INAYAH 47

INAYAH
INAYAH

Advertisement

47_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Firfito da idanuwa Haj umma tayi tana dauke kanta daga kallonsu batareda tasan tayi hakan sbd rudewa.

Anty juwairiyyah ma dauke kan tayi tana shafawa Al’amarin Inayah Ido Kuma daga Nan.

MAJEED Daya riqe balance dinsa da kyau sbd kiris yarage su Fadi har ita
cikin yanayi na kokarin daidaita kansa da ‘dan fada a shaqe yace”

Inayahhh,,,me ke damunki ne?
Ki nutsu mana…

Matsar da ita yayi daga jikinsa batareda ya kalli kowaba yaja hannunta suka fice dakin.

Itama kasa cewa komai tayi sbd Batasan yariga ya tasoba kodata iso idonta nakan Neman Inda Zata ajiye robar ruwan hannunta Dan haka ba zato tajisa ya miqe Bayan tariga ta iso dad dashi.

Suna fitowa Palo su zubbi dake gyaran yamma da sauri suka sauke Kai qasa daga kallonsu.

Umma yaganah data fito lokacin taci Karo dasu Yana gaf da shigewa da ita dakinta tabisu da Ido cikeda mamaki sbd ita kanta Batasan Yana gidaba alokacin.

Tsakiyar bedroom dinta ya tsaya da ita tareda dakinta ahankali ya dago Yana dauke idonsa daga kan jikinta da kayan jikinta suke lafe cikin yanayi na Dan fada yace”

So nawa Zan fada Miki kin girma ki ringa nutsuwa?
So kike Haj umma tayita Miki fada tunda bakya ji ko?
Meye hakan kike sakawa kina yawo cikin gidan bayan akwai mutane yanzu…

Advertisements

Sanyi jikinta yayi shikenan ita yanzu Abbi fada zaita yimata komai tayi tunda Haj umma bataso,

Ta saba yawo da qananun kayanta na Shan iska acikin gida ko yananan Amma yanzu shikenan sbd Haj umma Abbi fada yake Mata.

Zuciyarta taji tayi sanyi har idanuwanta suka nuna hakan
Jiki a sanyaye tace”

Kayi hkr Abbi bazan Kuma ba.

Juyawa yayi zaibar dakin saikuma ya dakata batareda ya juyoba sbd yanajin kukan datakeson yi ajikinsa Dan yasan halinta Sarai.

Ajiyar zuciya yayi Bai juyo dinba sbd tana ganin ya juyon Zata fara hawaye Dan sauya Masa ra’ayi.

Kofa ya nufa ya fice yabarta da kayan jikinta da dakin dasuka Dan dauki kamshinsa.

Hawayen dataso saukewa agabansane suka gangaro Mata zuciyarta na Mata nauyi Dan kuwa komai na sake tabbata Haj umma Zata wargaza duk wani matsayinta agurin Abbinta.

Daqyar ta iya lallaba kanta ta nufi toilet ta tube ta shiga ruwan zafi a bathtub ta lafe tanajin rashin Dadi a ranta.

Tajima a toilet din kafin ta fito daureda towel blue fuskarta ba wata walwala.

Neu Oil kawai ta shafa tareda spray da mist kadan ta saka free doguwar Riga har qasa Mata nauyi da qaramin hannu tayi sallar la’asar tana idarwa ta koma kan gadonta ta kwanta tana Dan dudduba wayarta kafin ta ajiye tana rasa meke Mata Dadi.

Karshe tashi tayi ta nufi dakin umma yaganah acan yayi kwanciyarta tayi baccin yamma na kusan mintuna arbain zuwa awa daya kafin ta tashi.

Advertisements

Sallar magriba tayi ta sauya kayanta zuwa Rigar sweater da wandon jeans ta saka babbar jacket coat da qaramar hijab iya wuya ta fito riqeda wayarta sai key din motarta Zata tafi asibiti Dan tana leqawa wasu lokutan da daddare.

Umma yaganah ce kawai tasan fitarta Dan abbin baya gida Dan haka tana fitowa Kai tsaye ta wuce ta shiga mota ta fice.

Ta Dan samu wasu patients Dr Abdul dayake asibitin shima yanata fama dasu dayar anmata aiki Amma kaman ta jiwa kanta ciwo gurin yunquri Mai qarfi dayan Kuma jininta yayi qasa sosai gashi likitoci da nurses na fama da ita taqi tsayawa a qara Mata jinin.

Wannan aikin yasa ta tsaya asibitin har kusan qarfe goma batareda Tama lura da time ba.

Suna gamawa taje ta wanke hannuwanta ta fito tareda zaro wayarta dake aljihun jeans dinta taga misscalls na Abbi kusan guda shida dana umma yaganah guda biyu sbd wayan a silent take.

Ya Salam” ta furta a gajiye tana saka Kiran Abbi.

Harta Isa mota ta bude Bata samu Kiran yashigaba Dan haka ta ajiye wayar gefenta ta tada mota tabar asibitin.

Tana shiga harabar gidan Abbinta tafara hangowa tsaye Yana waya da alama fita zaiyi sbd harda key din mota a hannunsa.

Jallabiyace milk a jikinsa duk da dare ne tana iya hango yanda jallabiyan tayi Masa kyau kaman wani Dan matashin black Arab.

Duk wadda ta auri Abbinta tasamu the best miji…..
Au itace matansa ko?
Yanzu Abbinta shine mijinta?

Wani murmushin farin ciki tasaki a fili tana cewa”

Koba komai dai tariga ta alaqantu dashi har abada Dan haka Haj umma matsayinta daban nata dabam.

Da farin ciki kan fuskarta kan fuskarta ta fito sbd mood dinta daya sauya take sbd wannan tunanin datai na tuna shi din fa mijintane itace matarsa.

Gurinsa ta nufa tana sake kallon kyakkyawar fuskarsa dako yaushe take cikeda kwarjini da kaunar ‘yarsa akai.

Cikin yanayin shagwaba tace”

Abbi kayi hkr banji kirankaba wayan na silent kuma hankalinmu ya dauki akan wata patient…
I’m sorry Abbi””‘ta qarasa cikin wani yanayi na sangarta.

Kashe wayar dayake yayi batareda ya gamaba sbd can bangaren anajin abinda take fadan.

Kallonta cikin idanuwanta yayi yaga gajiyan dake tareda ita ya sauke numfashi kadan tareda cewa”

Idan ba call duty zakiyiba ki Dena kaiwa dare haka a asibiti
Idanma Yakama kinyi daren ki kirani Zan daukoki da kaina..na soke tuqin dare da fitan daren Nan ke daya.

Murmushi tasake tana kallonsa tace”

Ok Abbi.

Ciki suka nufa tana basa labarin aikin dasukai da daren.

Kaman yanda ta saba suna shiga ta aje wayarta da takalmanta tareda zare Jacket coat dinta ta miqawa zubbi data bude musu kofa.

Kokarin balle maballan rigarta takeyi sbd tanada singlet aciki sukai Ido biyu da Abbi Wanda ya dauke kansa Yana Dan kame fuska yayi gaba batareda yace Mata komaiba.

Tunowa tayi da fadan dayayi Mata dazu akan hakan Dan haka ta fasa cirewa ta nufi dakinta tana karban wayarta da sauran kayanta.

Wanka tayi ta saka kayan bacci masu santsi Riga da wando ta haye gado daga kwance tayi addua sbd ta gaji sosai take bacci ya dauketa.

Washe gari Bata fita aiki da wuriba sbd ciwon Kai data Dan tashi dashi na lattin bacci.
Tana fitowa a shirye palon Abbi ta nufa Kai tsaye.

Shima a shirye ta samesa zai fito sai qamshinsa Mai sanyi yake zubawa ta zubawa fuskarsa idanuwa tana tunani wahalhalun dayasha da gwagwarmaya akansa take taji idanuwanta na cikowa da hawaye zuciyarta na qara cuduwa da kaunarsa Mai girma.

Jin shiru yasanyashi dagowa daga wayarsa dayake dauka ya kalleta a natse.

Ganin yanayinta da irin kallon datake Masa yasashi Dan kame fuska Yana nufan kofa yace”

Tsayuwar me kikeyi kina lattin fita aiki.

Bayansa tabiyo tana cewa”

Good morning Abbi.

Dan juyowa yayi ya kalleta murmushin fuskarta Bai tafiba saima qaruwa da yayi
Da mamaki yace”

Are you okay?
Kinada labari Mai dadine kike Jin dadi.

Ba zato ta riqe hannunsa tana cewa”

Abbi farin ciki nakeyi ganinka kawai.

Dakatawa yayi batareda ya juyoba ganin su haj umma dasu umma yaganah dasuka fito rakiyar anty juwairiyyah da Zata wuce.

Kallonsu kowa keyi sbd umma yaganah batama San ta tashiba harta shirya ta nufi gurin Abbin,

Itakuma Haj umma mamaki takeyi meyasa haryanzu wannan ‘yar batada kunya ko tunani.

Ahankali ya zare hannunsa Yana Dan kokarin basarwa cikin nutsuwa yace”

Harkin shirya kenan anty juwairiyyah?
Muje na ajeki airport din saina wuce.

Haj umma Inayah ta kalla cikeda kulawa asake tace”

Ina kwana Haj umma?
Anty juwairiyyah Ina kwana?
Tafiya zakiyi yanzu?
Bazaki zaunaba kema kaman haj umma.

Janyota umma yaganah tayi gefenta tana matse hannunta qasa qasa tace”

Kiyi shiru idan bakisan abin fadaba Inayah.

Abbin da duk yabi ya rasa abin fada tayi ganin harda Haj umma zaa ta baro gurin umma yaganah tana cewa”

Abbi zanbiku a ajeni asibiti na kwana akan hannuna ciwo yakeyi bazan iya driving ba.

Da kulawa ya juyo Yana kallonta a natse yace”

Wat?
Shine kike tsaye anan tun dazu kina surutu?
Umma yaganah ta shafa Miki balm kafin kifita
ki zauna Charles zaizo yakaiki asibitin.

Shiru tayi tana kallonsa Jin bazaije da ita dinba.

Qin kuma kallon Inda take yayi ya nufi kofa Yana cewa su Anty juwairiyyah su fito.

Anty juwairiyyah ce ta kalleta tana cewa”

To saina Kuma dawowa Inayah,
Allah yabada zaman hakuri.

Amin” umma yaganah tace cikeda sakin fuska tana Mata Allah ya kiyaye har kofa.

Suna ficewa tadawo gurin Inayah tana cewa”

Da gaske kike ciwon hannun muje na shafa Miki ko rub kokuwa wani sabon halin kuka samu keda Neesah na hakan?

A dungure tace”

Kaina ne keyi yanzu ba hannunba
Na wuce saina dawo.

Tun su abbin Basu Gama ficewaba itama ta fito da tata motar ta fice da gudu ta wucesu
Yana kallo Bai nuna yaganiba Amma hankalinsa ya rabu da tuqin nata kusan zuciyarsa kasa samun nutsuwa tayi su umma na gani yabi hanyar databi yayi dogon zagaye dasu har Saida yaga isarta asibiti lafiya ya wuce dasu airport batareda yasan da suna lureda uban zagayen dayayi dasuba Dan ganin Yar gaban goshinsa ta Isa aiki lfy.

Suna Isa airport ba wani Bata lokaci anty juwairiyyah ta shige sbd lokacin zasu tashi.

Gida yadawo ya ajiye Haj umma ya wuce aiki.

Gidan yau yaqara yin tsit sbd anty juwairiyyah cema keda Yar hayaniyar wayoyinta da jama’ar kasuwancinta.

Da wuri tadawo yau Dan tare sukaci abincin Rana da ita
Tana Gama cin abincin Rana ta koma daki Dan tanada vid conference call dasu Neesah da wasu abokan karatunta da zasu qarawa juna sani akan aikin nasu Wanda sukeyi akai akai sbd da yawan wasu sunfi wasu qwarewa Musamman su dasuke Dan saka shiriritata itada Neesah.

A daki taqarasa wunin ranar tana conference din da abokanta saidatai sallar magriba ta fito sanyeda kayan Shan Isa gashinta a daure tsakiyar kai kaman wata Yar baby sbd fatarta daketa daukan idon hutu da gyaranta na aure da haryanzu yakeda saura.

Palo ta zauna gurin su Haj umma dake Dan fira sama sama da umma yaganah wadda wadda yanzu Ta Kama kanta a abubuwa da dama gidan sbd Haj umma dake nuna matsayinta na uwar maigidan.

Suna zaune palon Abbi yadawo yashigo idanuwansa akan Inayah datake kwance jikin umma yaganah kaman Mara lafiya.

Gaisawa yayi dasu dukan kafin ya wuce palonsa zuwa bedroom dinsa sbd a gajiye yake.

Wanka yafarayi yayi ya saka pradas na Shan iska ya zauna Yana duba sauran aikinsa acikin iPad Yana Dan amsa waya akai akai.

Lokacin magriba nayi suma duk suka tashi zuwa dakunansu sallah.

Sai qarfe 7 da mintuna suka hallara dining cin abinci.

Yauma kusan Haj umma nunawa tayi baa kulawa da majeed din yanda yakamata Dan haka da kanta taqara Masa salad akan Wanda Inayah ta zuba Masa Kuma ya nuna Jin dadin hakan a taqaice sbd haryanzu yakasa sakewa yakoma yanda yake ada gaban mahaifiyar tasa
itama Bata damuba sbd tasan sai ahankali ko wannan sabo da shaquwar tasu ta dah Zata dawo sbd shekaru kusan ashirin da hudu zuwa da biyar ba wasaba.

Fira taringa jansa cikin kulawa Yana amsawa shima cikin kulawar,

Inayah da umma yaganah Yan kallo da saurare suka koma
Karshe dai haka inayah tagama ta tashi ta komawarta daki sbd ganin yau ko kallonta Abbin nata baiyiba hankalinsa nakan Haj umma.

Umma yaganah ma tariga tashi tabar dining din ganin yau Haj umma Dagaske Jin ‘danta takeyi Dan haka kowa ya silale ya shige yabarsu.

Babu Wanda yasan lokacinda suka Gama harsuka koma Palo suka qarasa firar acan suka shige.
##MAMUH#

Leave your vote

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

GIPHY App Key not set. Please check settings

You May Also Like
Read More

TARTSATSI 46

Advertisement page 46* ******************* Hafsa hankalinta ya dawo ajikinta, koda ta waiga bataga Salma da khadija ba, nan…
KALLABI
Read More

KALLABI 39

Advertisement BABI NA TALATIN DA TARA *ABIN DA KA SAMU YAU, NA WASU NE WANDA KAYI HAKURI KA…
KALLABI
Read More

KALLABI 27

Advertisement BABI NA ASHIRIN DA BAKWAI Inna Marwa bata yarda zai iya daina zuwa fada ba, sai da…
Read More

TARTSATSI 56

Advertisement *Page 56* ********************* Da sauri ya waiga gabas yamma kudu da arewa, bai hango kowa ba saboda…