Advertisement
book 2 ππ»4&5*
….cikin nutsuwa zee ta fara kissing din bakin Sardauna tana kuka fizge bakinsa yayi ransa abace yace” wlh My Abulena sai na hukuntaki zaki san kinyi shaye shaye kuma kinyi yinkurin guduwa ki barni keda kikace baki sona ina ruwanki dani da zakiyi kissing DINA.dukansa ta fara cikin maganarta ta maye tana shashekar kuka tace”eh na fadi bana sonka sai me yo ni ko banda miji me zanyi da kai kaifa mijin Nisha ne da karfi tace nace bana sonka na tsaneka kabarni nashiga duniya mana ina ruwanka dani ko mahbeer baya takuramun bare kai kalan dangi. Bakinsa ya ciza bai kulataba sanin bata haiyacinta ya barta zai hukuntata ahaka har ya isa bakin titi gun mota Hamraz ya
taresa yana murmushi yace”Alhmdllh an sameta. kai Sardauna ya daga Hamraz ya bude masa mota ya shigar da ita baya ya zaunar da ita ya zungureta akai ya rufo kofar ya shiga gaba ransa duk babu dadi har yanzu haushin katon mutumin nan yakeji Kenan da shine zai gudu da zeey baby. lips d’insa ya ciza da karfi yanajin yada take sambatun maye Hamraz na masa magana yayi banza dashi dan fa Sardauna idan yan shirunsa sunzo abacin rai sai hakuri. su Ammi ne suka ISO Hassan ya bude mota suka shiga Ammi ta zauna ta janyo zeey jikinta Jannat suka zazauna amma duk sun matsu hussaini ya rufe motar Hamraz yaja suka tafi zee tace” Ammi kinsan abinda matar Sardauna tamin. bakinta Ammi ta rufe mata dan shirman yayi yawa manal ma hakance sambatu kawai take tana cewa”
habibty zanci gutsun uwar wacce ta tabaki dan ubanta Jannat baki ta rufe mata hassan yace” Allah ya shiryeku ku daina shaye shaye. Hamraz gudu yayi sosai amma saida Ana sallah isha’i suka isa gashi ko magarib basu yiba. yana parking akofar gidan hussaini ya fito ya bude gidan Sardauna ya fito ya bude bayan motar ya dauki zee su Ammi suka fito Hamraz yace” Sardauna zanje gidan bayan na Rama salloli zan kawo muku abunci. ” OK thanks Hamraz ya fadi yana shiga ciki rungume da zee su Ammi na biye dashi part dinsa ya nufa da ita. yana shiga ciki ya wurgata saman gado ya murzawa kofar key ya shiga bathroom ya dauro Alwalla ya fito ya hau kan
dadduma ya tayar da sallah. zee kuwa zaune ta tashi ta sabko daga saman gadon tana tangadi tace” ni guduwa zanyi ba ruwana dakai kofar ta nufa gashi tafiyar tata agwale ga maya ga zazzabi ya rufeta kofar ta murda ta kasa budewa. tayi zaune dirshin tana kuka azo abude mata kofa sai rawar sanyi take.dan zazzabine ya rufeta. Sardauna najinta babu yada zaiyi saida ya gama sallolinsa anutse yayi Addu’insa ya Mike ya shiga bathroom ya hada ruwan gumi ya fito ya nufi gunta matsawa ta farayi daga zaune” karka tabani mugu azalumi na tsaneka ai kasan ina Sonka kabarni ka auri wata Nima na auri wani
Sardauna bai saurareta ba ya ciccibeta tana dukansa ya nufi bathroom da ita ya cire mata kayan jikinta ya nasata cikin ruwan gumin saida tajima sosai ya mata wanka sai sambatu take ya nadota a towel ya rungumo abarsa ya fito ya zaunar da ita bakin gado ya dauko mai ya shafa mata ya kwantar da ita daga ita sai towel ta zabura ta Mike wata uwar tsawa ya buga mata” dan ubanki koma ki kwanta ko kiga abinda zan miki yanzu wlh. ai jikinta na rawa ta kwanta tana kuka tsaki yaja ya nufi kofar ya bude ya fice. a parlo ya samesu manal tayi bacci da sallama ya shigo Ammi tace” zainaba tayi bacci ne.” Batayi ba hassan tashi kawomun kayanta. Mik’ewa yayi
ya tafi ya dauko masa Sardauna yace” Jannat tashi ki kai yar mayanan gidansu kema ki wuce gida kar anemeki gobe kizo muyi hira da safe Ana jiranki pls karki makara. ” to shikenan zanzo ta Mike ta tada manal hassan ne ya iso da akwatin zee wacce Abu rahman ya hada mata kaya Sardauna yace” hassan ku rakasu har gida. suka amsa da” to ya amshi akwatin yace” Ammi dan Allah idan Hamraz yazo akawo mana abuncin mu bazan fitoba zazzabi takeyi. ” to zan shigo da kaina Allah bata lfy”Amin yace ya fice su Jannat suka fito manal na tangadi su Hassan na rike da ita suka fice. Sardauna yana shiga yaga zee tayi bacci hawaye sun bushe mata afuskarta barinta yayi dan tayi saukin wartsakewa dan ta Rama sallah jikinta ya taba yaji zafin ya rage sosai akwatin ya
bude ya ciro wata duguwar Riga mai kauri ya hauro saman gadon ya Samata rigar ya daure mata gashinta ya rungumeta ya shigar da ita jikinsa sosai kamar zai maidata cikinsa ya jamusu tattausan bargo ya lulubesu yana shafar bayanta yanajin hucin zafin zazzabin jikinta a jikinsa ya shiga danna mata jikinta yanaji tana nishin zazzabi tana Kara shige masa sosai yake danna mata jikinta.ga dumin jikinsa da tasamu ga tausa kusan 40 minute yaji zazzabin ya sauka sai gumi yake karyo mata bargon ya janye ya janye jikinsa ya matsa gefe ya zuba mata idanu tana bacci cikin nutsuwa bakinta yana motsi. karan buga kofa yasa ya Mike ya sabko ya nufi kofar ya bude. Ammi ce da babban tire ta hado musu komai na bukata ya amsa tace” Hamraz yana gaidata da jiki. “Ammi shiga mana ki ganta bacci take” kabarta ja’irar yarinya ni na tafi kai ya kada yaje ya ajiye tiran ya dawo ya
rufe kofar ya cire jallabiyar ya saka “3quarter da karamar Riga ya nufo gun zee ya sanya tattausan hannuwansa ya dauketa ya nufi bathroom da ita sabka ruwan da naji afuskata yasa na bude idanu na sabke ajiyar zuciya jina jikin mutum yasa na dago na kallesa cikin tsiwa nace “sakeni da jaraba kwarto kawai bakina ya dalle mun da karfin gaske ya min wani mugun kallo ai ba shiri na sada kaina ina gumguni na shiga dukansa saboda tunowa da abunda yamun direni yayi k’asa ” maza kiyi alwalla ki fito ya fice tsaki naja nayi alwalla na fito har yanzu inajin gabana yanamun zafi ina dingisawa na fito hawaye ya wankemun
Fuska saman kujerana na ganshi zaune yanacin abunci fuskarshi ahad’e tsaki naja na nufi gun akwatina da nagani na dauki mayafi na yafa na hau kan darduma naji yace” yar shaye shaye sallah magrib da isha zakiyi ki gama ina jiranki. Banza na masa na tayar da sallah. Sardauna saida yaji cikinsa ya dan taso ya bari ya Dora coffee ya mike ya shiga toilet ya wanke bakinsa ya fito yasa kayan bacci ya murza mansa mai kamshi ya fesa turare ya dauki wayarsa ya haura saman gado ya danna number Nisha. can ko Nigeria daide lokacin Nisha tana zaune aparlo bakin cikin duniya ya ishe tayi alkawalin bin shawara matar zata zubar da cikinta ta kuntatawa Sardauna yada ya kuntata mata taga kiransa ya shigo
Advertisements
ta danna ta Kara akunnata da sallama. murmushi ya Saki ya amshi sallama” my Neesher ya kk ya babyna…? daga can ta Saki murmushi tace” my Dr muna lfy sai rashinka wlh Dr wani mugun mafarki nayi amma ba komai nayi Addu’a. Sardauna yace “matar Dr namefa ai dai ba akan cikina dake bane ko…? ” wayyo sweetheart bari kadawo zan fada maka yaushe zakazo” gobe insha Allahu ki daure kizo tarbar mijinki nayi missing dinki kinji mamar babyna..?” Zanzo mijina I love u my Dr. murmushi yayi ya sakar mata kiss ta wayar sukaci gaba da hira. jikin zee baby ko ina b’ari yakeyi wani irin mahaukacin kishine ya rufeta nan take zazzabin ya dawo mata yada taga Sardauna yanama Nisha tasan ita kadaice azuciyarsa kukanta ta danne tayi Addu’a ta shafa ta kwanta saman
Dardumar tana rawar sanyi amma batayi kukaba batada hujjar yin hakan. Sardauna sun jima suna hira da Nisha kafin suyi sallama ya dago yaga zee kwance tana rawar sanyi da Sauri ya zabura ya sabko ya nufo gunta yana zuwa ya dauketa yaji jikinta zafi rau saman kujera ya nufa da ita ya zauna yana rungume da ita idanuna na lumshe dan nayi alkawalin bazanyi kuka ba kuma bazan Nuna kishiba magana ma bazan masaba zan hakura na jure har muje gida na fadawa mahbeer duk irin iskancin da yayimun”my zainab bude idanuki kici abunci kisha magani ban musaba na bude ya bani tea nasha
yaci gaba da bani abunci abaki na amsa ko kallonsa banba har ya gama bani yaban magani nasha duk ina jikinsa ya Mike ya ciremun kayana ya barni sai pant da bra ya kwantar dani shima ya kwanta ya kashe wutar dakin ya daukeni ya Dora kirjinsa ya rufemu da bargo yana shafar bayana ahankali yana dannamun jikina ko motsi banyi ba nazame masa kamar gumki birkitoni yayi ya mannani jikinsa ya matseni sosai ya tallabo kaina yana huramun iskar bakinsa” my bugun numfashina zainabata my Abulena menene. shiru banyi maganaba” sweet baby kimun magana meyasa kika mareni saboda zafin kishinki zainab kina masifar sona sona yamiki mugun kamu meyasa kikaso shiga duniya saboda na kusanceki zainab ina mugu mugun sonki ina kaunarki wlh da kekikemun son da nake miki wlh yanzu da kinbar duniyar dan bazaki iya jure abun da na jureba. idan munje gida duk abinda kikaji kika gani kiyi tawakali ki amshi kaddara. Wani mugun haushinsa ya kamani amma bance komaiba na nutsa kaina kirjinshi ina fitar da wani irin numfashi tamkar numfashina zai tsaya
Sardauna jin yada zee numfashinta yake sama da k’asa yasa ya dagota “zainab wai meyasa kikemun haka yanzu don girman Allah meye na miki na Bacin rai kalli yanda numfashinki yake neman daukewa. yana rufe bakinsa zainab ta sume masa cak numfashinta ya dauke akidime ya zauna tana rungume jikinsa ya kwantar da ita ya sabko ya lalubi makunin wutar dakin ya kunna ya dauki robar ruwa ya kurbi kadan ya hauro gadon ya dauketa ya rungume ya tallabo kanta ya Dora bakinsa ahancinta ya fesa mata ruwan ahancinta da karfi ajiyar zuciya ta sabke da karfi numfashi na fita da Sauri amma idanunta alumshe hamdalah yayi ya kwantar da ita ajikinsa ya rungumeta gam yaja bargo ya rufesu yana tofa mata Addu’a yana shafa bayanta da gashinta ya tallabo kanta ya Dora bakinsa anata yana Kara busa mata numfashinsa tana Shaka sosai dan idanunta biyu tayi alkawalin karyatashine zata Nuna masa bata sonsa bata kishinsa tun tanajin yada yake hura mata numfashinsa tana shakar kamshin bakinsa har bacci ya dauketa shima ahaka bacci ya daukesa bakinsu cikin juna bacci suke sosai manne da juna da sun dan motse cikin bacci sai sufara tsotsar bakin junansu suna tande yawun junansu suna manne kamar zasu koma cikin junansu. Asubah ta gari.
β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘
*Washe gari* a *Nigeria* da misalin karfe hudu na yamma Nisha tana zaune. a parlonta tun jiya acikin farin ciki take irin yada Sardauna ya nuna itace azuciyarsaπniko nace Nisha bakida wayo har kin manta abunda kika ga Sardauna yayima zee Rabia ta kira sai gata” hajiya gani. ” Rabia kawomun kaza ai inada Sauran ta rana. Ko? ” eh bari na kawo miki. ta koma kitchen sallamar matar nan taji akanta atsaye atsorace Nisha ta kalleta ta Mike tsaye” Ma’alumah ta ina kika shigo zama tayi tana dariya. “Aisha Allah ya shiryeki ina knocking fa kikace nashigo abude kina cewa Rabia ta kawo miki kaza. murmushi Nisha tayi tace” wlh na shafa ya gida. ” lfy lau Aisha yau mijinki ke tasoyawa su shigo kano gobe karfe shabiyu ya maganar mu ta jiya ko kin fasa ramuwar.? ” wlh ma’alumah ban fasaba ai nafara dorasa ahanya nace nayi mugun mafarki
Bakiga yada ya rudeba. Rabia ta kawo mata kazar a plate ta gaishe da ma’alumah ta juya Nisha ta faracin naman” ma’aluma bismillah. murmushi tayi ta dauka tanaci tace” yauwa ai naji dadin yada kika masa yanzu amshi wannan. Nisha ta amsa tace” na meye…? ” ki zuba alemo gobe da safe kisha kafin kutafi Kano suna sabka ki fara tarbar Zainab ki rungumeta kina kukan kissa kinsan shegen kishine da ita zataji haushin tabatan da kikayi zatayi yunkurin gucewa sai
ki fadi da gangan wlh daide lokacin cikinki zai zube kuma Sardauna zai Dora laifin kantane yaga kamar da gangan tamiki to turba ta biyu zan doraki ne bayan munyi nasara zubar da cikinki. Dariya Nisha tayi “ai indai zai
saketa na yarda cikin ya zube nasan zan samu wani nan kusa dariya sukayi suka tafa sukaci gaba da hirasu suna shewa. can gida kuwa Daddy bayan sallah isha yana zaune ghaisha tace” Abban Sardauna goben harni zamu tarbo su momy? murmushi yayi” khadijah ai zama zakuyi nida tuwusai zamu da saminu da nuhu da hafeeza sai Aisha. ihu hafeeza tayi ta Mike da gudu taje ta fada jikin daddy. ” thanks my daddy zan gano su hassan da hussaini. Dariya ummi Raiyan tayi minata tace” wato abun yar wariyace ko. ” kudai yi hakuri Najib yace” daddy Nima su Ahmed da bandar zanbi suma suna zuwa” to Allah ya kaimu goben Ashe Kano tanada baki gobe.dariya sukayi hafeeza ta dagashi ta nufi daki ta kira, Ahmed taji da gaskene suna zuwa Kano.
β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘
*Saudi Arabia* tun bayan da sukayo breakfast Wanda daket Sardauna yashawo kanta ta yarda taci ya mata wanka ya bata magani Tasha wlh kallonsa batayi ba duk abunan da yake mata duk yabi ya tada hankalinsa ta fada masa abinda ya mata shiru tai masa Dole yayi banza shima da ita ya rungumeta ya rufesu da bargo ya matseta gam jikinsa. Tayi kamar tayi bacci πzee baby kenan Sardauna na bacci ta janye jikinta ta saka kayanta ta gudu part dinsu Ammi suma duk baccin suke jikin Ammi ta shige ta rungumeta tana kuka Mara sauti har bacci ya kwasheta ahaka dan jikinta akwai zafi duk Tasha magani ga yanda zuciyarta take harbawa da karfin gaske.
Haka suka wuni tunkur har dare zee taki yarda Sardauna ya ganta babu yadan baiba Ammi tace”ya rabu da ita ai Dole zasu zauna acikin jirgi tare. wajan su jannat da manal tun yamma sukazo suna tare da zee bedroom suna hirasu amma zee koda wasa bata fada musu abinda Sardauna ya mataba Sardauna dan yaba zee haushi ya kira Jannat suna hira aikuwa taji haushin dan tana jiyo dariyarsu toilet ta shige taci kukanta dan kal manal ta gani ta fito ta shiga sha’aninta tanaji ya amshi number Jannat yace zai mata wata kyauta ta musamman su hussaini ma dariya sukeyi suna tsokanarsa wai ko ta uku zaiyi da kawar. zee. Hamraz karfe goma na dare ya dawo suka shirin tafiya. karfe shadaya suna Airport harda su manal zee tana rungume dasu suna kukan rabuwa barinma Jannat da taji son Sardauna yamata dirar mikiya dan Sam batasan mijin zee bane cikin kuka Jannat tace” habibty inason yayaki.zee tayi tsayar da kukanta tayi murmushi tace gashi can ki fada masa ko kibari idan ya kiraki ki fada masa maybe ma shima sonki yakeyi tunda ya amshi numberki. cikin farin ciki Jannat ta rungume zee takai kallonta gefen su Sardauna karaf idanunsu ya sark’e da juna murmushi ya sakar mata zee tayi saurin kauda kanta dan tana lure dasu. zuciyarta na bugawa da karfin gaske
zata fadi jannat ta riketa suka zauna Ammi tace”yau bakijin jikinki zainaba kanta ta boye jikin Ammi tana fitar da numfashi da Sauri Sauri hawaye ya wanke mata fuska robar ruwa kusan ammi ta dauka ta bata tana sha sosai Tasha ta cire bakinta Sardauna na lure dasu hankalinsa duk atashe ya dai daurene. Manal tace”wlh kamar nabiku k’asarku jannat tace “wlh. nidai sai naje kwananan insha Allahu.inason Sardauna Zee idanunta ta rumtse tanajin maganar Jannat tamkar an soke mata kibiya aeuciya tun tana jinsu har bacci ya dauketa. can ko gidan Abu Rahman karfe shabiyu Allah ya bashi ikon farkawa daga baccin da yakeyi ya tashi ya fito yana addu’a dan tunaninsa bai bawani jimaba amma sai me yana fitowa yaga abinda yadaga masa hankali komai na gidan afashe Kiran Ammi ya shiga yi da Hassan da zainaba amma ba kowa da gida ya nufi gun dukiyarsa bakomai wayam ya duba wayoyinsa babu laptop babu komai babu da gudu yana ihu ya nufo harabar gida yana cewa”ayau sai nakasheki zainaba shegiya tsinaniya megadi kaima kasheka zanyi yana zuwa kan megadi
Advertisements
yagansa ashimfide kamar gawa yana bacci gun motocinsa yana nufa jikinsa na rawa amma yana zuwa yaga kowace mata anfasa glass dinta an sace mata iskar taya waje yafito kamar zarare ya nufi bakin titi dan yasan tabbas bazasu zauna ak’asar ba gudu zasuyi tax ya tara yace akaishi Airport π€£ niko nace haba ai sunfika wayo ya zasu tsaya a madina suna jiddah. Karfe daya daide aka fara Kiran matafiya zee tana bacci ya ciccibeta sukayi sallama da Hamraz yama jannat sallama tana kuka ta tsaresa da ido”yace kiyi hakuri zan kiraki kinjin. kai ta daga ta rungume ammi da su hussaini sukayi sallama manal ma kuka ranshi zee take gashi tana bacci haka suka nufi jirgi su jannat suna tsaye Hamraz yace “to muje na maida kowace gidansu jannat ta kama hannu manal suka tafi. zee tana rungume jikin Sardauna ahaka har cikin jirgi su Ammi suna gabansu zaunar da ita yayi can lugun Shi ya zauna abaki ya janyota ya rungumeta jikinsa ya lulubeta ruf da
bargon da ya dauko sanin ba lafiya gareta ba hannunsa daga ciki yana shafa bayanta yana sabke ajiyar zuciya yanajin sam bazai iya rayuwa babu zeener dinsa ba karfe biyu daide jirginsu ya tashi karan ya tashi zee ta kamkame Sardauna tana rawar sanyi kara shigar da ita jikinsa yayi ya lulubesu da bargon ya tallabo kanta ya had’e face dinsu yana hura mata iskar bakinsa yana shafar wuyanta cikin raunaniyar murya yace”My Bugun Numfashina meye yake damunki pls ki ajiye hankalinki kina tare da jigon rayuwarki babu abinda zai sameki. Kara ririkeshi tayi ta tura kanta kirjinshi tana shakar daddadan turarensa tana lumshe idanunta harshensa ya fido yana zagaya fuskarta dashi yana lasarta ajiyar zuciya kawai take sabkewa bakinsa ya dora anashi yana tsotsar lips dinta ya dan bude bakin nata yana nemna harshanta gintse hakoranta tayi babu yada baiba sam taki fuskarta ya kamo yakai bakinsa kunnanta murya can k’asa yace”Sanyin idaniyata menene wai meye namiki duk kin canza koda na kusanceki da farko baki mun wannan abunba.
My gidan dadina karki gujeni ina sonki wlh rabu dake daide yake da fitar numfashina zainab ina sonki ya fadi yana kissing din akunnata wani irin zirrrrrr yarrrr taji gashin jikinta duk ya Mike sanyi ya fara ziyartota wani masifafan sonsa na ragargaza mata zuciya ga wani irin feelings da takeji duk da tana cikin bacin rai kasanta ya fara zuba makaleshi tayi sosai tana rikeshi kamar zata koma cikinsa tana lumshe idanunta kome ta tuna sai ta barke da kuka cikin fitar haiyaci tace”wayyo My Sardauna nah Ya zanyi da raina don Allah ya kakeso nayi da rayuwata da sauri ya cafke bakinta ya matseta yana bata wani irin sansanyan kissing mai rai da lafiya yana tsir tamata yawunsa tana hadiyewa cikin shaukin kaunarsa laulausan harshenta mai taushi da zaki ya kamo yana masa shan minti yana juyashi abakinsa lakwas tayi ta narke masa tana jin dadin tsotsar da yakewa bakinta ga yawunsa mai azabar dadi yana tsirta mata tana hadiya amma bata tayasa ba jin dadin shan bakinta da Sardauna yakeyi anan take bacci ya dauketa sai numfashinta yaji abakinsa idanunsa ya bude yaga tayi bacci bakinsa ya zare yana murmushi ya gyara mata kwanciyarta jikansa ya matse abarsa ” my Abulena ina kaunarki pls ki ajiye hankalinki nasan kina sona nima ina sonki. ya ciro kansa waje dagowar da yakeyi suka hada idanu da wani bature ya sakarma Sardauna murmushi ya masa hakaππ»ππ»
Murmushi Sardauna ya maida masa yace”thank you.ya kara rungume zee ya lulubeta sosai yada ko yatsarta baturen bazai ganiba. jirginsu sosai yake sharara gudu asararin samaniya Allah ya kawoku Kano lafiya Amin.
******
Washe gari da misalin karfe goma su Daddy dasu Nisha Ahmed tuwusai hafeeza kawu saminu Nuhu duk suna Malam Aminu international Airport Kano suna jiran isowar su Sardauna da zee baby da yan uwanta da kakarsu. Karfe shabiyu da minti ashirin daide jirginsu Sardauna ya sabka a Kano Wanda saida ya zarema zee ya dawo Sardaunan sa sak ta hakura taci abunci ta kwanta jininsa yana mata tausa da kwantar mata da hankali har Allah ya kawosu lafiya. Yana rike da hannunta har suka sabko daga cikin jirgi su Ammi na biye dasu har suka fito inda zasuga kayansu kayan su Hassan da hussaini suka jido akwatinansu Sardauna yana gaba suna binsa a baya zee sai hararsa take gurin tarbar baki ya nufa dan yasan yan gidansu sunzo tundaga nesa ya hangosu ya murza hannun zee “my sweet babyna kalli daddy. banza ta masa Nisha tana tsinkayosu ta nufo gunsu da gudu cikin farin ciki tana Kiran zee Sardauna ya buga mata tsawa” kibi asannu ko kin manta bake daya baceba kallonsa zee tayi ta fizge hannunta daide lokacin Nisha ta ISO anutse ta”my sweetheart kayi hakuri murmushi ya sakar ta nufi gun zee ta rungumeta fashe da kukan farin ciki zee ma kukan ta saki ta rungume Nisha sosai cikin shashekar kuka zee baby tace” my dear da fatan na sameku lfy ga mijinki yazo gareki ina mahbeer dina ban ganshi ba……………
GIPHY App Key not set. Please check settings