Nisha tayi” aikuwa yi Sauri kuma ai iyayan soyayya ne kilama kema
kinyi cikin tun kafinma nayi ficewa zee tayi tana murmushi ta nufi kofar fita tana fita ta labe wani Dan lungu ta zauna ta Dora hannu akai ta fashe da kuka tin karfinta ita kanta batasan na menene ba yi take batada niyar fasawa,sai tari take tana dafe da kirjinta har lokacin da Sardauna ya shigo part din Daddah kuka zeey takeyi anutse yake takunsa amma da karfi karfi saboda yanayin bacin rai da yake ciki yana dab da shiga parlon daddah yakejin shashekar kuka Ana tari gabansa ya fadi kukan kamar Nisha kamar Zee lungun ya nufa ya ganta ta kifa kanta saman cinyarta tana kuka tsaki yaja ya juya ya tafiyarsa har yasa kafarsa parlon yaji bashida nutsuwa wani mugun tausayinta ya manaye zuciyarsa duk da baisan dalilin kukanba yasan bata wuce an rabata da mijinta tsaki yaja ya dawo gunta yayi tsaye daga nesa”Zainab ke me kikeyi Ana kika ishi mutane da kuka kiyi hakuri za’a maida muku auranku tashi maza ki shiga gida ghaisha na kiranki kiyi kokarin hana wannan tarin Dan ba alheri bane wani mugun haushinsa nakeji jinake kamar na tashi na
shakoshi na fadashi da duka banza na masa naci gaba da kukana harda shasheka wata uwara tsawa ya bugamun wacce ta tsoratani mutika” wlh zainab idan baki tashi ba zanyi mugun sab’amiki tashi kifice ko naci ubanki jikina ya dauki rawa na Mike tsaye nayi kansa jikinsa na fada na rumgumesa gam ina wani irin kuka”Yayana don Allah kadena mun tsawa haka abun yamun yawa ni bansan ma meke damu naba. tunda aka raba auranmu da Ya mahbeer da safe banida nutsuwa shine wai Nisha wai take tamun zancan kuna soyayya yo ni ina ruwana Yayana kacewa su Daddy su maidamun aurena zan zauna nima inason baby irin na Nisha wani mugun haushinta yaji da kishi ya tokareshi ya ingijeta zata bigi bango yayi saurin tarota Dan bazai iya barinta ta fadi ba saman kirjinshi ta fada makaleshi tayi ashagwabe tace” Yayana da naji ciwo fa kaidan kanada matarka shine zaka zalumci kanwarka ta fashe masa da kuka tana dukansa akirjinsa gabaki daya Sardauna baima san abinda yake masa dadiba tunda yaji zee baby a cikin jikinsa nutsuwarsa ta kwace masa azababben sonta da tsantsar kaunarta ya taso masa muryata ya tsinto tanacewa”Yaya Sardauna muje kasa amaidani gidana zan zauna kaji janyeta yayi jikinsa ya hankadata ta fadi ya fice yabar gun tashi tayi da gudu ta biyosa tasha gabansa tana rusar kuka idanunsa ya rumtse zuciyarsa na bugawa da karfi Dan ciwo take masa bakin cikinsa zee ta auri waninsa har an ketata tazama saura bakin cikinsa na biyu sakin da aka mata anmayar masa da ita bazawara gashi babu aure tsakaninsu kuma ko akwaima saide ya mutu da sonta bazai taba aurantaba kuma sauran wani jinsa yake kamar yabar duniyar saboda bakin cikin daurewa kawai yakeyi gashi bayason kukan zee gashi ta tisasa gaba tana masa kuka
idanunsa ya bude ya kamo hannuta gudun kar wani ya gansu lungun suka koma ya tsayar da ita ya tataro mata gashinta da yarufe mata fuska ya daure mata hawaye sai kwaranyo mata yake saman fuskarta fuskar ya riko ya goge mata hawaye da hannunsa ya ruko hannayenta duka biyu” zainab idan kinaso Nasaka amaida muku auranku to kiyi shiru ki hadiye kukanki ko nayi mugun sabamiki hadiye kukan nayi na dago muka hada idanu kaina na Sada saboda bazan iya kallon wannan idanunsa masu mugun dafi ashagwabe nace”Ya Sardauna na daina kukan kayi hakuri tarine ya sark’e Sardauna ya Saki hannuwan zee yana dafe da kirjinsa yana tari ya sunkuya arikice zee ta sunkuyo ta rikeshi”Yayana menene mura kakeyi sanu ta fada tana bubbuga bayansa ganin yaki dainawa ta rumgumeshi ta fashe da kuka”Yayana menene Dan Allah kabari kaji kalli yada jikinka yake karkarwa kuwa ta fada tana riko kansa ta kora masa idanu yada yake tarin kansa ta tallabo ta shafi fuskarsa
mai kewaye da kwantaccen saja” Yaya Sardauna kabari ta fada tana kifa fuskarta saman tashi tana kuka ganin bazai bar tarin ba bata tsaya komaiba ta had’e bakinsa yana mata tarin kokarin janyeta yakeyi yana girgiza mata kai gashi yanaso yatsayar da tarin Abun ya faskara zee idanunta sharkaf da hawaye ta lalubo harshen Sardauna tana tsotsa cikin nutsuwa cikin ikon Allah tana fara tsotsa tarin ya tsaya
idanu ya zuba mata yada take tsotsar bakinsa tana hawaye wani mugun kishine ya tokare masa zuciya bakinsa ya zare yana huci ya hankadeta ta fadi k’asa fashe masa tayi da kuka”Yayana duk ka canza mun bansa me nayima ba please kabarni nasha sweet yawunka wata biyu ban shaba Dan Allah karka hanani yayana ta fada tana ririkeshi tana kuka”Ya Allah wai ni wace irin masifa ce take tunkaroni zee kibarni na huta karki kasheni please yi shiru hakan babu kyau kiyi hakuri za’a maida muku auranku bari kukan ya fada yana janyeta daga jikinsa shagwabe masa tayi cikin shashekar kuka tace” Yayana to muyi kiss ni inaso nasha yawunka kaji ta fada tana Kara shigewa jikinsa tana kukan sangarta”Yaya Sardauna kabani yawunka kar na mutu wlh mutuwa zanyi ta fada tana ririkeshi tana masa wani irin kuka mata tab’a zuciya tana kiran sunansa Yayana Sardauna Numfashinta ya fara sama da k’asa jikinta ya fara Saki ta fara wata irin karkarwa idanunta na lumshewa arikice ya mannata jikinsa yana girgizata” zainab ke meye haka wai ya kikeso nayi da raina cikin fitar Haiyaci tace” Yayana Sardauna abubuwa sunmun yawa gashi ka kimun abunda zan samu nutsuwa ga bakin cikin abinda matarka ta fadamun ya tsaya azuciyata Yayana zan mutu gwarama na mutu na huta da bakin cikin duniya ta fada tana tari tun karfi jikinta na rawa”Yayana danne min kirjina ciwo yakemun ta fada tana wani mugun tari wata wawar rumguma ya mata yana ririketa yana buga bayanta cikin tsawa yace “inji ubanwa zaki mutu saboda ni kiyi hakuri karki kamu da irin ciwona kuma bazaki mutuba inko hakane wallahi saide mu mutu tare………………..✍🏻
Advertisements
GIPHY App Key not set. Please check settings